shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wanda aka fi sani da hausa novel wanda ni Muhammad abba gana nake rubutawa dan wayar tare da fadakarwa ga mutane a yanayin da muke ciki.

Thursday 2 November 2017

SIFFOFIN UWA TAGARI 2

SIFFOFIN UWA TAGARI

Kalmar macce abu ne mai matukar girma sabida daraja da kuma kima da Allah ya bata, Yaku mata kada ku shagala da jin dadin rayuwar duniya kuyi biris da baiwar da Allah ya yi muku kusani cewa duk wata jin dadin matukar baki kame kanki daga aikata fasadi ba yazama na banza kuduba kugani yanxu Rayuwar da muke ciki a bin haushi matan aure basa fita irin wadda Addini ya umurcesu dasuyi wa'iyazu billah haba mata, Ina kuka baro Hijabinku suturar ku wadda Allah ya ce ku lulluba da ita...??? Wai ace matar aure zata fita unguwa saita kashe makeup tamkar zataje gasar sarauniyar kyau amma abin haushi In ka tarar da ita A cikin gidanta tamkar yar aiki, Wai bazatayi wanka da tsaf ta ba sai in zata gidan biki ko asibiti ko wani abin to wallahi kisani duk wanda zaiga adonki ya yaba matukar ba mijinki bane kinyi a banxa. Wani abin haushi abin takaici Wai yanxu mata basu sallah cikin lokaci sabida an miki kwalliya karkije alwala ta goge Innalillahi wa'innah illaihirraju'un kenan kin xabi duniyarki a bisa lahira ko....?? wace riba gareki idan Allah ya dauki ranki kina cikin irin wannan halin...?? mezaki ce da mahaliccinki..?? kokinsan cewa mutuwa kowane lokaci zata iya yi miki bazata gaskiya mata a gyara yakamata ace duk wani abu komai mahimmancinsa ki hakura dashi har sai kin gana da mahaliccinki (SALLAH) , Adaure ayita cikin lokaci kuma bada garaje ba dan naga wasu ma sallar basusan yanda zasuyita cikin nutsuwa sabida kawai dadin duniya ya shagaltar Dasu. Allah ya sawwake. Ameen!!




Da farko yake yar’uwa ki sani aure bautan ubangiji ne. To amma mai yasa ku mata kuke banbanta yanayin zaman aurenku bayan Annabinmu dayane, domin da yawa daga cikin yan uwa mata basu dauki aure a matsayin bautaba wallahi. Bayan aure itace babban hanyar shigarki Al-jannah idan kikayi hakan kuma kika yarda da hakan to kinci riban duniya da kuma lahira. Allah yasa haka Ameen. Sannan ki sani yar’uwa duk wata ibada tana tareda jarrabawa musamman ma aure, domin zamane da ya kunshi farin ciki da bakin ciki, dadi. da mara dadi, hakuri da rashin hakuri, da sauran wasu abubuwan da basai na ambacesu ba, Yake yar’uwa ki sani aure anayinsa saboda wasu abubuwa da dama amma babban su shine natsuwa. Kuma natsuwa baya samuwa sai idan mace ta zama tagari shiyasa da yawa daga cikin maza basuda natsuwa saboda matansu ba nagari bane. Manzon Allah (S.A.W) yace duniya abin jin dadi ne, amma mafi alkhairin jin dadin duniya shine mace tagari, don haka ya yar’uwata idan harke ba mace tagari bace to ki sani baki da amfani a zaman gidan aurenki da mijinki idan kika sake baki gyara zamanki da mijinki ba, to wallahi zaki samu mummunana sakamako a wurin Allah. Allah ya karemu Ameen.


Ya kamata duk matar da ta tsinci kanta adakin aure, a wannan zamanin da muke ciki, ta gode ma Allah. Ba don komai ba, idan ta duba zata ga wasu 'yan-mata irinta, sunfi ta kyawun halitta da iya ado, amma har yanzu basu samu mijin aure ba. Don haka zai fi alkhairi agareki ki Qudurce acikin zuciyarki cewa GIDAN MIJINKI NAN NE WAJEN NEMAN ALJANNARKI Ki rike mijinki hannu bibbiyu, ki kula da tsaftar jikinki da tsaftar Muhallinku. Ki kiyaye MUGAYEN QAWAYE... Ba zasu rasa yi miki hassada ba. Tunda ke kin samu miji, su kuwa basu samu ba... Dole suyi miki hassada. Ki kiyaye sirrin mijinki, kar ki gaya ma kowa. Musamman ma kawayenki zasu so suji abinda yake faruwa. Don haka kar ki gaya musu Idan kuna da 'ya'ya to ki kula dasu, ki kula da tsaftarsu. in ma 'ya'yan kishiyarki ne, to ki kula dasu kamar yadda zaki kula da 'ya'yanki. Ki kiyaye dukkan amanonin mijinki. musamman ma iyayensa da 'yan uwansa da dukiyarsa. Allah Ya bamu ikon kiyaye Hakkin iyalan mu.
Share:

0 comments:

Post a Comment

pls drop down your comment......
dan Allah ku ajiye comment.

Tallata Kayanka

Guide Tricks Blog

Be With Me Technology

Popular Posts

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).