shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wanda aka fi sani da hausa novel wanda ni Muhammad abba gana nake rubutawa dan wayar tare da fadakarwa ga mutane a yanayin da muke ciki.

Wednesday 26 October 2016

Waye sanadi? 51&52



[10/19, 9:27 AM] 💖Äbbå-Gãñâ💖: 💘WAYE SANADI?💘 󾠲󾠮 💘💘💘 💘💘💘 💘💘💘 💘💘💘 💘💘 💘💘 💘 💘 💖MUH'D*ABBA*GANA💖 09039016969 www.MuhdAbbagana.blogspot.com To mallam yaushe zamu tafi? Rakiya insha Allah gobe zamu tafi ku hada kayanku, da sauri rakiya ta mike dan ita duk ta gaji da zaman garin tana shigowa dattijuwar da take sakar mata fuska ta shigo tana dariya tace rakiya kina murna zaki gudu ki bar mahaifarki? Ta juyo wajen babah yanzu sofi in kin tafi sai yaushe? Nan take babah ta juya baki tayi magana da fillanci rakiya sai kallonsu take cikin mamaki har suka kare maganarsu. Karshe bakwai suka rakomu tasha, shabiyu daidai muka shigo cikin garin kano mota muka dauko har kofar gida ta kawo mu koda yana zaune a kofar gida yana ganin tsayawar mota yayi sauri tashi tare da karasowa yana dariya sannunku baffa yanzu Alhaji nasir ya bar nan sai muka fara shiga gidan mallam mado habi tace rakiya kin dagawa alhaji nasir hankaki kullum ai sai yazo nan yanzu haka gobe suke shirin tafiya da kado. Sai da mukayi sallah sannan muka fito karfe takwas mukaji sallamar alhaji nasir lokacin ina sallah sai babah ce ta amsa masa yayi saurin shigowa har yana tuntube sannunku banah kun dawo lafiya? Lafiya klau alhaji ya iyali, lafiyansu klau. bayan na idar na juyo muka gaisa muna gaisawa na mike nayi daki, sai karfe goma ya mike, nabah ina son magana da rakiya har na fara barci naji babah tana tashina kizo Alhaji zai tafi na mike ya fito yana tsaye a sororo na karasa rukkaya in sati biyu sai da akayi wata daya, fuskata a hade nace haka Allah ya tsara, rukayya ya kamata ki fara zuwa awo dan haka gobe zanzo na kaiki na mika masa ledar da babah ta ban na bashi tsaraba. Ina komawa daki na dauko hoton safiyya ina kallo naji hawaye yana zubar mini kina ina nana ki dawo na ganki kin saka rayuwata cikin matsala ban san wane hali kike ba kina ina nana? Nan dake zuciyarta ta hau rawa tana son tayi kuka. Washe gari kare tara alhaji nasir yazo muka tafi asibiti nasarrawa, muka nufa bayan yayi parking ya juyo yana kallona fukarshi dauke da murmushi ya zaro kudi ya mikomin karfe sha biyu zan dawo na dauke ki. Bana bukatar ka dawo ka daukeni zan koma da kaina me ka dauken ne babu aure a tsakaninmu meye kuma kake shiga rayuwata fatana na haihu lafiya ka karbi abinka cikin mamaki yace rukayya wani abu na miki kike gayamin wannan munanan kalaman? Bakayi komai ba gaskiya nake gaya maka wani irin kallo kake so ai mana ka riga ka sakeni meye kuma kake bibiyar rayuwata kana so mutane suyi mana mummunar zargi? Na gode rukayya amma karki manta kina dauke a cikina hakkina ne na kula da lafiyarki da abinda yake cikinki, to daga yau bana bukatar haduwarmu ga mallam nan shine wakilina duk wani abu da zaka bamu to ya biyo ta hannunsa na gaji da ganin fuskarka kullum muka hadu sai na tuna yata wadda kukayi min sanadin rabamu da ita". Rukayya daman kalkon da kike min kenan, naji dadi da kika gayan abinda yaje ranki amma nayi mamaki sosai da har kika iya budan baki kika gayan haka ashe zaki iya mancewa da alkhairina a gareki, ban taba zaton haka a gareki ba laifin wani bayan shafan wani uhum daman ance dan adam tara yake bai cika goma ba rukayya wani irin wulakanci da cin mutunci ne safiyya batamin ba, amma albarkacinki bana taba nuna mata damuwata ba wai yau an wayi gari dan wani abu ya faru bisa kaddara ki.......' kan ya karasa ta tari numfashinsa. 🅰bbagana hausa novels @ faceebook. [10/20, 7:57 AM] 💖Äbbå-Gãñâ💖: 💘WAYE SANADI?💘 5⃣2⃣ 💘💘💘 💘💘💘 💘💘💘 💘💘💘 💘💘 💘💘 💘 💘 💖MUH'D*ABBA*GANA💖 09039016969 www.MuhdAbbagana.blogspot.com Tun kan ka aureni na gaya maka halin yata ka kuma yarda ka auren da yata alkhairi kuma kai kayi niyya kai mana tunda nake banta ba tambayarka wani abu ba, dan haka ka bar tunanin kayi mana wani alkairi da kai mun, in kuma safiyya kake tunani kawai alkhairi ka mance cikin sharadun aurena da kayi ta gaya maka duk abinda take so zaka yi mata ka kuka yarda in koh har yanxu wannan sharadin yana nan to duk abinda kayi mata kayine cikin sharadinku dan haka babu wani alhairi da kai mata sai sharudin da yake tsakaninku, mahaifiyarka da danka da kuma mahaifiyata kunyi min babban SANADI kuma rabani da farin cikin zuciyata ta tafi da kiyayyata a zuciyarta nasan halin nana koda zan gaya mata gaskiya ba zata taba yarda ba, duk lokacin da naga fuskarka sai na tuna nana dan haka dan Allah ka taimakamin ka daina zuwa wajena." Naji rukayya kuma na miki alkawarin har abada ba zan kara zuwa wajenki ba, ba tare da kemeni ba duk kuma nauyin da ubangiji ya dauramin zanyi kokarin saukewa mallam ne ya ban ke dan haka zan dinga komai ta hannun mallam kar kuma ki mance da abu daya har abada ba zan taba zama SANADIN batan safiyya ba Allah yasan zuciyata na rike safiyya kamar yadda nake rike yayana. Har abada ba zan taba cire cikin wadanda sukayi min SANADIN batan nana ba tana fadar haka ta bude motar ta fita. File taje ta bude bayan ta gama komai taje tabi layin wadanda za'ayi wa awo tunda ta zauna babu abinda take sai tunani, ji tayi an mata sallama tayi saurin dagowa sannu mama" wata yarinya ce ta fada wadda ba zata gaza shekarun nana ba nace yauwa sannu yata tun dazun ake kiran sunanki nayi saurin tashi wani dakin zan shiga? Ai sun gama sun zaya bakya nab nayi saurin dafe kai yata yanzu bazasu taimaka suyi minba tana murmushi tace karki damu bari na yiwa babban magana sai ta dubaki to na gode ta tafi tana waigena kamar zan gudu abin ya ban mamaki ba tafi minti biyu ba ta dawo. Mama ki shigo ta dubaki tace dani, muna shiga naga matar ta cire glass din idonta wanda da alama na kara karfin ganine ta hau girgiza kai har na karasa wajenta tana kallona ikon Allah ta furta yarinyarce ta dawo dani daga tunanin da nake momy kinga dan Allah basu kama?? Humm aysha kama sosai kamar an tsaga kara ta juyo wajena kece rukayya nasir?? Na amsa mata, meyasa tun dazun ana kiran sunanki baki amsa ba? Hajiya banji bane tana murmushi tace kina dai tunani shine yasa bakiji ba me yake damunki har akayi ta kiran sunanki bakiji ba , shawara zan baki kina da juna biyu ki rage tunani dan lafiyarki da ta yayanki yawan tunani zai iya kawo miki matsala da kuma barazana a rayuwarki kanwata komaii yayi zafi ki kai kukanki ga ubangiji wanda na tabbata zai amsa miki........... 🅰bbagana hausa novels @ facebook.
Share:

Saturday 22 October 2016

waye sanadi? 46---50



WAYE SANADI? 46 MUH'D*ABBA*GANA 09039016969 www.muhdabbagana.blogspot.com Ina gama karantawa kiransa ya shigo na daga tare da yin sallama safiyya kinga sakona? Na gani mene ne? ki gayan inda kike nazo mu gaisa wai kai dole sai ka ganni? Babu dole to tunda babu dole in dai kana da zuciya karka ka kirana ina fader haka na katse wayr muryar momy naji daga bayana “gaskiya kina burgeni safiyya tana fadar haka ta shiga toilet ta dauro alwala bayan ta idar da sallah ta juyo tana kallona safiyya meye yake damunki? Wallahi in baki daina yiwa maza rashin mutunci ba zakizo kiyi dana sani” momy bana son naga namiji yana min Magana koda na minti daya ne na gaya masa ya daina kirana yaki yarda shi yasa na sake gaya masa Magana dan yaji haushi ya daina kirana. Ke a ganinki hakan da kikayi shine mafita? Na daga mata kai to wallahi wannan ba zata zame miki mafita ba shawara ta karshe da zan baki in kin dauka kin taimaki kanki kuma wannan itace shawara ta karshe d azan baki, in har baki dauka ba har abadah bazan kara baki shawara ba kin yarda? Momy ki…….tayi saurin katse ta ban nemi wata Magana a wajenki ba kawai ki ban amsa shi kenen momy na yarda kuma insha Allah in har kika gaya min shawararki zan dauka nayi aiki da ita dan nasan bazaki gayamin abinda zai cuce ni ba ‘ safiyya ki bawa Muhammad dama yazo ya ganki, kai ta dago a razane momy bana son na yaudari mutum dan haka bana sauraran samari.” Okey ke haka zaki zauna ba zakiyi aure ba? Momy waye zai auri wadda bata da uba ni kam b azan batawa kaina lokaci ba, nazo na kamu da son mutum daga baya yazo ya guje ni. Ni dai shawara na baki in kinga dama ki dauka in kin ga dama ki barshi, wayar tace tayi kara kallon momy take wadda ta tsare da ido, dole na dago nayi sallama da sauri ya amsa safiyya Dan Allah ki gayan inda kike” zan turo maka da message ina fadar haka na katse wayar tare da juyo ina kallon momy bude bakina keda wuya kan nayi Magana tace’ to tura masa da text din’ momy ya zance? Okk baki san meh zaki gaya masa ba kika ce zaki turo masa? Na daga mata kai tace sai ki rubuta masa kalaman soyayya tare da alkawarin zaki aureshi zaro ido nayi ina dariya kai momy in na rubuta hakan ai naji kunya na zubar da ajina; au har ma aji ne dake? Kai haba momy me kika dauke nine? Kinga karki shiriritar dani ki tura masa yanzun nan. Abbagana hausa novels @ facebook. [10/12, 9:07 AM] Äbbå-Gãñâ: WAYE SANADI? 47 MUH'D*ABBA*GANA 09039016969 www.MuhdAbbagana.blogspot.com Ina tura masa ya kira na gode safiyya gobe karfe biyar zan zo toh Allah ya kaimu ina fadar haka na katse kan na mata magana wayarta ce tayi kara ta dauka tare da cewa Salamu alaikum Abba lafiya klau sun jima suna hira sannan ta miko min wayar abba an yini lafiya? Lafiya klau safiyya ya karatu? Alhamdullilah ai gobe zan zo ganinku gayan me zan tawo miki dashi? Ina dariya nace ba komaii zuwanka ya fiye mana komai Abba, ina hajiya? Mun jina muna hira sannan mukayi sallama momy shine baki gayan Abba zaizo ba? Tana hararata tace ce muku nayi albishir kika mike har dace mana in dai sai kince goro ne to abar albashiri din dan haka na bar maganar sorry momyna ina son allbishir din goro goro har sau biyu daman gaya miki zanyi Abba zaizo kuma gashi ya gaya miki da kansa ni ban so ya gaya miki ba naso ya zo yaga yadda kike wulakanta mutane. Baby yau bakya jin yunwa ne? Me kika gani? gani nayi baki fara mitar inzo muje aci abinchi ba ni kam baran kara zuwa restuarant din da muke zuws ba in dai bamu canza ba bazan kara binku muci abinci ba, saboda me? Bana son wannan kafurin yana damuna ke dai Allah ya gyara miki meh ruwanki dashi tun... kan ta karasa saadiya da farida suka shigo ruki yau azumi kuke yine? Farida ta fada tana kallona sarkin korafi da mita ce ta zauna tana aikin nata wai bazata kara zuwa inda muke cin abinci ba saboda me wajen yana zuba mata ido. Mun fito cikin makaranta muka hadu da saifullahi ya shigo, yana ganinmu ya hau murmushi rukayya fita zakuyi? Kan tayi magana farida tace saifu ba rukayya zaka tambaya ba ga mutumiyar taka zaka tambaya tana magana tana nuna ni wata uwar harara na zabga mata ta hau dariya, sadiya tace lallai farida zaki sha mita yau yace au sadiya safiyya bata son ai mata magaba? Nikam in za'a shekara ana min maganarta bazan gaji ba momy tace tana so a mata hirarka wai kunyarka take ji. Yayi saurin natsowa kusa dani har takakminshi ya gogi kafata yana murmushi yace wai haka safiyya kina san ma.... kan ya karasa na matsa kamar a mafarki na daga hannu na zabga masa mari wata irin kamewa su momy sukayi bana sonka! Bana kaunarka!! Ka fita a rayuwata ana son doke ne? Ya girgiza kai hannunsa yana dafe da inda na mareshi naci gaba da cewa ka takurawa rayuwata na gaya maka bazan taba sonka ba meye ruwanka dani wannan maganar ta zama ta karshe a tsakaninmu wannan marin ka da nayi zanyi maka wulakancin da yafi wannan ina fadar haka na juyo yayi saurin shan gabana na gode safiyya yau naga karshen kiyayya na miki alkawarin daga yau bazan kara yi miki magaba ba har abada amma a yanzu ina neman alfarmanki kiga cikin idona ki gayamin abinda kika gani muryarshi da naji tana rawa yasa nayi saurin dagowa ruwan hawaye ne kwance a cikin kuakkyawan idanun nasa ya saki murmushi ya juyo wajensu sadiya duk kansu ji suke kamar zasu nutse dan kunya. Rukayya sai anjima yana fadar haka ya tafi... na juyo wajen momy bude baki nayi zan mata magana tayi saurin katseni cikin tsawa karki kuskura ki fadamin wata kalma muje inda muka nufa in kuma zaki tsaya marin wasu mazan ne to taja wani dogon tsaki tayi gaba a wajen ma hakan ce ta kusa faruwa. Haka muka kwana babu wanda yayi wa wani magana balle kula wani karfe sha daya abban rukayya yazo, keh ki tashi abban rukayya yazo kanta bata amsa ta fita na fito yana zaune cikin motar abokinsa na karasa har kasa na zube muka gaisa safiyya ya karatu? Mun jima muna hira nace abba aunty rukayya ta daina kulani ina maganar hawaye ya fara zubomin cikin bacin rai ya dago yana kallonta daman fada kike da kawarki? A,a abba laifi tayi min to wani irin laifi ne zaki daina yi mata magana abba in na gaya maka abinda tayi zaka iya dukanta.... Abbagana hausa novels@ facebook. [10/13, 8:06 AM] Äbbå-Gãñâ: WAYE SANADI? 48 MUH'D*ABBA*GANA 09039016969 www.MuhdAbbagana.blogspot.com Bana son ki gayan safiyya kanwarkice duk abinda tayi a hankali zaki dinga nuna mata tayi ba daidai ba in kika daina mata magana me kikayi? Maza ki bata hakuri bana son na kara jin haka Ta juyo wajena kiyi hakuri tana fadar haka ta fita tana cewa bari na kira su sadiya to ki bude but ki dau sakonku da hajiya tace a kawo muku" Karfe biyar abba ya tafi muna dawowa momy ta bude ledar da hajiya ta aiko mana da shi katuwar cooler ce cike da soyayyar miya, Bayan sati daya Fitowar mu kenan da momy daga class mota tazo tayi fakin a dai kusa damu bayan motar naga an rubuta element sai daukar ido take kalko daya nayiwa motar na dauke kaina a hankali ya sauke glass din barinsa wata zazzakar murya naji ta doki kunneta mai faranta zuciya tabi ta ratsa duk sannan jikina kamar an watsa min ruwan sanyi na dago kai na kalli inda akai mana sallama idanuwa ya sauka akan kyakkyawan fuskarsa me cike da kwarjini zuciyata ta buga sa sauri, dauke kaina nayi dan zan iya mutuwa a wannan lokacin. Momy ta amsa masa sallamar sannunku dan Allah ina tambaya ne kan ta bashi amsa nace mallam bamu sani ba' da sauri ya juyo yana kallona sai yanzu ya kare mata kallo tsarki ya tabbata ga ubangiji tabbas duk inda ake neman kyau akazo wajenta an gama ganinsa tsaki nane ya dawo dashi daga tunanin dayake muna hada ido na aika masa da harara nayi gaba, cikin kunya momy tace ina sauraronka fuskarshi cike da murmushi yace ina neman wata daliba mai suna safiyya mukhtar tazo daga kano cikin mamaki momy tace kaine wa? Nine muhammad imran salis yau satina daya ina zuwanm nemanta amma Allah baisa na sameta ba, toh amma ka kira wayanta mana nan da nan fuskarci ta canza zuwa damuwa tun ranar da mukayi alkawarin zanzo kullum inna kira wayarta a kashe to kai baka san ta a fuska bane saita waya? Gaskiu ban santa ba, hasalima ban taba ganinta ba kullum nazo makaranyar nan sai an nunamin wasu masu suna safiyya amma inna je sai naga ba ita bace amma kai da baka taba ganinta ba ta yaya in an nuna maka wata ka gane ba ita bace? Safiyyar dana zo nema tana da tsiwa da fada ga kuma bata da kawaye sai mutum biyu sadiya da momy duk wadanda ake nunamin ban samesu da irin halin safiyya ba. Me yasa baza ka tsaya ka kalli yan matan da aka nuna maka ba? Na tabbata yan matan da aka nuna maka suna da kyau kar kaje ka hadu da safiyyar dakazo nema ka tarar da ita wata mummuna kamar hadari ba kalar da kake so ba ya saki murmushi ya daya kara fito da kyaunsa karki manta na gaya miki a waya muka hadu da safiyya, na kuma kamu da kaunarta tun kan na ganta bana zakuntar zuciyata, ina son safiyya a kowanne haki take bara nayi miki a takaixe ko dana tarar da safiyya a keken guragu bata ji bata gani zan iya aureta ki taimaka in kin santa kigaya min nasan safiyya Dan Allah da gaske? in baka yarda ba shikenan sai kaje gaba tana fadar haka ta fara tafiya yayi saurin fitilowa ya sha gabanta Dan Allah ki tsaya ki taimakeni, nace maka nasanta kana nema ka karya tani sai kayi gaba koh zaka samu wanda ta santa kiyi hakuri mutane da dama suna cewa sun santa suyi ta wahalar dani wasu suna karban kudina ni kam ban damu da kudin ba burina na ganta koh jiya sai dana bawa wata kudi mai yawa take cemin bara ta kirata shiru har shadaya ina zaune a waje harna hakura wata zuciyar ta kara gayamin da yardan Allah safiyya matar kace kar kayi zuciya dan haka yau yasa na dawo nemanta kiyi hakuri ki taimakeni ki nuna min saffiyar koh zuciyata zata iya samun sukuni tana murmushi tace tare muke da ita zuwanka ne ya koreta ya zaro ido kamar zasu fadi kina nufin wadda kuke tare ce safiyya??........... Abbagana hausa novels @ facebook. [10/15, 8:21 AM] Äbbå-Gãñâ: WAYE SANADI? 49 MUH'D*ABBA*GANA 09039016969 www.MuhdAbbagana.blogspot.com Kwarai kuwa ko kanwar tawa ba tayi maka bane no aunty safiyya ta min sosai fatana ta yarda dani amma baki gaya min sunanki ba, sunana rukayya amma safiyya tana kirana da momy sunan umman tane ni kuma in kiranta da baby, ina fatan zaka iya tuna wata ranan da ka kira ta wata ta daga take gaya maka bata da lafiya. Duk abinda safiyya takeso nima ina so ka karaso na kirata ku gaida. Hannunsa ya hade yana murmushi na gode anty bara na gyara parking ina sallah ta shigo tana zaune har na idar baby ki fito ku gaisa da muhammad momy wanni muhammad kuma? Wanda kuke waya kika kuma yi masa alkawarin yazo ku gaisa momy ni......karkice min komaii kije ku gaisa in kin ga dama koh in kin fita shima ki mareshi tana fadar haka ta mike ta fita, yana jingene jikin motarsa ta karaso ga tanan zuwa kayi hakuri muhammad kasan halin kanwartawa kan ya bude baki yayi magana na fito fuskata hade tunda na fito ya ziba min ido kamar zai hadeye ni har na karaso na tsaya a gefen momy, momy tace imran bari naje na dawo da sauri yace to anty a dawo lafiya, sai da ta harareni sannan ta bar wajen a zuciyata nace momy akwai shiga abinda ba ruwanta maganarci ce ya dawo dani daga tunani" yau Allah ya nunamin safiyya farin ciki ya cika zuciyata safiyya kina farin ciki da ganina? Kamar ba dani yake ba naci gaba da kalle kallena please safiyya ki min magana . Wai to dole sai nayi maka magana ne? Ido ya tsura min can kuma ya hau dariya tabbas safiyyata ce sai yanzu na yarda, harara na mayar masa wacce ce safiyyar taka? Wallahi darajar momy da karatun da kake saminne yasa na saurareka' Ina son mace mai tsiwa da fada kinyi daidai da kalar matar da nake so na kuma ji dadi da naci darajar girman alkurani da momy Allah yasa koda yaushe zan dinga cin darajarsu ya dan matse fuskarchi wanfa yakara fito da kyawunsa. Safiyya ya karatu? Meye ruwanka da karatuna ina fadar haka na juya zan tafi naji an rije gefen mayafina a fusace na juyo ina hararansa meye haka? Da zaka kamanine? Ban gama ganinki ba zaki tafi kya bari anty momy ta dawo karta ce nagudu da kanwarta nayi saurin buge hannunsa da sauri ya janye ina kallonsa nayi mamaki da ban maka abinda yafi haka ba ka kiyaye duk lokacin da kayi karanbanin rike wani abu a jikina zan maka abinda yafi haka, ina fadar haka na juya muryarshi na juyo "i love you safiyya ban ko juya ba na koma daki ina mita momy ta shigo hannunta dauke da manyan jakunkuna ta zuba a gabana tana murmushi baby ga tsarabar ki nace tsarabar me? Iman ne ya kawo miki tsarabar america gaskiya baby kun dace da imran nayi miki murna imran yana sonki tsakani da Allah, dan Allah momy me haka ce miki nayi ina sonsa? Wallahi nayi mamaki da dazun ban mareshi ba kanna karasa momy ta katseni ina tunanin safiyya kin samu tabin hankali har na tsaya tunanin kan abinda na fada meye ya hanaki marinshi to wallahi tun wuri ki nutsu ki tattara hankalinki kina wasa da damarki, momy safiyyarki kike cewa bata da hankali nagaya miki inda kina dashi har baki tsaya kin saurari imran ba sai na gayawa dady muna tare dake nayi saurin dago kai ki rufamin asiri; bazan ruka miki ba momy bana son imran kwata-kwata bana so kuma na yaudareshi dan haka bana so na shiga rayuwarsa yaga kamar na yaudareshi ki gane nufina, naji na gane nufinki nima kuma kin gane nufina zaki iya gayawa imran bakya sonsa amma bata wannan sigar ba ki gyara halinki. Shi kenan momy zanyi kokarin naga na gyara ina wayarki? Tana nan wato shine kika kasheta dan kar yazo koh Allah kuma yayi sai kun hadu ai kya tausayawa imran ko da wuyarda yasha na nemanki ki dau wayarki ki kunna ko zai kira kusha hirar soyayya....... Abbagana hausa novels @ faceebook. [10/18, 8:33 AM] Äbbå-Gãñâ: WAYE SANADI? 50 MUH'D*ABBA*GANA 09039016969 www.MuhdAbbagana.blogspot.com Kai momy gaskiya kada ki min haka zan kira abba na gaya masa kullum sai kin sani kuka kina daina kulani, oho dan kinga abba yasa na baki hakuri shine zaki kuma kafa da abba koh? Bata ko bata amsa ba sadiya ne ta shigo a,a wannan kayan fah momy tace yau babban bako mukayi waye babban bakon? Muhammad imran ta zaro ido kamar zasu fadi dan Allah ruky da gaske kike imran ne yazo? In de baki yarda ba shikenan yace a gaisheki gaskiya naso ganinsu tare da safiyya yaushe zai dawo? Ina hararanta nace bansani ba meye ruwana da dawowarsa, ke din baki da hankali safiyya baki san kanki ba kina abu kamar wacce bata taba sanin hanyan makaranta ba wallahi in naga saifullahi rasa inda zan sa kaina nake dan kunya harya gane daya ganin sai ya canza hanya. Hmm sadiya baki kaini jin kunyar saifullahi ba, jiya ina kokarin guduwa muka hadu nama rasa ya zance masa wallahi sadiya ga mamaki babu wani abu a fuskarsa muka gaisa har yake nuna min budurwansa yarinya kyakkyawa me hankali da kin ganta babu alamun fada a tattare da ita kai amma ruky naji dadi Allah yasa ya aureta a fusace nace kune wahallalu kuna son shiga abinda bai shafeku ba. **** **** **** **** Tunda mukazo gongola babah take cikin damuwa musamman in ta shiga dakin wata tsohuwa kullum sai ta tambayeta amma saitace bata babu komai yau ma fitowarta kenan daga dakin dattijuwa da babu wata magana a tsakaninmu in ba gaisuwa ba na shigo dakin da muke kwana na tarar da babah zaune babah ki gaya min me yake faruwa yau watanmu daya kullum in kuna magana sai kutayin yaren da bana ji meye yake faruwa ki gayamin gaskiya tun da mukazo kullum kina cikin bacin rai dan Allah ki gaya min gaskiya ta dago fuskarta wanda idanuwanta cike da ruwan hawaye tace babu komai rakiya kawai suna fadamin meyasa bamu zuwa musu haba babah me yasa zaki boye min gaskiya in har wannan hausin sukeji yaci ace sun fada mana tare da harshen da zan fahimta rakiya ki bar shiga abinda babu ruwanki. Muna cikin magana mallam maso ya shigo rakiya ta juyo wajensa dan Allah mallam ka gayamin me yake faruwa, rakiya me kika gani? Ya tambayan yana kallon babah , kullum in babah ta shiga dakin wannan matar sai ta fito tana kuka kuma sai filatanci sukeyi me dalilin? Babu komai rakiya kawai tattaunawa sukeyi. Abbagana hausa novels @ facebook
Share:

waye sanadi? 41---45

WAYE SANADI? 42 MUH'D*ABBA*GANA 09039016969 www.abbagana.pun.bz cikin kuka nace momy kinyi niyar cimun mutunci waye zai aure shegiya momy karkisa zuciyata ta buga please karki kara min maganar aure babu tunanin aure a raina ballantana yanzu da nasan matsayina nasan waccece ni koda ina son saifullahi ko muhammad sunfi karfina momy koda yanzi aure sai dai nasamu dan uwana shege na aura umma ta cuceni ta cuci rayuwata kullum ina jin haushin kaina me yasa ban bari abba ya cimma burinsa a kaina ba......kuka ne yaci karfina jikin momy yayi sanyi sosai ta tsunguna a gabana kiyi hakuri kibar kukan nan yau satin mu hudu tunda mukazo kullum kina cikin kuka haba baby kamar ba musulma ba tafi awa tana lallashina tare da nasiha. bayan munyi break muna rufe daki sadiya tazo ina kuma zaku kuke kokarin rufe daki zai kai baby asibiti tako kwashe da dariya wannan uwar zaki kai asibiti to wai ke din ina kika sani da zaki fita wata kawatace zata rakamu. na zaro ido momy kawa kikayi tace kwarai kuwa ko ban isa nayi kawa ba amma musulmace? meye ruwanku kiyi hakuri momy to ya sunan kawartamu muna cikin magana wata shirgegiyar bakar mata mai sa kukan dare ta nufo wajanmu kannan nata yaci karin gashi daga ita sai wani mini siket da farar riga nida sadiya muka bita da kallo har ta karaso muka gaisa na juyo wajen momy' momy wannan ce sabuwar kawar tamu? kai ta daga tana harararta. da sadiya mukaje asibitin karfe biyu mua fito tare da ita muka shiga daki na juyi ina kallonta kawata baki gayamana sunanki ba ta juyo tana murmushi oniya okinwa ke kumafa ina dariya nace nana saffiya mukhtar suna mai dadi ina son irin sunanku amma kin burgeni kina da kyau sosai kuna kama da rukayya sosai amma ke kanwartace? juyiwa nayi ina kallon momy tana waya maganar oniya ce ta dawo dani ina son muyi kawance ina son inga inda kawaye kyawawa duk cikin makarantar nan ban ga me kyanki ba zakiyi samari da dami dariya nasaka oniya kin ban dariya tace me nayi na baki dariya? maganar ni din bana kula samari kuma oniya aikin fini kyau, kina zagina ne kawai dazun da muka fita ake miki magana don ma kar muji me zakice sai ku juya baki, safiyya duk wanda kikaga yayi min magana cewa yake na shigar dashi a wajen ku musamman ma ke. mun jima muna hira sannan ta tafi gida na juyo ina kallon momy nace momy yunwa nakeji a hasalce ta dago sai na zama abinci ki cinye kwanciyar ta tayi ta shareni. har wajen karfe uku tana barci wayarta ce ta tasheta tana tashi ta juyo tana kallona na kwantar da kaina daya bari, bayan ta gama wayar ta shiga toilet tayi wanka ta dauro alwala bayan ta idar ta mike kizo muje wajen abincin ban ko kulata ba na mike muka fita. ban garen umma kuma...... sallama tayi yafi sau uku amma shiru don haka ta shigo gidan tana zaune tsakar gida fuskanta shakaf da ruwan hawaye. Rakiyya!! Rakiyya!! ta hau kiran sunanta kamar an tasheta daga barci ta juyo babah sannu da zuwa banji shigowarki ba zuciyarta cike da tausayin halin da yar tata ta shiga tace Rakiyya kuka kike? babah wani irin kuka kuma fuskarta cike da mamaki tare da tashin hankali tace ga hawaye nan a kumatuki....(nima can fuskata ne ciki da raunin tausayin rakiyya) TO BE CONTINUE SOON!!.... DON'T FORGET HAVE A LIKE ON MY FACEEBOOK PAGE: Abbagana hausa novels. [10/5, 8:34 AM] Äbbå-Gãñâ: WAYE SANADI? 43 MUH'D*ABBA*GANA 09039016969 www.abbagana.pun.bz kanta karasa umma ta kai hannunta fuskarta wanda kamar an watsa mata ruwa sunkuyar da kanta tayi hakan ya dada tawo da wasu hawaye mazu zafi kan fuskarta har sai da suka taba kasa zama tayi kusa da ita cikin taushin murya babah tace rakiya nayi nadamar korar safiyya daga gidan nan kiyi hakuri duk halin bakin cikin da kike cikii ne yaja miki na rabaki da farin cikinki rakiya ki yafe min dan Allah, baban dan Allah ki daina ban hakuri nice zan baki hakuri in na miki laifi. tana maganar tana goge idanunta wanda ke cike da hawaye rakiya ki rage tunani ki duba halin da kike ciki karki haddasawa kanki wani ciwo munyi magana da mallam ranar laraba zamuje gongola . babah kar muje zasu ce dan muna cikin matsala ne yasa mukazo, sai da mallam ya gayan haka ni kuma nayi tunanin rashin zuwana bazai kwantar da matsalar da take tsakanin ba cikin mamaki nace babah wace irin matsala? hmm rakiya in munje kya gani da idonki mallam yace in munje karmu nuna auranki ya mutu kuma kar muyi maganar batan safiyya zamu nuna tana makarantar kwana, shikenan babah babah bayan fitarki alhaji nasir yazo bai tar da keba yace zai dawo da magariba. karfe takwas alhaji nasir yazo bayan sun gaisa da babah ta mike bara na shiga wajen mallam bayan fitarta ya juyo yana kallon umma rukayya ina so na tambayeki tsakani da Allah ki ban amsa ta daga masa kai bai damu da rashin bashi amsa da tayi ba yace ki gayan tsakani da Allah ina dangin mahaifin safiyya suke a razane ta dago bata taba tunanin tambayar da zai mata kenan ba kantayi magana yaci gaba da cewa karki boyen komai safiyya bata da uba ne?? cikin kuka taxe wallahi da ubanta to yana ina? in kuma ya mutu ina danginsa? karki boye min gaskiya rukayya in safiyya bata da uba kaddara bata wuce kan kowa ba bata tsaya wata wata ba ta bashi labarin auranta da Dr. mukhtar har sakinta da yayi bayan dawowarta gida ciki ya bayyana akaje aka gaya masa sa duk abinda yace ta kara da cewa wallahi alhaji tunda nake a rayuwata ban taba sanin wani da namiji ba sai shi amma yaxe safiyya ba yarsa bace nayi tunanin zuwan wannan ranar da babah zata gayawa safiyya wannan maganar tun farko nina cuci kaina sa ban bawa safiyya tarb.....kanta karasa ya tare numfashinta karki karasa dana sanin a bata da amfani tun farko kika cuci rayuwar safiyya kina nunawa safiyya so mai tsanani wanda haka yasa kika gaza sauke nauyin da Allah ya dora miki tun tashin safiyya duk abinda tayi bakya taba tsawatar mata ko tayi ba dai dai ba ki mata fada kinga soyayyar da kike mata ta zama cuta gashi yanzu cutar ta zama babba kin kasa maganinta ido ta daga wanda ke cike da hawaye alhaji wace iein cuta nayi wa nana? kin cuceta mana tunda baki sauke nauyin da Allah ya dora miki ba baki taba tarbiyya da duk wata uwa take bawa danta ba. Abbagana hausa novels @ facebook. [10/7, 7:51 AM] Äbbå-Gãñâ: WAYE SANADI? 44 MUH'D*ABBA*GANA 09039016969 www.abbagana.pun.bz kiyi tunani safiyya macece duk daran dadewa zatayi aure kina ganin akwai namijin da zai aureta bai isa ya gaya mata magana ba, koh ya bata umarni taki bi kuma su zauna lafiy kin san haka ba zata sabu ba. kema ai babah tana sonki ta tsaya ta baki tarbiyya tun kina karamarki in kika yi ba daidai ba ta nuna miki har kika girma gashi kin haihu ke ma meyasa baki taimaki yarki ki nuna mata gatan da aka nuna miki ba. cikin kuka tace Alhaji Allah ya jarrabeni da kaunar nana wadda kukan ya jawo nayi mata Babban SANADI, tun da safiyya ta tashi ba tasan fada ba balle tsawa ko duka, ko babah bana bari tayi mata fada tun abin yana damun babah har ta gaji ta zuba mana ido akwai lokacin da babah tayi wanki nana tazo ta debi kayan ta wasa cikin rijiya shine ranar da babah tayi niyyar dukanta amma na dauke ta na kaita daki ina bata hakurin tsawar da babah tayi mata wanda hakan ba karamin bakantawa babah yayi ba ta biyo mu tana fada karshen kalmar babah dana dau abin wasa yau gashi ta zama gaskiya kull.....kuka yaci karfinta ta kasa karasawa kiyi hakuri kuka bashi da wani amfani addu'a zaki yi, Allah ya dawo da ita. ya jima yana kwantar mata da hankali har sai da yaga ta daina kuka har ya mike zai fita ta tuna bata gaya masa zancen tafiyarsu zuwa Adamawa ba, tana gaya masa ya juyo Rukayya ki bari in kin haihu sai ku tafi toh saboda me? fuskarta dauke da damuwa yace Rukayya ina tsoron ko bara ku dawo ba dan Allah in wani abin kika kulla kiyi hakuri ki kwance kin san ba a san raina na saki ki ba, ina gudun fushin mahaifiyat in Alllah yayi zaki dawo zaki dawo dakina babu wanda ya isa ya hanaki, kaddara daman lokacin rabuwarmu yayi in kika gujen baki min adalci ba, kar kisa abinda zaki haifa yayi marauci. abin har ya bata dariya wallahi alhaji babu wani abinda na kulla a raina za dai muje muyi zumunci tunda mun jima bamu je ba. shi kenan rukayya na yarda dake yanzu yaushe zaku tafi? ranar lahadi zamu tafi to kwana nawa zakuyi gaskiya ban sani ba yayi saurin dago kai in kun tafi kenan babu ranar dawowa? haba dai ba zamu wuce sati biyu ba Allah ya kaimu zan kawo tsarabar da za a kaiwa yan adamawa. Ana gobe zamu tafi misalin karfe tara Alhaji Nasir ya shigo hannunsa dauke da manyan jakunkuna guda biyu wadda umma zatayi tsara ba tare da kudi masu yawa dan kula da kanta kafin sun dawo. karfe shida yazo ya kaisu tasha sai dayaga tashin motarsu sannan ya tawo ziciyarsa cike da damusa da kuma tunani, tunda umma suka sauka a tasha take kallon yanayin garin cike da sha'awa mallam mado ne ya dauke su ya shigarda su har kauyensu, maganar mallam mado ce ta katsewa umma tunani tajuyo tana kallom wajen da yayi umurni a tsaya, hango wani dirkekiyar darbejiyan yara jingim a zaune bayanta bukkokine da yawa dukkan su suna zagate da karare. Abbagana hausa novels @ facebook. [10/7, 8:30 AM] Äbbå-Gãñâ: WAYE SANADI? 45 MUH'D*ABBA*GANA 09039016969 www.abbagana.pun.bz muka karasa cikin gidan babu kowa a ciki sai wata kyakkyawar yarinyar tmdaga tana kallonmu cikin rashin sani duk da haka tayi saurin mikewa ta dauko tabarma dake cikin wata bukka ta shimfida. babah tace ina mutanen gidan? yarinyar tace sun tafi kasuwa, su baffa kuma suna kiwo mallam ya mike tare da cewa muje ka rakani ya gayawa wani yaron daya tayasu shigar da kaya. tunda suka fita da mallam basu dawo ba muna zaune har wajen karfe biyar sannan matan gidan suka dawo suna ganinmu suka yi shiru da surutansu suka hau yi mata sannu da zuwa wasu tsofaffi biyu ne suka tsurawa babah ido tare da sake baki daya daga cikin su ta furta sufi kene ta daga kai tana murmushi kai kawai ta girgiza sufi kinsha hanya ta juyo tana kallon matar gidan maza ku dura abina sannu ta Rakiya haka kika girma ku taso mu shiga ciki. muda mado ne yaje wajensu baffa kun sha hanya rakiya ina yayan naki? ina murmushi nace guda daya ce tana makarantar kwana ta juyo wajen babah nan take suka juya harshensu zuwa fulatanci abinde ya daure min kai ganin babah tana hawaye, nikam sun saka ni a duhu tunda bana jin fulatanci shigowarsu mallam ce ta katse musu maganar da suke tare da wani mutum wanda naji mallam ya kira da jauro sunde jima suna maganganunsu wansa ban san kome suke tattaunawa ba **** ***** ****** ***** yau watanmu biyu a lagos muna tare da oniya muna duba wani littafi sadiya ta karaso tana dariya mukayi oniya tace ina ruka? (sunan da take gayawa momy kenan) suna tare da saifullahi ina jin ta fadi haka na maida kaina ga littafina safiyya yakikayi shiru?? na dago ina harararta idan bakinkine sai ki matse nayi maganar kan na rufe baki momy ta farida ne suka shigo tare da cewa yan uwa albishirinku sadiya da oniya sukace goro" momy ta dago wato ke bazaki ce goron ba ko? gaskiya momy in har sai safiyya tace goro sai dai su hakura da jin albishirin nikam dana ji da kar naji duk daya ne ina fadar haka na tashi ban karasa dakinmu ba text ya shigo waya ta sai dana shiga nayi sallah sannan na bude "đáñ gírmàñ Àlláh §à₣₣íýà kî gâýàñ wäjéñ đákìkè ñäžõ mùgâî§ā, kî táímákâmîn ñámíkî âlkãwárìñ ìñ đâì ñãzõ mùkã gâì§å §àù đãýâ bá žãmù kãrá hāđùwâ bá hâr ábãđã, kì tãìmâkî rãýúwâ ÑÂÑ ŠÁ₣ÍŸŸÂ đâñ ùwâñkì čìkìñ mùšùlüñčï. muhammad imran Abbagana hausa novels @ facebook.
Share:

TANA TARE DANI (end)

TANA TARE DA NI... TANA TARE DA NI... PAGE 99 BY MIEMIEBEE *THE END* “Little Fauzi kinsan in Mammy taganki zata zane kikoh?” “Daddy hide me” tasake matse mai k’afa, hannu yasa ya d’agota sama yana k’are wa jan bakin dake fuskarta kallo kawai seya hau dariya, hannu tasa cikin dimple nasa tana matsewa itama se ta gwada tab’a nata. “Makeup artist indeed why are you being stubborn kinason mu fara fad’a dake?” Ta girgiza mai kai “toh karki sake tab’a kayan Mammy kinji? Duk wanda yake sa Mami magana fa ojuju zasu kama shi irin na cikin story books naki.” “O’o Daddy nadena.” “Who is a good girl?” “Aysha Hanan Fauzi!!” “Great! High five!” Suka tafa hannu a sama “low five” suka yi a k’asa “then friendly punch” sukayi punching juna a hannu, kayanta ya cire mata ya nufa bayi da ita ya mata wanka da k’yar ta yarda yafito da ita dan shegen son wasa da ruwa ne da ita, kayakin Fannah ya hau tattarawa ya ninke ya miyar cikin wardrobe d’in da sauran accessories nata. “Ina Mammy?” “She is sleeping” ta basa amsa tana k’ok’arin ciro d’aya daga cikin hand bags na Fannah dake rataye a hanger. “A’a little Fauzi banda b’arna zo na saya miki chocolate” da gudu tayi wajensa bekaita ko ina ba se wajen data yi rubutu “Little Fauzi what is this?” “Wannan?” ta nuna mishi da yatsa. Kai ya gyad’a mata. “Daddy bakasan capital letter A and small letter a ba? Aahhh! Shame on you” Tasa hannu tana tare kumatunta. “I mean mesa kikayi rubutu ajikin k’ofa da nan?” “Aunty said we should practice everywhere.” “Hanan what she meant is that kuyi practicing a books ko papers ba jikin walls, floors da k’ofa ba, ba’a rubutu ajikin bango kinji? A book kad’ai akeyi.” “O’o nafison anan my book is too small.” Da k’yar yayi convincing nata ta yarda barata sake rubutu ba se cikin littafi dukda kuwa yasan baji zatayi ba. A 2 seater ya zaunar da ita ya kunna cinema yasa mata Cartoon network wai a tunaninshi cartoon ze d’auke mata hankali baratyi b’arna ba dan ze shiga bayi watsa ruwa, “Behave yourself kinji little Fauzi? Banda tab’e tab’e.” “Yes Daddy” tayi maganan tare da sake riqe teddy bear nata tana mai murmushi yana b’acewa daga kallonta ta sauk’o kan kujeran ta d’au remote tasoma bin buttons d’in one by one tanaci seda ta cinye kap sannan ta miyar ta ajiye ta nufa dining ita wai a dole yunwa takeji zata d’iba abinci. Flask d’in ta bud’e taga spaghetti seta sakar da murmushi ta fara bin kan naman ciki one by one tana chi kad’an ta rage agarin rufe flask d’in tayi b’arin abincin duka ya zube a k’asa. “Oh no! Mammy will beat me today, Aunty said learn to tell your parents sorry when you are at fault” cute smile nata ta sakar sannan ta ja teddy bear nata ta nufa d’akinsu Fannah a hankali ta bud’e k’ofar ko noticing nata su Fannah da suka zurfafa suna kissing juna basuyi ba, baki wangalau Hanan ta sake, a nitse ta dosa cikin d’akin taje ta zauna kan couch opposite them tana kallonsu, har a ynzu basu san da shigowarta ba seda Anas ya juya Fannah, Fannah taga Hanan ko kad’an shi Anas ma be ganta ba. “Habeebi wait! Ka tsaya Hanan is here” firgit ya miqe zaune yana k’ure wa Hanan data sa hands nata a both side of her cheeks tana kallonsu ko kyafta ido babu. Dukansu were at shock bawanda ya iya mata magana gawani kallonsu da take har yanzu. “Little Fauzi why didn’t you knock before you came in?” “Because the door was open, Mammy what are you doing with Daddy?” Cike da kunya Fannah tace, “nothing sweetie jeki d’auko min princess gown naki mu nuna wa Daddy.” “Saboda in na fita ku sake kama junanku ba, hmm bad girl” “Little Fauzi don’t say that kinga Mammy batada lafiya ne nake dubata.” “Are you a doctor? Toh aima you may kill her kayi nauyi ka zauna akanta.” “Ya Salam Hanan dan Allah kiyi shiru kuma karki sake magana haka, we are sorry kinji?” Cewar Fannah. “Perfect! Dama nima nazo ince miki sorry kuma kin fad’a min thank you Mammy’ tayi tsalle ta sauqa daga couch d’in. “A’a wait Hanan what did you do?” “Nothing Mammy, Daddy ka cigaba da duba Mammy bye” taja musu k’ofan. **** Chan dare around 7:30PM su Fannah suna zaune a parlour, Anas is busy with work itakuma tana taya Hanan homework sede sam Hanan tak’i concentrating. “Daddy Mammy our teacher has a veryyy biiggg nose.” “Ikon Allah Hanan me ruwanki da hancin teacher’nku kuma.” “Mammy baki gani bane? Ai seda na gwada sa 5 fingers d’ina aciki kuma duk suka shiga kuma setacmin wai you this Aysha you’re so stubborn you are lucky your dad is... Is.. Billo oho ni na manta haka de tacemin.” Dariya sosai Anas ya tsaya yi. “Habeebi Allah kadena mata dariya the more kana mata dariya the more take sake rashin ji.” “Flower I can’t help it.” “Flower??” Hanan tayi maganan tare da tab’e baki “Daddy mesa kake cewa Mammy Flower? Flowers fa acikin story books suke” shiru kawai yamata dan kuwa Hanan tafi k’arfinsa bayan sun gama mata home work d’in da k’yar, Anas yace, “Hanan baby miqo min remote” “Daddy gashi” daidai ze danna power button kenan yaga wuyam! Hannu ya aza kan bakinsa in shock. “Hanan Fauzi! What is this? Ina kika kaimin buttons d’in? “Daddy bani bane.” ”You are lying ko? Then waye ne?” “Mammy ne naganta d’azu tana ci but don’t tell her” aiki Fannah dake fitowa da towel na Hanan ta jiyota. “Hanan nice nachi remote?” “Eh kece.” “Oh Allah shiryeki Hanan.” “Ameen Mammy kema Allah shiryaki.” “Ai ka soma gani da kanka ni wuce muje mu miki wanka ki kwanta gobe akwai school.” “O’o ni barin sake zuwa ba hancin teacher’n mu is too biggg.” “Oh ni Maman Hanan da ana siyar da mutane dana siyar dake Hanan in huta.” “Kema Mammy da ana siyar da mutane dana siyar dake.” Hanan ta kwaikwayeta. Anas na tashi shiga d’aki dan d’auko wani abu Hanan ta kewaya taga ba Fannah tuni ta nufa gun dataga papers na Anas “aha! Daddy said we only write in books and on papers” biron dake kusa da wajen ta d’au tahau zana ‘Aa ’ masu desings akai, fitowan Anas yayi daidai da lokacin data ke danne danne cikin laptop nasa. “Daddy does like this and like th-” “Omg! Little Fauzi Allah yasa baki fitamin daga inda nake ba saboda banyi sav-” aiko be k’are maganan ba yaga tayi shut down na system d’in gabad’aya. “Hanan” ya juyo yana kallonta cute smile nata ta sakar masa da innocent baby face nata. “Daddy!” Kafin yamata magana ta d’au files na F&C enterprises da suka basa dan signing meze gani akai? ‘Aa’ na Hanan akai kota ina baki yasake totally speechless “Flower!” Ya danna wa Fannah kira ”yes Habeebi” tayi maganan tana fitowa daga kitchen. “Kizo ki d’auki wannan b’eran kisata baccin dole please.” “Yau kuma kanku akeji da little Fauzi da bata laifi? Hanan me kikayi wa Daddy?” “Be iya rubuta A bane na mishi kuma d’azu yace I should stop writing on doors and walls I should write on on papers and in books shine nayi.” ★★★★ _6 months later..._ Tsaye Fannah ke a kitchen tana girki da k’atoton cikinta wanda yake nan kaman na twins na 5 months, aiko Hanan ta tabbatarmin da eh cikin ‘yan biyun ne da Mammynta. 12:30PM driver yadawo da Hanan gida bayan ta yi wulli da takalamanta dakuma jakan makarantan ta a parlour ta dosa kitchen inda taji motsin Mammy. “Mammy I’m home.” Shiru Fannah tayi bata tanka taba “Mammy I said I’m home” nanma shiru. “Mammy I’m sorry.” “Ai ba ruwa na dake Hanan tunda bakiya jin magana kinga in na haifi baby twins d’ina barin sake shiga harkanki ba, saboda su basu gagara in akace musu stop zasu bari not like you.” “Mammy I’m sorry.” “Aini ba ruwa na dake kicigaba da biye wa Daddy, Airah da Aidah (baby twins nata) kawai nasani ina haifansu zamu bar miki gidan nam sekita rashin jinki me kad’an ki.” “Mammy no please karki tafi min da sisters d’ina.” “Toh mesa zan bar miki su? Dan ki koya musu rashin ji suma?” “No Mammy I’m sorry I won’t do it again” ta riqe kunnuwanta. “Are you sure?” “Yes Mammy” “Oya come here” ta wanke hannunta a sink da gudu Hanan tayo kanta Fannah ta d’agata sama “daga yau bara ki sake min b’arna ba?” “Yes Mammy.” “Thats my girl zaki tab’a sisters naki?” Cike da jin dad’i ta gyad’a kai nan Fannah ta ajiye ta sannan ta aza hannunta kan cikinta aikuwa tayi having kick. “Mami najisu Airah da Aidah koh?” Fannah ta gyad’a mata kai. “Mammy se yaushe zasu fito?” “In 3 weeks time in shaa Allah” “Yeyy! Zan zama Ya Hanan koh? Yawwa Mammy zanje wajen Ummimi yin weekends Ya Amal tace zamuyi wasa kuma zata kaini wajen Ya Aiman.” “Wallahi data kyauta min kona samu sakat bari zuwa anjima zan shirya miki akwatinki oya jeki cire uniform naki sauran kuma kice zaki wanke kinji ni ba?” Daidai nan wayan Fannah dake kan counter yasoma ruri ganin Afrah ke kira ta d’aga da wuri. “Mata a gidan Shettima.” “Hehe Mom Hanan maman ‘ya biyu ya jiki?” “Wallahi alhamdulillah ya hidima?” “Se godiya, nikam gown da zansa a bridal shower d’innan nakeso ki rakani store inje in duba anjima.” “Aww ba d’inkawa zakiba?” “Baby yaban enough kud’i siyan na kanti kawai zanyi.” “Toh fa Afran Shettima Allah nuna mana bikin nan naku, zuwa anjima in Amal tazo ta d’au Hanan se in taho muje mu duba miki.” “Yauwa ina wannan meh blue eyes nakin?” “Wai Hanan?” “Eh mana kai! Yarinya ko jaraba?! ai wallahi banson ta sake zuwa mana yin weekends waya na fa ta d’auka ta tsoma cikin miyan kukan Mami, tad’au shampoo tana wanke wa bebinta gashi, farin jallabiyan Baba ta d’auka tana gogawa a k’asa wannan Hanan seku.” “Toh naji karki zagar min ‘ya ahakan Amal keson d’aukanta yau har ina rowa, zanso kema Allah baki ‘ya kaman Hanan.” “Chab! Allah raba I’ve got to go zani booking makeup artist bye!” Ta katse wayar murmushi Fannah ke “su Afrah amarya oh! Wataran kuma na Aiman.” 4:25PM Anas yadawo from office, alokacin har Amal ta tafi da Hanan. Fannah kad’ai ke zaune a parlour tana shan tuwon madara “welcome home Habeebi yau ka k’ariso da kanka barin iya tashi ba.” Murmushi ya sakar mata sannan ya ajiye jakansa ya nufo inda take ya zauna light kiss yamata brushing. “The queen of my princesses I love you.” “I love you too king of my princesses.” “Ina little Fauzi?” “Amal tazo ta d’auketa d’azu wai zatayi weekends achan.” “Flower mesa kika barta haka last weekend ma Hanan batayi a gida ba.” “Toh wake neman ‘yar jaraban chan? Kasan yadda ta buga min ciki kuwa d’azu da safe?” “Ta tab’a mana Airah da Aidah koh?” Ta gyad’a mai kai. “Kinsan Hanan she got no worries se hak’uri we love you much.” “Wallahi nagaji Habeebi daga wannan I’m not getting pregnant again tunda nasamu two in one” “Haba the queen of princesses sauran two bayan wannan.” “In kai zaka haifesu kam ai ba matsala amman bani ba.” Pecking nata yayi a goshi “muje mu wanke miki kan.” “Banaso ai tun jiya nace kamin kak’i.” “Jiya ai nayi wa Hanan ne yi hak’uri Flower” arms nata tayi cycling a wuyansa tare da kissing nasa passionately na ‘yan mintuna “I love you Mr. Fauzi.” “I love you too Mrs. Fauzi tashi muje toh” a hankali ya miqar da ita suka wuce d’aki. ______________________________ *ALHAMDULILLAH!!!* Anan ni MIEMIEBEE na kawo k’arshen wannan littafi nawa me taken *_TANA TARE DA NI_* inda nayi kuskure ko na fad’i ba daidai ba Allah yafemin, kamar yadda kuka sani wannan labari k’irk’ira na ne (fiction) saboda haka adena kwatanta min shi da real life nayi littafin ne dan nishad’i sekuma dan fad’akarwan dake ciki. I will first of al like to thank *you* for reading my novel and supporting me through out, thank you so much as we keep loving each other haters wanda basuda zuciya bayan nace subar karantamin littafi amman sun kasa dan dad’i should keep on hating, mutum in baida maqiya to be kaiba abinda Fans ke cemin kenan kullum, alhamdulillah tunda ina dasu dan haka nake godiya wa haters d’ina keep on hating I got the f*ck finger up for yah! Godiya me tarin yawa ga *Aunty Sis* my sweet mom I love you Allah bar zumunci yacigaba da kare min ke, to *Lubiee (finest)* thank you for your support I’ll love you always like you do ME. To my co writers that have been supporting me through out thank you. Fatima malumfashi Hanefah usman Queen Meemiluv Anee Futha lurv Pherty Lilmeerahcute Munaysat Bebeelo Miss Hafsy Rash kardam Sahaf Miss xoxo Xybab Yusuf Ummi Aysha S.A Azeez Pharty B~B Nafee anker Ummee Adnan Hafsy Rano Xarah B~B Qurratul ayn da sauran wanda sunan su ya kwanta min kusani duk kuna raina. Special thanks to all of my group members *(MIEMIEBEE NOVELS GROUP)* yours support is different I Love you guys so much, Allah cigaba da had’a kawukan mu (OneLove) To my Fans club *(MIEMIEBEE FANS)* thank you for your love and care. From the buttom of my heart nas lisafo duka names na true fans na wannan littafi nawa butbthe prblem is Allah yayi wa wannan littafi masoya dayawa, na rubuta kusan 50 na goge saboda naga fans d’in basu k’arewa kuma banason in rubuta wasu in bar wasu, wai wannan ma wanda nasani kenan ina ga wad’anda bansan su bafah? Thank you so much guys for making my novel talk of the town. *MIEMEIBEE LOVES YOU SO MUCH WOLLAH* akwai lokacinda na fita naje kasuwa wasu ‘yan mata tsaye a gefe na suna hirar Tana Tare Da Ni wata ke cewa Allah had’ata da marubuciyar koda na fad’a musu nice writer’n they couldn’t believe it dan dad’i so dayawa ana bani labarin yadda Fans ke tad’in novel d’ina abinda nakeso kusani shine kamar yadda kukeso na kuke kuma *_TARE DANI_* nima haka nakeson ku nake kuma *_TARE DA KU_* I’m nothing without you guys (fans) kusani comments naku da wanda na gani da wanda ake ban labari akai ke keeping d’ina moving, forward ever backward never in shaa Allah haters will keep on hating till they die munyi gaba bame dawo damu baya. Allah had’a fuskokinmu agidan Aljannah, AMEEN. BISSALAM!❤
Share:

TANA TARE DANI 98

TANA TARE DA NI... TANA TARE DA NI... PAGE 98 BY MIEMIEBEE *A/N* *Dear Supporters (fans) barin che dear readers ba dan kuwa dayawa suna karanta wannan littafi nawa suna min hassada akai, wasu kuma suna zagina akanshi ba gaira ba dalili, anyways ina me farin cikin sanar da masu min unnecessary k’orafi akan wannan littafi nawa, wannan shine second to the last page of the story, Allah’n daya had’a mu shi ze rabamu, wataran zaku nemen danku zagen ma baraku sameni ba dama shi had’uwan social media haka yake. Dayawa daga cikin readers harma writers sun b’ullo ta duk inda suka san zasu iya dan hanani cigaba da wannan labari nawa amman dake nasan masoya na sunfi maqiya na yawa sesa ban d’aura kowacce aka ba na cigaba da abinda na fara, true fans kusani ko badan saqonnin alkahirun da kuka riqa mani ba, tsoronku wai kar nayi fushi na katse labari na inason kusani wallahi ba’ayi wacce zata hanani k’arisa abinda na fara ba. I just want you guys to know that no matter what *_INA TARE DA KU kamar yadda kuma kuke TARE DA NI_ Allah shige mana gaba.* *Babban albishir danakeson ma supporters d’ina shine page 98 of *_TANA TARE DA NI_* *is dedicated to each and everyone of you for the love, support and care I recieve anytime I turn on my data* *ina fatan yin hakan ze sanya ku nishad’i dakuma jin dad’i kamar yadda lovely comments naku ke sanya ni jin dad’i nima. MIEMIEBEE loves you so very much!!!* ___________________________________ Washegari suka shirya tsaf suka wuce office, duk meetings da Anas yake dashi dakuma appointment dayake dasu da mutane yayi cancelling ba abinda ya tsinana a office d’in ranan se soyewan da suka tayi da Flowersa dakuma wasa da Hanan, sun d’au selfies ba iyaka bayan sunchi lunch Hanan tayi poopoo aikin da Fannah ta tsana kenan wanke kashi, ko time da Aiman ke baby haka take kwana-kwana in Mami ta sata yi. “Habeebi Hanan tayi ajiya.” “Toh meh aciki? Kowa nayi.” “Nikam...” Ta turo baki wipes na hannun nata ya karb’a cike da mamaki take kallonsa “Habeebi meh zakayi?” “Zan goge mata mana.” “Ka iya ne?” “Zauna kiga.” Akan matress na ta ya kwatar da ita sannn yacire mata pampers d’in yayi disposing sanan yayi using wipes d’in ya gogeta tatas yasake sa mata new pampers kallonsa kawai Fannah ke she can’t be happier than this duk wani abinda tasani Anas nata ya iya she’ve got the best man! Se dariya Hanan ke ma Daddy’nta dayake sa mata new pampers bayan daya gama ya d’agota yana nunata da wa Fannah, “ya kika ga?” “Habeebi kasan ban tab’a ganin amazing person like you ba komai ka iya zamuyi deal kai zaka na wanke mata poopoo in tayi nikuma zannayin sauran.” “Niko duka ma kika ce zan nayi barin damu ba because I love my little Fauzi” yayi pecking Hanan a kumatu daidai nan wayar Fannah yasoma ringing tana kai dubanta taga Mami. “Omg! Habeebi yanzu me zance mata? Nasan definately tana gidanmu ne yanzu haka seda nace maka kar muzo kace se munzo.” “D’aga yanzu muji” ba gardama ta d’aga “hello Mami?” “Eh Fannah gani a gidanku fa ina kika jene?” “Erm.. Erm..” Ta hau kame kame. “Daga tafiya na kin kama yawo koh?” “Mami ba yawo bane fah” ta kare wayan da hannunta “Habeebi meh zance mata?” Amsar wayan yayi “Hello Mami ina wuni?” “Lafiya Babana kuna tare da Fannah ne?” “Eh mun fito asibiti ne d’auka wa Hanan allura.” “Ohh okay toh dama tuwo na kawo wa Fannah zan ajiye mata seka fad’a mata.” “Okay Mami mungode.” “Yawwa ashafa min kan jikata.” “Toh anagama se anjima” karap ya katse. Pecking nasa tayi a gefen idansa “Mr. Fauzi can tell lies ehm!” “LOL ai da nayi shiru ta sissileki.” “Ai cemata zanyi kai kace in biyo ka.” “Haha! Zan qaryata ki ince kekika dameni wai sekin biyoni.” “Allah ko?” ”Yes Baby d’an had’a min coffee kinji I can’t remember when last nasha coffeen Mrs. Fauzi.” “Barin had’a ba” ta murgud’a mai baki. “Flower menayi kuma yanzu?” yana tab’a hannunta taja da baya. “Bansani ba ni miqo min Hanan in bata lunch nata.” “Zo ki bata anan yi hak’uri Mom Hanan” a hankali ya jawota ta zauna agefensa sannan ta amshi Hanan tafara shayar da ita yana zaune gefensu yana kallon su cike da adoration**** ★★★★ Life couldn’t be better, Anas, Fannah da Hanan nasu rayuwa na tafiya masu daidai se girma Hanan take wane kazan agric, tana girma tana kyau tana kuma sake kama da Daddy’nta, a yanzu haka Hanan nada 5 months tafara zama, yarinya son kowa k’in wanda ya rasa sede Fannah bata shiga da ita cikin jama’a ba kowa so yake ya karb’eta. _Mother’s day 8th May 2016 4:10PM A GIDAN MR. FAUZI_ D’an rumfa ne wanda k’ark’ashinsa su Ummie, Ummimi, Mami dasu Afrah da kowa da kowa ke zaune akai. Tun jiya Anas yaketa preparation na wannan babban rana he want to make Ummimi feel special on this special day. Atare Fannah dake riqe da Hanan a hannunta suka fito da Anas tasha wani purple lace wanda yayi fitting nata sosai, purple kaya tasawa Hanan ma, kullum haka suke suna anko. Wajen da Anas ya tanadar mata ta zauna sannan Anas yayi welcoming kowa da kowa wani k’atoton cake aka shigo dashi aka ajiye a tsakyan d’an taron daidai gaban Ummimi kenan da *HAPPY MOTHER’S DAY* rubuce akai. _“Ummimi on this special day I your son Anas, Shettima my brother and Amal our sister will love to show our love for you, thank you for being there for us all the time we love you so very much thank you for being the perfect mother”_ ya miqa hannu ya d’agota daga kan kujeran da take zaune. “And all the other mothers here, Mami, Ummie and my dear wife Fannah Happy Mother’s Day” nan duk suka mimmiqe sukayi cutting cake d’in sannan Anas yayi presenting gift nasa wa Ummimi, se Ummie se Mami haka duk sauran ma sukayi lastly yakai wa Fannah wani d’an medium sized cake da *I LOVE YOU MAMMY (HANAN)* rubuce akai “thank you Habeebi.” “Always Flower this is from Hanan ita tace in baki so thank her not me” murmushi ta saki sannan tayi pecking Hanan a lips. “And this is from me as a token of appreciation da kula mana da Hanan da kikeyi” amsa tayi ta bud’e white diamond ne aciki na d’an kunne d sarqa aciki. “Habeebi this is too much.” tafad’a disbelievingly. “Its not Flower because I love you.” ”I love you too.” Nana suka ci kuma sukayi wasa da cake suka b’ab’b’ata jikinsu, sunyi having fun like never ba k’arami ba yaro duk suka zage suka ta wasa daga k’arshe Ummimi tasamu Anas tamasa godiya sosai in person. *RAYUWAN HANAN* Dan nishad’i. _2 years later..._ Hanan an zama ‘yan mata fa yanzu tana da 2 years 5 months yanzu se uban surutu da rashin kunya kullum suna cikin fad’a da Fannah, Allah Allah Fannah ke asata a school tayi tayi da Anas yasata koda a pre school ne Anas yak’i acewarsa se Hanan takai 3 years tukuna. Badan komai Fannah keson asa Hanan a school ba illa dan ta huta daga headache da Hanan kesa mata, gashi bata san me ba duk abinda Hanan ta mata bata iya dukanta saboda yadda take son ‘yarta. Yau ranar ta kasance Tuesday k’arfe shidan da Fannah ke tashi dan ma Anas breakfast Hanan ke tashi itama sekace me alarm Fannah ta rasa ya hakan ke faruwa na farko bawai a d’aki d’aya suke kwana ba amman sede bata tashi ba Hanan ma seta tashi tana fitowa daga d’akinsu ta tarar da Hanan tsaye bakin k’ofan d’akinta da babban pink teddy bear nata da tsayinsu d’aya riqe a hannunta d’ayan hannun kuwa ribbons na kanta ne wanda da alama pincikesu tayi. “Good morning Mammy.” tace cikin siririyar muryarta me uban sauri. Gabanta Fannah ta nufa ta tsuguna “Good morning baby, Hanan sweetie yanzu kitson dana miki jiya kika warware duka? Ina sauran ribbons d’in?” Baki ta turo tayi nuni da d’akinta. “Sweetie mesa kika tsefe? Bana ce miki karki tsefe ba?” “Banacho! I want a new one.” ”Allah ka rufa min asiri!” Fannah tayi maganan tana kallon sama, “koma d’akinki ki kwanta kokuma kije kisamu Daddy a d’aki” tayi maganan tana kama mata dogon sumanta gu d’aya. Kafad’a Hanan ta buga ”ni jan biki kitchen.” “Saboda ki sake fasa min plates ba? Banaso koma ki kwanta” tana kaiwa nan ta nufa kitchen Hanan na biye da ita. Kaman dagske Hanan ta ajiye teddy nata a gefe ta d’alle kan kujera tana kallon mamanta na aiki chan ta miqa mata wuqa ganin Mammyn nata ta d’au albasa. “Good girl” Fannah tayi praising nata. Sid’ak sid’ak Hanan ta wuce store room taciro bucket da moping stick ta cika da ruwa sannan tajawo shi kitchen, inda ake ajiye morning fresh ta nufa tajuye roba d’aya ciki duk anan Fannah batasan me Hanan keyi ba as she is busy cooking. Yadda Hanan taga cleaners keyi itama ta soma mopping kitchen d’in Fannah na juyawa dan d’auko abu taga Hanan na mopping kafin tace Hanan bari aikin gama ya riga ya gama Hanan ta juye ruwa kusan rabin bucket a k’asa. “Aysha Hanan Fauzi!!! Yau sena zaneki a gidan nan” da gudu ta yi d’akin su taje ta d’ale jikin Anas anan shima ya tashi. “Daddy talk to Mammy wai seta min duka.” “Duka kuma?” ya maido da kallonsa kan Fannah. “Metayi kuma Flower da zaki ce zaki daka min little Fauzi?” “Habeebi ruwa kusan rabin bucket ta zubar a kitchen.” “Toh shine abin tada jijiyan wuya?” “Dama ai nasan haka zakace Hanan ki nutsu tam! Asata a school kak’i an bar yarinya se uban gagara oh ni Fannah zaki kasheni wallahi.” “Oya Hanan say sorry to Mammy.” “But Daddy..” “Shh! And say sorry.” “I’m sorry Mammy” tayi maganan hanneyenta riqe da kunnuwanta “barin sake ba.” “Allah sa Hanan” tana kaiwa nan takoma kitchen. ****_Some minutes afterwards..._ “Habeebi baraka tafi office da Hanan ba yau?” Fannah tayi maganan tana bottling wa Hanan shirt nata. “Inada very important meetings yau bareyi inje da ita ba gobe in shaa Allah zamuje ko little Fauzi?” “Yes Daddy!” ta fad’a tana jin dad’i. “Oh ni wallahi toh kaja mata kunne karta min gagara yau kuma karta shiga harkan cleaners.” “Who is a good girl?” “Aysha Hanan Fauzi!!” Hanan tayi maganan tana jin dad’i. “Good banda disturbing Mami kinji?” “Yes Daddy” Fannah na gama sa mata kaya taje tayi hugging Anas. *** _3:15PM_ Zaune Fannah ke akan gadon d’akinta daidai tagama ciro wa Hanan kayakinta daga drawer kenan. “Hello Habeebi ina jinka kace Moosa zezo?” Tayi maganan wayanta maqale a kunneta. “Eh zezo seki basa files dana bari akan gado earlier d’azu.” “Oka-” bata samu daman k’arisa maganan ba takira sunan Hanan da k’arfi “Haanaaan! Nooo!” Ai bata k’are maganan ba Hanan ta ture duka jeren da Fannah tayi gaban dressing mirron abinda ya kama kan turarukanta man shafawa komai da komai. “Hello Flower what is it?” Anas yayi maganan cike da tashin hankali acewarsa abu ne yasamu Hanan. “Habeebi wallahi yau sena zane Hanan.” “No please don’t metayi?” “Baraki matsa a wajen ba sena iso tukuna koh?!” Fannah ta tsawata mata, jin haka Hanan tabar d’akin ma gabad’aya tasa gudu da wani baby pink overall dake jikinta ta wuce nata sannan taje ta fara sabon b’arna achan, bin pages na story books nata take tana yayyage su one by one tana littering d’akin nata dasu. “Jeren dressing mirror na fa ta ture kap a k’asa.” “Flower please karki tab’ata.” “Wallahi Habeebi kabarni da ita” da k’yar Anas yayi convincing Fannah ta hak’ura. **** Hanan de ba wanda yasan ranan shiryuwanta gagaran yau daban na gobe daban Fannah tayi magana har tagaji batasan kuma me zata sake yima Hanan ba kotace zata bugeta bata iyawa, yanzu sede in Hanan tayi b’arna kawai ta kalleta ta kad’a kai tace Allah shiryeki yarinya kuwa ta amsa da Ameen Mammy tana mata murmushi nan kawai se Fannah taji ta huce. Akwai lokacin da ta kama Hanan da wuqa da albasa a kitchen ita wai a dole zata yanka albasa. Sede in Hanan bataga bayi a bud’e ba se ta saci jiki ta shiga takuma kulle da key sannan ta bud’e tap na jacuzzi ta cikasa dam da ruwa harya fara yoyo a k’asa, ita Fannah tsoronta ranan da Hanan zata fad’a cikin ruwan. Hanan nada shekara uku aka sata makaranta dad’i kaman ya kashe Fannah finally zata huta itama first day of Hanan a school ta koyo rubuta letter A believe me gidan Mr. Fauzi gabad’aya seda aka zana da capital letter A and Small letter a. Anas na dawowa daga office kafin ya shigo gida yaga letter A na masa sallama jikin k’ofa koda ya gwada gogewa kuwa bai goguwa kasancewar da permanent marker tayi rubutun tunanin ina tasamu ya soma chan ya tuna ashe jiya a gabanta ya miyar da markern bayan daya gama rubutu dashi. Bayan k’ofa ya bud’u masa ya shigo yaga a kan marble floor na parlourn ma an rubuta Aa baki ya tab’e sannan ya shiga kiran sunan ta. “Hanan! Daddy is home” alokacin Fannah na a d’akinsu tana baci itako Hanan tana d’akin Fannah taje ta bud’e drawer tacicciro ninkakkun kayakin Fannah tana hargitsa su fuskarta kuwa janbaki ne ko ta ina har akan girarta tana jin muryan Daddy tasoma k’ok’arin cire bangles da sark’ok’in Fannah datasa a wuyanta dakuma hannu sede kafin tagama cirewa Anas yashigo ya kamata. Murmushi ta hau mishi “Daddy!” “Omg Hanan what have you done?” Yayi maganar yana bin d’akin da kallo k’aran zuban ruwan daya keji a bathroom yasa yayi sauri ya bud’e ya duba, jacuzzi ya tarar cike dam da ruwa da sauri ya rufe yafito. “Little Fauzi ban hanaki tab’a kayan Mammy ba?” “Daddy you did” ta had’e rai. “Toh mesa kike b’ata mata kaya?” In kaiki amiki allura ko?” Dagudu ta je takama k’afansa “no Daddy nadena.” *© MIEMIEBEE*
Share:

TANA TARE DANI 97

TANA TARE DA NI... PAGE 97 BY MIEMIEBEE Hawayen jin dad’i ne suka soma tsiyaya daga idanun Ummimi tana meh godiya wa Allah azuciyarta, mahak’uri mawadaci, ayau ta tabbata wannan zance hak’urin ta be tafi in vein ba tunda finally Anas nata ya dawo gareta. Har a yanzu Anas be raba jikinsa daga nata bekuma bar kukan dayake ba, hannayenta ta aza a bayansa a hankali tare da sake tightening hug d’in “Alhamdulillah, Allah na gode maka daka dawo min da Anas d’ina, kabar bani hak’uri Babna ba abinda kamin is okay kaji? Stop crying.” “Its not okay Ummimi nasani I’ve been treating you bad har kuka na saki kiyi hak’uri dan Allah if only nasan kwatan abinda kikayi going through kafin kika haifeni believe me wallahi barin tab’a k’untata miki ba” yayi breaking hug d’in tare da riqo hannayenta cikin nasa “I’m truely sorry mother” a hankali ta raba hannunta daga nasa ta sa ta share masa hawayen da yakeyi “bakayi offending d’ina ba Babana, nice ya kamata nan in baka hak’uri. *I love you so much Anas.”* *“I love you too Ummimi you are the queen of my heart”* ya sake hugging nata dad’i sosai Ummie taji kamar ta cinye su finally! Anas yayi accepting Ummiminsa. “Babana ya condition na Fannah?” Ummimi tayi maganar cike da damuwa. “Ya condition nata please Anas” Mami ta mara mata baya wani sabon kukan yasoma musu wajen seda Ummimi tajasa kan kujera ta zaunar dashi “haba na miji dakai kake wannan kukan Anas gaskia beyi ba agaban Mami fah? Me kakeso tace? Surukin nata rago ne komeh? A’a gaskia bana so” tasa hannu ta share mai hawayen. “Kukan ya isa haka” “Ummimi I can’t watch her suffering like this, kuyi wani abu please.” “Zaka iya komawa ciki?” Da sauri ya girgiza kai “barin iyaba barin iya juran kallon Fannah tana shan wahala haka ba kuma ba abinda zan iya yimata to ease the pain ba, I can’t Ummimi.” “Shhh! Ya isa in shaa Allah zata sauk’a lafiya.” ta kwanto shi jikinta tana sbubbuga bayansa. Sede hawqyen da Anas yake yanzu ba dan Fannah bane, hawayen dayake na missing d’umin jikin mahaifiyarsa ne wanda ba abinda yakaisa dad’i a fad’in duniyan nan, bare iya tuna when last yajisa comfortable daga anriqe shiba se yau. *_our mothers are priceless lets respect them ba abinda zamu iya musu wanda zekai koda k’wayan zarrah ne daga cikin abinda suka mana. D’aukan ciki, rainonsa, haifan mu, shayar damu, tarbiyyattar damu d.s they’ve made alot of sacrifices just so to make us happy, they don’t give a damn in abinda zasuyi ze cutar dasu as long as it’ll make us happy toh zasuyi, Allah yabamu ikon kwantata masu so kamar yadda suka somu, Allah musu albarka ya saqa masu da gidan aljannah AMEEN_* _2 hours later..._ Anas ne tsaye akan Fannah data kasa haihuwa tin tin d’azu yanzu da labourn yad’an sauqa ne tasamu hankalinta, zufan dake akan goshinta yasa hanky ya share yana me mata sannu. “Flower I’m here kinji you can do this” kai kawai ta kad’a mai. “Habeebi I can’t barin iya ba.” “Sure you can Sweetheart” yayi pecking goshinta. “Please karka sake tafiya kabarni Habeebi stay with me please.” ta sake matse hannunsa dake cikin nata tana hawaye. Badan yanaso ba ya gyad’a mata kai alokaci guda labour natan yasake hitting nan aka shiga new chapter again ihu da kukan da take yafi nada data wani damk’o Anas seda ta yayyak’ushe shi da zafin yazo yayi mata over batasan a lokacinda tafara ja mai Allah ya isa ba duk yana ji yasan ba’a cikin hankalinta take ba se sannu yake mata chan ma tace yafita mata daga d’aki batason sake ganinsa haka sukayi spending numerous hours cikin labour room suna abu d’aya. _3 hours later exactly 3:20PM_ Bayan azaba da wuya da kuka da zagi da yak’ushi Flower tasauk’a lafiya tasamu ‘yarta wacce take nan tubarkallah. Wani irin nunfashi ta saki, seji take kamar an sa mata sabon rai, “Flower you did it, Hanan is finally with us” yayi pecking nata a goshi “thank you so much Sweetheart Alalh miki albarka for this blessing I love you so much.” “I love you too Daddy’n Hanan, I love you so much” tayi maganan da murmushi kwance akan fuskarta. Daidai nan nurse ta miqo ma Fannah Hanan dake weighing 6 pounds, lullub’e take cikin pink shawul kamar a saceta a gudu. Yarinya k’atuwa tubarkallah, farinta da kamanninta sak na Daddy’nta yanayin gashinta kuwa koba a tambaya ba ansan na Mammynta ne, gashi har kan goshi da kuma kumatu ruwan zamzam da dabino Anas yabata how cute and adorable suna kallon Hanan insu, daga nan Anas ya amshe ta “Flower this is just my carbon copy ana cewa muna kama da Amal but not as we do da Hanan I love our baby Flower most of all I love you.” Murmushi tamasa “you’ve once promised me ni zanyi naming baby’nmu ko?” “Yes Flower and zan cika promise d’in yau gata kiyi mata hud’uba” amsar ta tayi ta mata wasu maganganu a kunne sannan a fili tace, “Allah raya mana AYSHA.” Cike da rashin fahimta Anas ke kallonta “Aysha kuma Flower? Kin fasa Hanan? Your dream name?” Kai ta kad’a mai ko kad’an “My Lion sunanta Aysha takwaran Ummimi but na mata alkunya da Hanan dashi zamuna kiranta ka gane?” “Dagaske takwaran Ummimi ce?” “Yes Sweetheart.” “Wow! this is great news Allah raya mana mahaifiya ta” duk sukace “ameen” sede wani gudu ba hanzari ba kan Fannah ya d’aure ta d’au Anas will freak out inyaji batun sunan amman kuwa se gani take kamar ma yafita jin dad’in sunan Hanan. “Habeebi kasani cikin rud’ani, nad’au barakayi accepting asalin sunan Hanan as Aysha ba.” “Mesa barinyi ba Flower bayan Ummimi mahaifiya ta ce, kamar yadda kika sha wahala kafin kika samu Hanan haka nima tasha kafin ta sameni, I never knew haka mothers namu suke shan wahala da ace inada masaniya akai wallahi da ko na second barin tab’a b’ata wa Ummimi rai ba, kamar yadda barin bari for once Hanan ta miki ba daidai ba nima barin sake yiwa Ummimi ba daidai ba I’ve asked for her forgiveness earlier we are all good.” dad’i sosai taji maras misantuwa. “Dasgaske Habeebi?” Ya gyad’a mata kai. “Today is indeed the happiest day of my life Habeebi, kai da Ummimi kun shirya ga zuwan Hanan omg! I feel like a queen” daidai nan Hanan tad’an yi miqa tare da bud’e idanunta se gasu nan blue sak erin na Daddy’nta atare sukace “she has blue eyes too.” sekuma suka murmusa. “Habeebi Hanan nada blue eyes.” “Yes Sweetheart mena had’a rai kuma Flower?” “Eh mana ni insha wahala in haifeta kuma ta d’au kominka, farinka, face naka eyes naka ni kawai gashi na ta d’auka.” “Ohh common Flower nan gaba kika sake haihuwa masu kamanninki zaki haifa in shaa Allah.” “Wa ze sake haihuwan? Ni? Chab!” “Eh mana we will have like 10 kids.” “Engine d’in yara ka miyar dani ko meh?” “LOL but jokes apart we will have like 4-5 kids ba? Please say yes Flower.” “Muddin you’ll be the strong Hyena I know we can have like ten kids in kanaso” tayi maganan tare da kashe masa ido daidai nan Ummie dasu Mami suka shigo Ummimi ce a sahun gaba ita ta fara amshe Hanan “wow tubarkallah sannu fa uwata” nan tasa mata albarka sannan ta miqa sauran suma sekuma sannu da sukayi wa Fannah wanda ya biyo baya. “Ummimi ga Aysha fa.” Cewar Anas. “Aysha kuma aina?” “A hannunki” Fannah ta amsata. “Kai tun ayau na zama kaka kun fara min tsiya wato koh?” “Am serious Ummimi Fannah named our baby after you sunanta Aysha but za’a na kiranta da Hanan.” “Ummimi kar kijisa mu biyu mukayi shawaran muka bata sunan kuma ma shi ya fara kawo shawaran.” Hawayen jin dad’i Ummimi ta soma “barin iya muku godiya ba Anas da Fannah, addu’a na d’aya ne Allah ya barku tare, ya k’ara k’arfin soyayyan dake tsakaninku yacigaba da kawo mana zuriah d’ayyyiba yakuma raya mana Aysha me suna na” duk suka amsa da ameen. In next Flower ta samu twins kuma Ummie da Mami zamu sa ko Flower? Ta gyad’a mai kai tana murmushi. “Wai Anas akwai son baby girls inkuma maza ta samu fah?” cewar Ummie su Mami se dariya suke. “Fine se asa musu sunan Baba dana Abuu.” Allah kawo masu albarka Habibti Mami tayi maganan tana shafa kan Fannah. Ameen Mami I love you” “I love you too” Anas ganin haka yayi gun Ummimi da Ummie shima tare da hugging nasu all “I love you momies. Kin d’au ke kad’ai kike da mama ne anan?” Ya juyo yana kallon Fannah kaman d’an yaro “naki d’aya ne nawa har biyu infact har uku tunda ga Hanan.” Duk suka kwashe da dariya banda Fannah dake dariya kad’an kad’an dan azabah. _some hours later... A gidan Mr. Fauzi_ “Ummimi wai ina zaku kai kayakin Flower ne?” “D’akinta chan zata koma da kwana har se ta fita daga arba’in.” “WTF!” Yayi exclaiming ba tare da yasan lokacin daya fad’a hakan wa mahaifiyar saba. “Meh kace Anas?” Ta zaro ido cike da mamaki. Kai yasoma sosawa “I mean Where’s The Fork da Amal tashigo dashi d’azu?” “Zakamin irin na Yusuf kenan kad’au bansan meaning d’in WTF d’in bane koh? What The Fuck ko ba haka ba?” Kallon Ummimi yake cike da mamaki sekuma ya tuna tayi zaman tsawon 14 years a k’asan turawa dole tasan abubuwa irin haka. “Uhmmm” yasoma shafa gemunsa “Ummimi please kubarta anan.” “Kamar ya abarta ne wai Anas?” “Muna kwana tare.” “Chankwad’i!” Tayi maganan tana tafa hannayenta “katab’a jin inda mace ta haihu takuma cigaba da kwana da mijinta? Dan ma Mami batace zata kaita chan gida suyi arba’in ba kenan kake wannan magana.” “Haba mana Ummimi please kubarta anan” da k’yar d’in k’yar Ummimi ta shawo kan Anas ya yarda Flower takoma d’akinta badan yanaso ba dan Ummimi keso. (Mother’s Love) Haka nan tun daga ranan da aka samu Hanan akayi limiting tarayyan Anas da Flowersa abin har rashin lafiya yakeson sasa shida ya saba kullum tare da Flowersa yau an rabasu na k’arfi da yaji a wuni befi su had’u na ‘yan mintuna ba, abin damunsa yake sosai ga yadda dangi daga Bama suka rik’a zuwa suna zuba k’auyenchi a gidan. Ahaka har Allah yakaisu ranan suna inda dangi da mutan arziki suka halarci bikin sunan Hanan. True fans na *_TANA TARE DA NI_* dam cikin gidan Mr. Fauzi musamman ma ‘yan *_MIEMIEBEE NOVELS GROUP_* se zuba k’auyenci suke gun security door kowa tace se k’ofa ya kira sunanta haka sukasa Amal agaba tana registering sunansu. Su Mrs Shamsur ne a b’angaren kitchen ansha bidirin suna wane na bikin aure kowa yasan Mr. Fauzi da son kashe kud’i ba sena tsaya lisafo abubuwan da akayi a bikin sunan ba ande ci uwar naira thast all (LOL) anchi, ansha anyi pictures, Fannah da Baby Hanan nata sun ci gifts ba dama. Tunda Fannah ta haihu Ummimi da Mami ke kanta, Ummie na achan gida dasu Abuu sede in ta wuni musu takoma, su Amal anzama Aunty rawan kai ya k’aru a yau Ummimi ta koma gida itama, ya rage Mami kad’ai ita kanta Fannah missing Habeebinta take ji take kamar taja 40 days d’in yayi ya k’are takoma gun Lion nata. Kamar yadda al’ada ya tanadar seda Fannah tayi 40 days cur! Sannan Mami ta barta takoma d’akin Anas a ranan itama Mamin takoma gida aka ragar da love birds zallah. _4:25PM_ Daidai dawowan Anas gida daga office kenan meetings hud’u yayi attending yau he is all tired k’ofa na bud’uwa yaga Fannah da Baby Hanan nashi tsaye behind it tasa wani red flow lenth gown me siraran hannu wanda yasha ado sosai, kamar yadda take sanye da jan kaya haka ma tasa wa Baby Hanan jan ‘yar kanti da white socks seda white head band se k’amshi ke tashi a jikinsu take wajen Anas yanemi gajiyan daya tattaro daga office ya rasa ko be tambaya ba yasan Mami ta tafi dalilin dayasa Fannah tafito kenan. “Welcome home My Lion.” Ta fad’a tana mai murmushi. K’arisawa ciki yayi ya amshe Baby Hanan tare da kissing nata passionately sun d’au tsawon loakci suna abu d’aya sannan a sannu tayi breaking kiss d’in. “I missed you” suka furta wa juna sekuma suka murmusa. “Flower you are looking extra ordinary beautiful I mean you and Baby Hanan.” “Thank you Honey, muje kachi abinci” tayi maganan tare a karb’e masa jakar laptop nasa sannan suka nufa dining tayi serving nasu, Hanan na a hannunsa har suka gama cin abincin. “Flower amman bake kikayi girkin nan ba.” “Why do you ask?” “Sabida I know girkin Ummimi ne wannan.” Habeebi ba’a iya maka wayo just like Hanan kasan d’azu dana mata wanka na shayar da ita har ta fara bacci fa ina cire maman daga bakinta ta tashi tasoma kuka koda nasa mata sucker nata tak’i sucking sabida tasan ba nono bane, you two ba’a iya muku wayo.” “Team Blue Eyes kikeji” nan yad’aga Hanan sama yana mata wasa. “A’a Habeebi a hankali please kasan she is still a baby.” “Toh Mom Hanan nida bansan zafin haihuwa ba se a fad’amin magana.” “LOL its the truth ba abinda yakai haihuwa azaba Habeebi.” “I know Babe tunda har kika jamin Allah ya isa kam ai komai ya b’aci.” “I said I take it back kaima kasan cikin hayyacina barin tab’a ja maka Allah ya isa ba Daddy’n Hanan.” “Nima wasa nake gobe tare zamuje office.” “Kai dawa?” “Me, you and our Hanan, dama jira nake Mami ta tafi mufara zuwa tare ‘cause I’m missing you guys like hell.” “In Ummimi ko Mami sukaji na bika office kaima kasan da akwai k’ara’i.” “Bawani k’ara’in nan you are my wife and this cutie over here” yayi kissing kunatun Hanan “is my daughter whats there? Final discussion gobe zamuje office tare.” “Yes Sir” ta fad’a tana mai murmushi anan sukayi d’aki. *© MIEMIEBEE*
Share:

Monday 17 October 2016

PHERTY 1___END

PHERTY 1__5 NA HALEEMATU LAWAL BALA ( Serdeeyerh😘 ) Tafiya take ah hankali kamar kwaii ya fashe mata a ciki ga ruwan saman da ake ta shek`awa kamar da bakin kwarya amman bay hanata tafiyarta cikin kwanciyar hankali ba da ka ganta kasan natsatsiya ce akwaii natsuwa a tare da ita jikinta duk ya jik`e kayan makaranta ne ajikinta ( uniform ) da gani na islamiyya ne doguwar riga ce ah jikinta ta yadi maiy ruwan kasa (brown) da farar abaya kayan duk sunbi jikinta wannan ne yasa nagano yanayin jikinta Doguwa ce maiy matsagaicin tsayi bata da jiki kuma baxa'a kirata rammamiya ba farace kuma ba fara sal ba tana da dogon hanci kamar al'k`alamin rubutuna bakinta dan matsa gaici lab`enta na kasa jajir yake gata da idanuwa masu kyau baxa kayi mata kallo daya ba kace baxa ka sake ba duk wanda ya kalleta so daya sai ya kara juyawa dan Allah yayi mata kyau wanda sai ka kureta kake gane hakan (k`ananan kyau kenan) Ta juya ta kalli titi taga babu kowa ba machine babu keke napep yau taci burin ko xata mutu sai tahau machine duk da gdnsu an hanasu hawan machine ko keke napep tunda driver ke kaisu duk inda xasu je yau kuma baixo daukarta ba gashi duk ta gama jik`ewa da ruwan sama dan danan ranka ya baci har fuskarta ta nuna idanuwanta sukayi jah ta sake juyawa gabas da yamma amman ba alamar abin hawa sai ga hawaye sharrr ta fara kuka kamar wacce akayi ma mutuwa Babu abinda take tunani sai nisan gidansu kawaii saita sulale ta xauna gefen titin ta bude jakkar islamiyyarta ta ciwo wayarta tana latsawa kawaii sai taga ba charge kafin tayi wani yunk`uri wayar ta dauke diiff charge ya kare wani irin takaici taji ya rufeta kamar ta hadiye xuciyar ta taita kuka kan titi ta saka kanta cikin cinyoyinta tanata kuka can taji hon din mota ah gabanta da sauri ta daugo kanta tana kallon wanda ke cikin motar Yana xaune a cikin mota amman da ganinsa kaga dogon mutum choculate colour gashi da sexy eyes idanuwansa ah waje suke kamar ya xaro su gashi da dogon hanci har baka gashin idanuwan sah gaxar-gaxar fuskarsah tasha gyaran fuska bakinsan dan karami sumarsah kwance luf akasan kamar wani black american fitowa yayi daga motar anan ne naga tsayinsah dogo ne sosai yana da k`ark`ar fan jiki kuma bai da k`iba kirjinsah ah bude yake kamar namijin xaki black jeans ne ah jikinsah da red shirt ya saka takalmi black cover shoe yana xuwa gab da ita ya fara murmushi wanda yasa kefen kumatun shi dukka biyu lotsawa (dimple's) ©sadteeyeesh😘 [9/25, 9:01 AM] Sadeeya Luv: [4/29, 11:09 AM] Sadeeyer: 6⃣-🔟 PHERTY👯 NA HALEEMATU LAWAL BALA (Serdeeyerh😘) Tana d`ago kaii ta kalleshi ta sake daure fuska tare da bashi baya cike da shagwaba cikin dariya yace sowrie baby kiyi mana uxiri plx mama ce fa ta aiki driver ni kuma kinsan ina office kuma nayita kiran wayarki a kashe yanxu haka daga islamiyyarku nake tunda ya fara maganar bai tsaya ya numfasa ba sai yanxu Shiru tayi tak`i kulashi bare ta bashi amsa ya dad`e tsaye kuma yasan halinta in xai shekara a gun baxata kulashi ba daman can miskila ce kamar shi barema tana fushi dashi yasan baxata taba kulashi ba hakan baisa yaji haushi ba saboda yasan halin yan kayanshi dole ya duk`usa ta gefen da ta juyar da kanta ya tallabi habbarta tare da cewa sowrie PHERTY! Kema kinsan babu yarda xa'ayi ah barki ah makaranta inma kinyi fushi dani to da gan-gan tunda kinsan bani ke xuwa daukar ki ba in kinga dama ki taso muje in bakiga dama ba kuma sai kiyita xama yana kaiwa nan ya mik`e ya nufi motarshi Tana kallonshi taga har ya shiga mota yana kokarin tafi aii da gudu ta kwashi takalmanta da jakarta ah hannu ta shige motar tanata haki tana shiga ta fara shan kamshi ta gefen ido ya kalleta yayi wani munafukin murmushi ah ransah yace a banxa bayan kin gama kwasa gudu gabana xakiyita min wasu yan harare-harare har suka isa gidan bai kulata ba itama haka ita ah dole fushi take da shi A motar ya barta yayi shigewar shi part din yayanta HAKEEM yana shiga ya same shi xaune yana kallon wani indian film your are family film ya dauko dadi yaji maganar abokin nashi da sauri ya mika mashi hannu tare da cewa ABDOOL DAN KWALISAH wanda aka kira da abdool yayi dariya mai k`ayatarwa Tare da cewa hakeem ya kuka baro pherty makaranta duk ruwa da bugeta hakeem yace wai bata dawo bane yace ta dawo yanxu na daukota lokacin dana shigo kana barci mama tacemin in dauko kasan mutuniyar batasan abin arxiki ba sai shegen miskilanci taki mgn har na tashi na shiga mota sai gata ah tsiyacee hakeem ya kwashe da dariya yace da kabarta miskilancin ya kawota gida aii inda nine wllh tafiyata xanyi yace ai da yakema cewa kayi inda kaine to bakai bane . ©Sadteeyeesh😘 [5/1, 9:31 AM] Sadeeyer: 1⃣1⃣-1⃣5⃣ PHERTY👯 NA HALEEMATU LAWAL BALA (Serdeeyerh😘) Tana ganin ya fita tayi k`wafa tare da fita tabar motar ah bude tayi cikin gida d`akinta ta nufa kaii tsaye tana shiga tayi wanka tare da saka wata doguwar riga marar nauyi dardumar sallah ta shiffid'a ta dauko xureran hijab sallah ta kabbara tayi magrib tana gamawa ta fara karatun alqur'ani tana nan xaune har aka fara kiran sallar isha'i tana gamawa tayi shafa'i da wutiri tana tashi tayi falo bataga kowa ba kuma bata nemi kowa ba ita ah dole fushi takeyi da mutanen gidan hanyar fita ta nufa Tana kaiwa kofar falon xata fita taci karo da yayanta kallo daya tayi maii ta rab`a gefen shi xata wucce ya rikota tare da cewa qanwas nima fushin akeyi dani shiru tayi ya saki hannunta tare da cewa inma kinyi fushi dani ke kika sow tunda kinsan ko da wasa ban taba kaiki makaranta ba bare daukoki bata ce mashi komaii ba har ya gama maganar shi sannan tace to bani hanya in wucce in kagama shiru ya mata kuma yaki bata hanyar sunanan tsaye sai ga abdool ko inda take bai kallah ba ya mik`ama hakeem hannu suka gaisa ya wucce cikin falon daki mama ya nufa kaii tsaye sai tym din hakeem ya bata hanya ta wucce Tana fita gidansu abdool ta nufa da sallamarta ta shiga gidan a falo ta samesu durk`usawa tayi har kasa tace dady barka da dare yace mata kin yini lafiya "yata" tace lafiya qlau ta juya tace momy ina yini momy tace takwara duk yau bamu ganki ba halan laifi mukayi murmushi tayi kasa-kasa tare da cewa momy ummie na daki ne tace eh dakin ta nufa tana shiga ta had`e raii ta had'e girar sama da ta k`asa ummie na kallonta xatayi magana ta rigata tace da kika taho kika barni ruwan bai kasheni ba kuma ban rasa wanda zai daukoni ba harara ummie ta bita da ita tare da cewa Aii naso ruwan ya kashe ki kuma ki rasa mai dauko ki tunda da akaxo daukata ban miki magana ba kikace baxaki bini ba inama amfani kedaii wllh mijinki ya shiga ukku da k`orafin ki da shegiyar mita mtsww inama amfani wannan abun irin ku ne kullum sai kunyi fada da miji kin canxa hali dan wllh yah abdool bai sown yawan nanata magana kullum complain yake dake ina ga anyi auren pherty batace komai ba har sai da ummie ta gama masifarta tukuna tace to sannu mama aii da tashi kikayi kika bugeni sai fadan naki yafi shigata koda yake ba laifin ki bane ni na sow daga ke yar yah abdool din fuska na baku shiyasa duk maganar da taxo bakinku kuke gayamin Tana kaiwa nan tayi gaba abinta koda ta fita falo bata tarar da kowa ba ah gun fita ne taci karo da yah abdool ta wani bala'in dauke kaii tare da gugar kafad`ar shi xata wucce da sauri ya fisgota ta fado kan kirjinshi yayi mata kyakyawan ruk`o itako sai mistilniya take yace haba mami (sunan da yake kiranta dashi kenan cos sunan momynshi ne da ita) meya faru ne kiketa faman fushi tace nidaii sakarni xaka wani rungumeni kamar wata "diyarka" ko matar ka yace aii kedin matata ce ko kin manta yah abdool i realy luv u so much irin maganarta yayi cike da tsokana tace yah abdool i realy hate uu da sauri ya daugota yace karya kike ta gantsara mashi cizo ah kirji tare da muguda baki tace kace ka fasa aurena dan nima ban sown miji mai yawan kawo complain dina gidansu tana kaiwa nan tayi wajen abinta ta barshi tsaye cike da mamaki. ©Sadteeyeesh😘 [9/25, 9:01 AM] Sadeeya Luv: 1⃣6⃣-2⃣0⃣ PHERTY👯 NA HALEEMATU LAWAL BALA (Serdeeyerh😘) Harta fita get din gidan bai dena kallonta ba metake nufi da complain wato ummie tayi Mata wata magana kenan tunda gashi har ta ambaci baxata auri mai yawan kawo k`arar ta ba shakka babu sunyi fada da ummie harta fada mata hakan Dakin Ummie ya nufa kanshi tsaye da shigarsa ya fara tambayarta ke mekika fadama maminah cike da nuna halin ko in kula tace metace nace mata wata tsawa ya daka mata tare da cewa keni sa'anki ne ina miki mgn kinamin fusge-fusge answer mee fuskarta a daure ta fada mashi yarda sukayi yace to wannan ya xama na karshe daga yau wani abu ya sake hadaki da ita ku sakoni cikin shirmenku inbada munafunci da hadin bala'i miye nace mata kullum ina complain da ita yaushe nayi dake ? Yaushe na xauna dake nagaya miki hakan shiru tayi tare dayin kasa da kanta amman ta k`udurama ranta sai sunyi fada da pherty sai dai in kasheta yah abdool xaiyi ya kasheta. Tana fita gidansu ta wucce mama na xaune a falo har ta kusa shiga dakin ta mama tace phertymerh xo man dawowa tayi tare da xama gefen k`afar mama tace kinci abinci kuwa tace uhm mama tace kiban amsa eh ko a'a tace eh naci ta fada tana wani cika tana batsewa ita a dole fushi take rankwasar Mata kai mama tayi tare da cewa kedai kin bani da bakin hali wllh kin wani bi kin chanxa hali tana kaiwa nan ta tashi ta barta gun aii kamar jira takeyi ta mik`e kawaii saita saka kuka tare da ihu waii ita an tsaneta dan anga abbanta bainan an matsa mata kamar ba'a kaunarta tana cikin kukan abdool ya shigo yanayi sallamah ya ganta tsugune tana kuka yace ohhh mami kin cika rigima matsawa yayi kusa da ita tare da rik`o kafad`arta jikinshi tare da cewa sowrie sweet sis meyasa kin cika rigima ne kuma waye yace miki ba'a sownki ana kaunarki ko abban yaga abinda kikeyi xai miki fada kwata-kwata kin sake hali ne ga wani fushin banxa da kika gane maras amfani ya kamata ki sawa xuciyarki salama duk kin wani harmitsa kanki kin sakama ranki damuwa da k`orafi komai Na magana ne gunki wai meke damunki ne? Serdeeyerh na muku barka da shan ruwan RAMADAN KAREEM ©Sadteeyeesh😘 [9/25, 9:01 AM] Sadeeya Luv: [11:59PM, 7/1/2016] Aunty serdie luv😘: [11:43PM, 7/1/2016] Aunty serdie luv😘: [11:28PM, 7/1/2016] Aunty serdie luv😘: 2⃣1⃣-2⃣6⃣ PHERTY👯 NA HALEEMATU LAWAL BALA (Serdeeyerh😘) Gyara kwanciyarta tayi akan k`irjin shi yace kiyi hak`uri ki dena halin nan plx tace uhum uhum yace why Tace to yo bakai bane naganka makaranta daxu da wasu yammata yace tofa dawa kuma kika ganni? tace halimcy mana yace wacce halimcy kuma tace kafi ni sani yace kamar ya? tace kamar yarda kaji tana gama fadar haka ta tashi d`akin ta ta nufa ta barshi nan xaune yana kallonta tare da murmushi a fuskarshi yace mami uwar kishi Yana gama fadar haka ya tashi part din hakeem ya nufa tare da wak`a abakinshi yana cewa (pherty pherty ina kira kiyo amsawa sanadin kaunarki ne take sani tsuma pherty) hakeem yayi dariya harda durk`u shewa kasa sbd dariya dan danan abdool yasha murr yace miye haka [11:43PM, 7/1/2016] Aunty serdie luv😘: Kakemin dariya kamar kaga wani xararre cikin dariya hakeem yace yo kaima dai dan kwalisah naga kamar ka xaren ne kawaii karamar yarinya ta birkita ka duk ka wani xama kamar xararren duk kwalisar nan babu ita tsoki abdool yayi mai tsayi mtsswww aikai naga ummie aysha ba xararra da kai tayi ba hakeem ya daure fuska Yace aiidai kasan ummienah tafi maminka hankali wata harara abdool ya xabga mashi tare da cewa a hakan hakeem yayi murmushi yace eyeee ashe har irin harararta ta koya ma abdool yace saima kaga na rikid`e na xama phertyn Hakeem yace lallaikam da bakayi dace ba cikin bacin rai abdool yace hakeem yafa isheka wllh dan raina ya sake baci har dakuwa xamu iyayi dakai Hakeem ya saki baki galala yana kallonshi yace akan phertyn yace kwaraii in kuma kanajin wasa mu xuba kawaii sai ka xauna kayita kushemin mata to wllh xamu iya raba hanya dakai akanta yana gama fadar haka ya fita fuuuu hakeem yabi bayanshi da kallo tare da cewa ba shakka SHIN WAII WACECE WANNAN PHERTYN 👯 KU BIYONI DOMIN JIN WACECE QAWAR NAN TAWA [11:58PM, 7/1/2016] Aunty serdie luv😘: ************** ASALINSU Alhaji suleiman aliyu karad`uwa da dan uwanshi alhaji mustapha aliyu karad`uwa alhaji Suleiman ne babba iyayensu daya uwarsu d`aya ubansu d`aya ma biyi da ma biyi ne su kadai iyayensu suka haifa yan asalin garin katsina ne a wani local government karad`uwa iyayensu nan da rai amman suna garinsu wato karad`uwa Alhaji suleiman ne babba wato mahaifinsu abdool dan siyasa ne dashi gwamnati ke damawa domin kuwa shine kakakin majalisar dattawa na garin katsina wato (speaker) sab`anin dan uwansa alhaji mustapha wato mahaifinsu pherty da yake cikakken dan kasuwa yana da gidajen mai sunfi a k`irga da plaxer da kuma super market. Sadteeyeesh😘 [9:58PM, 7/5/2016] Aunty serdie luv😘: [10:38PM, 7/4/2016] Aunty serdie luv😘: 2⃣7⃣-3⃣0⃣ PHERTY 👯 NA HALEEMATU LAWAL BALA (Serdeeyerh😘) Matar alhaji suleiman daya sunanta phertymerh yaransu ukku yaseer, abdool, ummie aysha. Yaseer ne babba soja ne yana aiki ah kaduna amman yafi xama england yana wani cos ne a can basu shiri da pherty kokaran duk da tana da sunan mum dinshi kuma miemie yake ce mata duk in suka hadu sai ya daketa sbd pherty surutun tsiya ne da ita ga iyayi shi kuma duk baya sown wadan nan abu buwan shiyasa baya shiri da ita duk da yafi shakuwa da ita akan ummie aysha. Abdool ko yagama digree bautar kasa yake a inda aka turashi makarantarsu pherty komai pherty keyi yana burgeshi bata tab`a b`ata mashi rai ba hasalima komi tayi ganinshi yakeyi dai-dai dan shi pherty bata laifi shi kuma mami yake ce mata Abdool na sown pherty sosai dan shi irin maxan nan ne masu sown mata ba kamar in yaga mace yar gayuce haka xalika mata na rububinshi duk inda ya shiga sai yayi budurwa sama da d`aya hakan ke sa yanmatanshi kullum cikin fada suke amma ta dalilin pherty duk ya watsar da yan matanshi sbd baya sown bacin ranta ko kadan duk ya shagwabar da ita indai yana nan bata tab`a neman abu ta rasa ko miye xai nemo mata shi kab xuri'ar su sunsan da soyayya da shakuwa mai tsanani a tsakaninsu Yana da wata budurwa mai suna halima ana cemata halimcy a uguwarsu layinsu daya sun sow juna kamar su mutu duk sown da yake mata sai dai sown da yake ma pherty ya taka nata saboda pherty ya hakura da ita ko magana baya mata itakam kullum sai ta xo gidansu hakan ne kadai ke hadashi fada da pherty Ko tafiya yayi sai tayi ciwo shima haka wannan dalilin yasa babu inda yake xuwa ya tattaro kayanshi ya dawo part din yayanta hakeem. Ummie aysha ce k`aramarsu kuma ita hakeem xai aura iyayensu na alfahari da wannan soyayyar da ta k`ulu tsakanin yaransu tana karatun ah jami'ar ummaru musa yar'adua dake cikin garin katsina tana karantar biology education ajinta biyu. [9:48PM, 7/5/2016] Aunty serdie luv😘: Shima alhaji mustapha matar shi d`aya sunanta maryam yaranshi biyu abdulhakeem da pherty hakeem ne babba sai pherty Hakeem ya gama karatun shi yana aiki EFCC abuja bai cika xama katsina ba sai in yana hutu Alhaji mustapha naji da pherty sosai bai had`ata da kowa ba haka ita ma dan ko shawara batayi da mamanta ko Ummie aysha daga abbanta sai yah abdool ita kuma mamansu tafi shiri da yaseer da ummie aysha saboda miskilancin su shiyasa idan tana ma pherty abu kamar bata sownta abbanta ke fada Hakeem kam daman dan gidan momy ne shiya ba ruwansa da abubuwan nan nasu. WANNAN KENAN BARKAN MU DA SALLAH YAN'UWA ©Sadteeyeesh😘 [9/25, 9:02 AM] Sadeeya Luv: 31-35 PHERTY👯 NA HALEEMATU LAWAL BALA (Serdeeyerh😘) Yau cikin nishad`i pherty ta tashi da sauri take shirinta na xuwa makaranta kuma tana sown ganin abdool dan ta hucce da fushin da ake dashi na kwana biyu doguwar riga ta saka (gown)pink ce da ratsin blue-green ansha powder da pink din jambaki ta shafa kwalli sai tayi wani irin kyau abinka da farar fata gyalen rigar tayi rawling dashi. (da yake qawar tawa akwai sown wannan shigar shiyasa take girmamata duk ranar da xatayi shigar cikin farin ciki take.) Fitowa tayi daga dakinta kitchen ta nufa tea ta hada tana fitowa taci karo da mama aikau tea din ya xube mata a jiki tana dagowa ta kalli mama sai hawaye sharrr hararar ta mama tayi tare da cewa kinmin b`arna kuma kina tsaye kina kallo na halan baki iya gaisuwa ba takaici ne yasa pherty kuka tare da cewa Yanxu mamah saboda Allah kinsan haw many hours na b`ata gun kwalliyar nan wllh nasan baxan sake mai kyanta ba😡 buge mata baki taji anki aiko ta fasa ihu mama tace rufemin baki tun kafin in fasa miki wannan fitsararren bakin naki marar kunyar banxa dan danan ta hadiye kukan tare da wucewa dakinta Har ta fara shawarar cire kayan ta sake sai kuma aka fasa toilet ta nufa ta sakama rigar ruwa tare da fitowa hand bag dinta ta dauka da wayarta tayo waje tako tarar da mutumin nata har ya fito yasha farar shadda da black din hula sai kamshi ke tashi aranta tace ( annabi ma yace mafi kyawun sutura fari ). Bata san lokacin da ta saki wani irin murmushi ta saki wanda yasa kyanta ya bayyana abdool ma murmushi yayi dan yasan ta sauko kuma yasan tana bala'in sown shigar da yayi bai lura da rigarta a jik`e take ba sai da taxo gab dashi yace Mami meya jik`e miki kaya tace fitsari nayi murmushi yayi har hakoran shi suka fito tare da kad`a kaii yace to muje kinsan lecture safe xan muku 9to10 kuma mun makara k`in bude motar tayi ta shiga har sai da yafito ya bude mata tare da cewa HUKUMA murmushi tayi tare da cewa kaine ka sabamin shiyasa bana sown xuwa uguwa in baka kusa saboda bude mota kada kai yayi saida ya shiga sannan yace In ban kusa ba tace sai na fasa xuwa uguwar sai ka dawo. Yace in na mutu fa dandanan ta hade rai ta bata fuska har suka isa makaranta bata kalleshi ba koda yayi parking inda ya saba sai ga Halimcy tsaye agun da alama xuwanta kenan ta hango su ta fito daga motar ta. Kwata-kwata pherty bata ganta ba shikam ya hango ta da sauri ya kalli pherty yaga batama kula da ita wata siririyar ajiyar xuciya yayi. Pherty tana fitowa sukayi ido hud`u da halimcy ta dauke kanta xata wucce gefen halimcy ta rik`e mata gefen riga tana juyowa ta wanka mata mari ji kake tassss. ©Sadteeyeesh😘 [9/25, 9:02 AM] Sadeeya Luv: 36-40 PHERTY👯 NA HALEEMATU LAWAL BALA (Serdeeyerh😘) Wani kallon raini tayi mata tare da fusge rigarta tayi gaba abinya nan ta barshi tsaye da ita wani kallo yayima halimcy kallonshi tayi kamar xatayi mgn kuma sai ta fasa ta shiga motarta tafi bin motar da harara yayi tare dayin tsoki mtsww. Ko da pherty ta shiga hall ta iske ya cika mak`il da mutane tana shiga suka xubo mata ido kowa ya natsu dan sunsan mr.abdool bai da M kuma sunsan tare suke shigowa da pherty wannan dalilin ne yasa kowa yayi shiru sai kuma sukaga bai shigo ba harta xauna sannan ya shigo hall din. Yana gama musu lecture din ya shiga hangen inda xai ganta can tsakiya ya hangota da wayarta a hannunta da alama game takeyi baisan lokacin da ya saki murmushi ba wanda sai da duk yammatan dake hall din suka k`yasa dan wani irin kyanshi ya bayyana hade da kwarjini ya daga murya tare da cewa Mami kin d`agowa tayi duk da tasan da ita yake ya sake cewa mami tukun ta d`ago idanuwanta cikin yanga da bacin raii dtashi anunta har sunyi jaa sbd tsabar kishi. ( in banda abin qawata miye na bacin rai tunda har ta kaii mari). Yace xo yana gama fadar haka ya fita kab idanuwa suka dawo kanta ana jiran aga tashinta (kunsan dan makaranta) ganin duk ido na kanta yasa ta tashi bata tafi gun nashi ba tayi tafiyarta gida abinda duk da yace xai yi musu test hakan bai hanata tafiya gida ba. Shiru-shiru bata xo ba ya aiko wani dan ajinsu ya kirata yace mashi ta fito tun d`axu yace yah Allah! Mami kin cika matsala guy din da ya aika na tsaye yace rabu da ita kawaii malam cikin xafin rai da tsawa abdool yace get out!!! Cikin sauri ko ya fita. Tana fita daga makarantar ba ta wahala ba gun neman abin hawa ba sai gida koda ta shiga uguwarsu napep na ajiyeta ta hango motar halimcy a kofar gidansu halimcyn nan tasa mai napep ya ajiyeta dan gidansu abdool xata shiga saboda tasa in tashiga gidansu mama korota xatayi. Har takai kofar shiga gidansu abdool taji an fisgota harta kusa faduwa juyowar da xatayi sai taga halimcy tsaye tana ta huci wani tsoro ya dirar mata amman duk da haka sai da tayi ta maxa ta sake wanka mata mari har biyu tana sauke hannunta motar abdool nayi parking a gun cikin bacin raii ya fito daga motar tare da cewa da kyau pherty ta shige cikin gida abinta. Cikin bacin rai halimcy ta dubi abdool tana kana gani Karo na biyu wannan marar kunyar yarinyar ta mare ni ina raga matane saboda kaii d`axu bakayi magana ba yanxu kuma kace da kyau saboda ni ba yar uwarka bace ba ko wani irin kallon raini yayi mata tare da cewa Ta fiki hankali me shiyasa ta hukunta ki ta hanyar marin tunda ke baki da xuciya kinkai kasuwa kare ya lashe akan namiji kiyita fada kan layi saboda rashin kamun kai kamar dabba yarinyar nan ko damuwa dake bata yi ba magana bata taba hadaki da ita ba sai yanxu xakiyita nemanta da fada kema kinsan kab xuri'ar karad`uwa bata dauki raini ga kowa ba bare ke kayan banxa nace ban sown ki dole ne ?. Wani murmushi tayi mai kama da dariya tare da cewa haka kuma gidan mu bamu tab`a neman abu muka rasa ba dan haka yarda kace kana sow nah da farko ka koyamin sownka dole ka aureni baka da mata wacce ta wucce ni kaii wallahi in kaga ban aureka ba mutuwa nayi kona mutu kaida aure sai a lahira. Kallon banxa ya bita dashi tare da jan dogon tsoki mtsww gida ya shige ya barta gun tsaye. ©Sadteeyeesh😘 [9/25, 9:03 AM] Sadeeya Luv: 46-50 PHERTY👯 NA HALEEMATU LAWAL BALA (Serdeeyerh😘) Pherty na daga kwance kunya kamar ta kasheta dan bata tab`a jin kunya irin ta yau ba k`asa tayi da kanta. Momy tace d`ago kanki takwara aii tsakani na dake ba sarakunta xo ki rakani uguwar cikin sark`ewar murya tace momy yah yaseer nan fa kuma duka na xayyi murmushi momy tayi tace yo aikunyi abin dukan but muna tare baxai miki komai ba ko mutuwa na kunyar idon mahaifi bare shi taso muje sumi-sumi ta fito tana lab`e bayan momy har suka kai harabar gidan. Hankalinta bai tashi ba sai da taga momy ta bud`e bayan motar yaseer ta shiga tare da cewa shiga gaba dan-danan idanuwanta suka kawo ruwa bakin ta na rawa xatayi magana taji maganar abdool yana cewa momy nima ina xuwa. Tace ina xan tafi dakai k`ato dakai in kaika ina ? Yace momy gashinan xaki tafi da sweet berrynah. Tace ohh ni yau na shigesu abdool kwata-kwata inda kunya ta biyo baka bi ba yanxu ina surukar ka amman kaita xuba min ruwan rashin kunya tun ba'ayi auren ba kenan inaga anyi to baxan je da kai ba kuma yaseer xai kaimu. Abdool yace momy to gaskiya kije ke d`aya indai baxaki je dani ba to precious ma baxata ba. Momy mamaki ya hanata magana nadan lokaci. Tace aiko baka isa ba ashe iya shegen naka har yakai bansaniba juyawa tayi tana kallon pherty tare da cewa shigo muje pherty tayi k`asa dakai can kuma ta d`ago tare da cewa Reality in bita yace no precious ta d`ago tace momy yah abdool yace kar na biki but sowrie mum karkice sai naje dole wllh baxan iya tafiya ba tare da yarda reality ba. Takaici ne da mamaki ya kusa kashe Momy dan mutuwar xaune tayi kallonsu kawaii takeyi ta rasa abin cewa har suka juya suka nufi motar abdool yana rike da gefen kafad`arta suna isa ya bude Mata tashi ga kafin ya xagaya ya bude momy tace Abdool Ku fara shirin aure nan da wata d`aya dan wannan iskancin da rashin kunyar ba'a gidan nan ba murmushi abdool yayi tare da takowa har inda momy take. Yace momy dan Allah ya koma 3weeks kinga dai-dai dana gama service har nama fara aiki kinga salary na nafarko na precious ne tunda dai ku xakuyi mana auren nan Tace nagama magana 4weeks ko ka shirya ko baka shirya ba murmushi yayi yace thanks sweet mother in-law. Abun ya dena ba momy mamaki yanxu tsoro yake bata yarda tasan abdool da kunya amman yanxu ya xabure anya wannan soyayyar ta lafiya ce. Ita keta maganarta cikin xuciyar ta. Dady na dawowa ko momy tayi mai akan su abdool yace toke uwar amarya in kin shirya kika sani ko iyayen yaron sun shirya tace sun shirya yace bari dai in kira mustaphan. Koda ya kirashi yaxo yayi mai bayani yace ba komai Allah ya kaimu lokacin shirye muke ko yau ma akace xa'ayi mun shirya. ©Sadteeyeesh😘 Www.muhdabbagana.blogspot.com [9/25, 9:04 AM] Sadeeya Luv: 51-55 PHERTY👯 NA HALEEMATU LAWAL BALA (Serdeeyerh😘) Ana ta hidima aka saka ranar auren wata d`aya duk abin nan da akeyi yaseer bai saniba ba uwayen gayyar ko wata irin soyayya mai xafi ta sake shiga tsakanin su wanda barci ne kawaii ke raba su. Kwacham suna xaune part din abdool ita dashi tana tayashi marking pepar's na exams xaune take gefen shi na dama har kafad`arsu na gungan ta juna ta wani langwab`e kanta tare da kwantar da kanta ah kafad`arshi Tace reality am so tired k`arasa kwanto da ita yayi jikinsa tare da cewa mee too precious tace to mu huta mana baby yace owk had`amin pepar's din ki sakasu cikin dress merow tace kaii yah abdool yanxu pepar's din xa a saka cikin dress merow murmushi yayi tare da cewa kedai saka kixo tace to na sakawa ta dawo. Falo suka fita akan 3seater falon suka xauna yana xama ta xame tare da daura kanta a cinyar shi tana game da wayarta can ta juya ta murxa kanta ah gwaiwarshi yace ahhhhh!!! mami xaki karya ni plx d`agani uhum uhum. D`an kwalin kanta ya xame tare da cewa sweetheart 2dys ba muje saloon ba yau xamuje ko da yamma cikin shagwab`a tace nidai uhum uhum wllh ciwon kai suke sakani nidai plx kar muje murmushi yayi tare da cewa kema kinsan tunda nace sai muje to xa muje kawai kija please ki xunguri sowrie. Bata rai tayi tare da tashi a k`afar shi da sauri ya rungumota tare da cewa sowrie berry tace nidaii...... Kafin ta karasa sukaji karar bude k`ofar gaba d`aya suka d`ago kainsu yaseer ne tsaye yana kallonsu tare da cewa lallai yaran nan kun xama yan iska yau xanyi maganin ku, Abdool yace da mu kayi ma me?kuma iskanci me mukayi ma ? Dakina ka shigo kuma ka tarar dani da matata ka shigo ba nocking ba sallama bare mu kimatsa ma shigowar ka but kome ka gani kai ka sow . Jikin nan na yaseer har tsuma yake fuskar nan tayi jajir abinka da farin mutum fari ne dogo k`ak`arfa yana da k`irar xaki faffadan k`irji ne da shi fuskar nan tashi kamar bai tab`a had`a iri da hausawa ba wani irin kyau gareshi amman fuskar shi irin ta abdool dan dai abdool bak`i ne a kanshi inba dan kamanninsu ba mutum baxai taba yarda ta jinsi daya bane dan sumar yaseer irin ta indiyawa ce Kama yake da indiyawa dandai jini ba d`aya ba . Cikin b`acin rai ya juya fuuuuu falon Momy ya nufa bai sameta ba cikin xafin raii yayi part din dady can ya samesu xaune ciki-ciki ya gaishe su dady yace yaseer lafiya cikin masifa yace Yanxu saboda Allah dady kuna xaune cikin gidan nan yaran nan suke irin wannan rayuwar ya kamata ku rink`a lura da al'amuran su yanxu fa daki na tarar dasu rugume da juna nan dai yaba dady labarin komaii. Ajiyar xuciya dady yayi tare da cewa kiramin abdoul din har yaseer ya tashi momy tace bari na kirashi a waya cikin 5mnt ya iso falon dady yace Mashi yaushe kake gama service yace dady nagama but gobe xan mayar da wasu pepar's office din dana xauna insha Allah. Dady yace toka shirya xabi xaka tafi dubai daga can ka hado lefen aurenka kuma 3weeks xakayi cikin firgici yace dady 3weeks fa kace kuma in nayi 3weeks kaga saura 1week aurena kuma ina sown yin wasu shirye-shirye. Dad yace wannan ya rage naka na gama magana kaje ka fara shiri cikin d'acin rai ya fita yana fita yaseer yace dady naji yana maganar aure dady yace yearh bakasan an tsayar da ranar auren su ba nan da wata d`aya wani iron fad`uwar gaba yaji tare da b`acin rai lokaci d`aya suka bayyana ah fuskarshi fuskar nan ta sake rinewa tayi jaa haka idanuwanshi (TO MASU KARATU KU TAYANI BINCIKE WANNAN CHANJIN NA FUSKAR YASEER MIYE MA'ANAR SHI KO INCE MEYAKE NUFI??? INA SAURAREN KU 👂🏻) ©Sadteeyeesh😘 [9/25, 9:04 AM] Sadeeya Luv: 56-60 PHERTY👯 NA HALEEMATU LAWAL BALA (Serdeeyerh😘) Ko da ya fito part dinshi ya nufa amman bai samu pherty ciki ba gidansu phertyn ya nufa yana shiga ya marar da mama xaune a falo tana kallon labarai tana d`ago kanta ta kalli fuskar shi nan take ta gane yana cikin bacin raii, Tace abdool lafiya bayyi magana ba sai da ya xauna k`asa gefen k`afarta yace barka da hantsi mama tace barkanmu juna lafiya naga ranka a bace ko fada kukayi da mamin taka yace a'ah mama wallahi yah yaseer ne yaje ya had`ani fada da dady, Tace kamar yah nan ya xauna ya fada mata kome ke faruwa tace to in banda abinka abdool miye ai ba matsala bai fadama abinda xakaje yi ba yace no bai fadamin komai ba tace aii takardar samun aikin kace ta fito dan takai wajen wata d`aya da fitowa. Cikin murna yace kai haba mama shine ba'a fad`a min ba bayan ansan nayi alk`awalin salary na nafarko na maminah ne momy tace aikau inajin ma har an baka salary din yana gun abbanku. Cikin xak`uwa mama abban yana ina tace yana d`akin shi da sauri yayi d`akin abban cikin murna yace abba sannu da hutawa yace yawwa abdallah ya kaxo k`arbar kud`in ka ne yace abba kud`i na ko na maminah wani kallo abba yayi mashi na marar hankali tare da girgixa kaii. Yace abdool har yanxu da sauranka ya xa'ayi kawaii albashinka na farko wanda ko aikin baka fara ba an baka gashi ba'a k`asar nan ba kuma ga hidima gaban ka xakace waii ka dauka kudi kaba buduwar ka. Cikin sauri yace abbah matata daii kuma k`anwa ta kuma wannan aii al'k`awali ne tsakani na da ita albashina nafarko nata ne kuma ko bayan raina abata amman yanxu da raina kuma da lafiya ta xan cika al'k`awalin nan yanxu dan haka abba kuyi hak`uri. Kuma abbah hidimar biki su dady ne xasuyita abani mata ayiman aure murmushi abbah yayi tare da cewa yaro man kaxa abdool yanxu ko kunyata ba kaji mik`ewa yayi tare da shafa kanshi. Yace sowrie abbah na kasa jurewa ne but ina bala'een sown pherty fiye da yarda baku tsammani abba bansan yarda xanyi ba in nayi tafiyar nan wallahi abba inaji ne kamar xan rabu da wani b`angare na jikina plx Abba kace ma dady in fasa tafiyar nan har sai bayan auren mu da maminah. Cikin mamaki abba yace au tafiya xakayi ne yace eh abba xama yayi tare da yima abba bayanin komaii abbah yace too in banda abunka aii sauk`i ne da ragema aiyuka saboda haka kaje kawaii Allah ha kiyaye hanya abdool yace amin abba nagode. Yana fita d`akin pherty ya nufa kwance ya sameta da wayar shi a hannunta tana game kujerar da ke kallonta ya xauna tare da cewa precious ki tashi muje saloon din mu dawo cos da mun dawo xaki had`a min kayana dubai xan tafi. Wata irin xabura tayi tace ina xakaje yace dubaii tace dubaii?? Wa xaka dauko can yace uhum kedai bari nan ya fada mata kome ke faruwa aikau sai tahau kuka ita wallahi bata yarda yace toni ya xanyi mami dady ne ya tsara tafiyar nan kuma duk yah yaseer ne ya had`ani dashii..... Yawwa ke daman ina sown tambayarki. Cikin kuka tace ni ba wani tsaranin da xakayi wallahi.. ringing din wayarshi ne ya katse mata maganar da takeyi fuskar wayar ta kalla sunan da ta gani rubuce ah wayar ne ya d`aga mata hankali tare da yima abdool wani mugun kallo. Tace SWEET HALIMCY???? Cikin yanayin tambaya nan take hawayenta suka k`afe cike da masifa tace wato ni ka d`auka sakarya kenan ko ince mahaukaciya nice keta hauka har ina tutiya da na kora kowa ba shakka daman ai mai hali bai fasa halinshi..... Kafin ta sake magana taji bakinshi cikin nata yana kissing d`inta Cikin k`warewa da iya mugunta ta gartsa mashi wani mugun ciwo tare da hankad`a shi daga jikinta cikin masifa tace abinda ka iya kenan baka da wani burin da ya wucce ka jika kusa da mace kaico na dana amince ma yah abdool na tabbata yarda kayimin kiss din nan yammatan da kayi mawa sunfi dubu. Saukar mari taji har biyo ah kumatunta cikin mamaki suka d`ago kasu ita da shi ummie aysha ce tsaye gabansu tanata ta huci kafin pherty tayi magana abdool yayi mata mari ukku masu kyauu. ©Sadteeyeesh😘 [9/25, 9:04 AM] Sadeeya Luv: 71-80 PHERTY 👯 NA HALEEMATU LAWAL BALA (Serdeeyerh😘) Momy tace karki damu sati ukku ne kawaii kuma kinga yaxo daf da bikin kinsan tunda yaseer ya fara kawo k`arar ku ya sake kama ku ba k`arimin bala'ee xasuyi da abdool ba dan na tabbata baxai yarda ya bugeki ba haka kuma baxai yarda ya dake shi ba kinga xa'ayi b`atacciya kenan dan haka tafiyar tafi sauk`i. Sai da ta mayar da numfashi sannan tace bansan yarda akayi kika bashi jikinki ba pherty kin b`ata wayonki Allah ya taimake ki yana sown ki amman duk da haka nasan ko bayan auren sai kin tarar da wulak`anci a gidan abdool duk da kina jinin shi koda yake harda laifin mu. Tunda ta fara maganar hawaye pherty suka k`afe ta saki baki tana kallon momy cikin firgici. Tace momy bangane inda maganarki ta dosa ba momy tace babu komai karki damu xaki gane nan gaba. Tare suka fito da momy a falo suka tarar da abdool shi daya yana xaune kanshi ya d`au xafi kusa dashi taje ta xauna momy ta nufi d`akin mama tana xama ya kamo hannunta tare da cewa, Mami am sowrie plx baxan sake ba Kinji tace uhm waii yah abdool ni xaka sa ummie ta mara kuma ka d`aga hannu ka bugeni har bakina ya fashe kana ganin jini a bakina amman bai hanaka cemin in ka tafi in mutu aii inajin ko mutuwa kayi baxan mutu ba bare daga tafiya. Kallonta yake tayi yace nidai kiyi hak`uri amma nasan ko mutuwa nayi sai rayuwarki ta girgixa koda baki bini ba but ina sown tambayarki tun d`axu kin kifemin ciki sai da ta kwanto kanta ah kafad`arshi tare da cewa, Muje ina had`ama kayan saika tambayeni yace mexai hana in tambayeki nan tace nidai uhm uhm yace mami meyasa kikemin musu duk lokacin da xan tambayeki cikin shagwab`a tace Yah abdool kai d`in ne in ka fara tambayata kamar wani d`an jarida har sai nagaji da amsama marairaice fuska yayi tare da cewa to shikenan tunda bakya sow na tambayeki na hak`ura dan ban sown b`acin ranki. Shiru tayi tare dayin wani dan tunani tace to muje in had`a maka kayan. Yace ai na had`a fa tun d`axu. Tace to wa yace ka had`a aikin kane yace no aikin kine yi hak`uri daxu kece kika b`atamin rai tace muje to nidai muje a sake had`awa yace no jeki shirya muje in nuna miki wani abu. Tace aii shirye nake yace a'ah fita fa xamuyi tace to cikin xumud`i ta tashi doguwar riga ta saka ta shadda brown tasha aiki coffee brown tayi kyau sosai bata daura d`an kwali ba gyale ta sauka k`arami shima coffee brown kanta ta nad`e da gyalen tayi wani irin kyau Wanda ko ita sai da ta yaba ma kanta ta fesa turaren ta sweet deasire. Tana fitowa ta tarar dashi Yayi irin shirgar da take sow wato farar shadda da black din hula tace wow yah abdool kayi kyau fa yace wow maminah kinyi kyau fa cikin xolaya yayi maganar tace bari in d`auke ka hoto. Yace to harda gyarawa taita daukarshi ko tana cikin daukarshi ummie aysha tashigo yace yawwa xo ki dauke mu ummie tace to wayar ta ansa hannun pherty ya wani rugumota tai ta daukarsu ba k`aramin kyau sukayi ba. Nan take ummie taji su wani bala'ee burgeta ta dauke su yakai goma sannan yace barshi haka fita xamuyi tace Yayah ina xuwa yace no wannan tafiyar masoya ce ki Bari sai d`an jakaliyanki yaxo kema sai ku fita yana kaiwa nan ya ruk`o hannun pherty. Tafiya sukeyi suna fira cikin nishad`i yace plx ki bari iin tambayeki tace uhum uhum yace to shikenan babu inda ya shiga sai cikin estate din da gwamnati tayi sabbabi bakin wani gida ya tsaya horn yayi maigadin gidan ya taso ya bud`e get din aii tunda ga wajen gidan ta fara sakin baki, Gida ne babba anyi pant ashh & black ba k`aramin burgeta yayi ba aii suna shiga nan ta ida rikicewa falon ya d`au hankalinta sosai kujerun falon pink and blue but dark bata Ankara ba taji k`afarta ta nutse cikin wani lallausan carpet pink ne shima da blue amman kadan pink din kamar yarda blue yayi kadan a kujerun. Cikin d`akin yaja hannunta suka nufa shima harda falon shi an saka carpet purpple sai wasu pillow case an jera ah d`akin hatta pant falon purpple ne maganar abdool taji bayanta yace mami wannan gidanki ne ke kad`ai babu wanda yasan da gidan nan sai ke koda na siyeshi da sunanki na siya. Bata wani tsaya sauraroshi ba ta shiga cikin d`akin aii nan ta tsaya kallo royal bed ne purpple shima yayi wani irin kyau juyowa tayi xatama abdool magana ta kasa kawaii sai hawaye suka fara bin fuskarta yace no nifa bana sown wannan koke2 naki cikin sauri ta goge hawayen hannunta ya ruko suka dawo Arabian falo. [9/25, 9:04 AM] Sadeeya Luv: 81-90 PHERTY 👯 NA HALEEMATU LAWAL BALA (Serdeeyerh😘) Kan carpet din suka kwanta tana kwance gefenshi fuskarta na kallon sama shima haka cikin sanyi murya yace mami i luv u juyowa tayi tana kallonshi tare da cewa luv u too sweet bro juyowa yayi tare da rugomuta gaba d`aya a jikinshi, Yace karki damu ko baki fad`a ba nasan kina sownah plx kiss mee xaro idanuwa tayi😳 yace plx just kimin dan Allah tafiya ba xanyi gobe kika sani ko baxan dawo ba b`ata fuska tayi😡tare da cewa, Yace cemiki akayi kin b`atamin rai aii ra'ayinki ne sai kinji xaki iya dare nayi ki gayamin dan jirgin safe xan bi tace duk inda xaka kwana can xan kwana hanyar gidansu ya nufa da ita harabar gidan yayi parking, Yana k`okarin fita ta ruk`o hannunshi juyowa yayi yana kallonta fuskarnan a d`aure ya bude baki xai mata magana yaji bakinta cikin nashi wani irin hot kiss ya shiga bata haske ne ya cika musu fuska wanda sai da suka bud`e idanuwansu. Motar yaseer ce tsaye a gabasu Yayi musu full light cikin tsoro pherty ta xaro ido tana kallon abdool nan take maganar momy ta dawo mata batasan lokacin da tace na shiga uku ba. Abdool yace da akayi me dan ya ganki da mijinki malama fito muje dare nayi ki kwanta ki barci haka suka fito suka xagaye motar yaseer suka nufi cikin gida part dinshi ya nufa ita kuma ta nufi d`akin ummie harta yi shiri barci ya kira wayarta baice komai ba yace na manta ban baki takkadun gidanki ba kixo ki ansa tace to xata shiga d`akin sukai karo da yaseer Cikin sauri ta shige d`akin kallonta kawai yake cike da takaici yace yarinya kin mayar da kanki karuwar cikin gida Nifa ban sown irin wad`an nan maganganun fa yace sowrie to yimin plx tace uhm uhm yace biyu kenan tashi mu tafi gida tace to suna shiga cikin mota ya fisgeta bai sake mata magana ba har sai da ya shigo layin uguwarsu, Juyowa yayi tare da cewa ina xaki kwana gida ko gidan momy juyowa tayi tare da cewa kai ina xaka kwana yace i don't know marairaice fuska tayi tace am sowrie Suna xuwa ta bashi hot kiss yayi mamaki takaddun gidan ya bata tayi mai godiya ta shige gdnsu shima gidansu ya nufa yaseer ta samu falo da gudu ta shige d`akinta kallo ya bita dashi tare da tashi yaayi tafiyarshi daman dawowarta yake jira Washe gari karfe takwas abdool ya tafi ba bai samu yin sallama ta ita ba tana barci bata tashi ba kuma bai sow a tashe ta haka ya tafi duk da yasan sai sunyi daru da ita in taji ya tafi. Sai k`arfe gomaa ta tashi tana farkawa agogo ta kalla tare da cewa nashiga ukku wannan wane irin barcin asara ne nake wayar abdool ta fara nema amman a kashe cikin sauri ta fito falo babu kowa haka dukka d`akunan da kowa da gudu ta nufi gidansu abdool Mai gadi yace mai sunan manya aii duk basu nan sun tafi rakiyar abdool bai rufe baki ba saiga motocinsu na shigowa aikau ta rik`a hauka tana kuka tana fad`uwa kasa tana ihu kamar xararriya ai sai sukaita kallonta ummie aysha ce taxo gabanta, Tace yah abdool yace in gaya miki in kikayi kuka bai yafe ba aikau tanajin haka ta tashi ta goge fuskarta mutanen gun me xasuyi inba dariya ba tana ganin haka ta d`ad`aure ta Fara han harare-harare . . Agurguje. Bayan sati ukku abdool ne kwance a falon Hakeem da ke abuja waya ce manne a kun nenshi yace mamin ina abuja fa but hakeem nake jira ya shigo ban sown tahowa da kaya a mota kayan lefen xan bashi shi xai taho dasu daga can b`angaren tace nidai ka ajiyemai kayan ka taho tunda kasan sai yamma xai dawo yace owk maah. Dariya tayi tare da cewa plx mik`ewa yayi yace am serious gani a tsaye ma xan fita in shigo da kayan yana fita ya rink`a shigo da kayan set biyar ne na lefen bai bud`a ba bare in gano maki qawas. Kiranta yayi tare da cewa nan da awa biyu da rabi insha Allah ina cikin gida tace Allah ya kawo ka lafiya husby yace me kikace cikin dariya tace husby nace murmushi yayi tare da cewa lttr key din motar abdool ya d`auka da yake motarshi biyu. Yana tafiya yanajin k`ira'ar sudais suratul Maryam yanaji ban Ankara ba yaji wata qatuwar daff tabi ta saman motarshi nan take wuyanshi ya karye kafin ace kwabo gun ya cika ta mutane ko matsawa abdool bayyi ba nan take Allah ya d`auke abinshi Allahu Akbar kabiran... ©Sadteeyeesh😘 [9/25, 9:04 AM] Sadeeya Luv: 91-100 PHERTY 👯 NA HALEEMATU LAWAL BALA (Serdeeyerh😘) A dai-dai wannan lokacin pherty na kwance tana barci tun bayan gama wayarsu da abdool ta kwanta akan ta huta kafin ta tashi tamai girkin da yake sow tasan baxai wucce minti talatin ba barci takeyi mai nauyi koda ummie aysha ta shigo ta ganta tana barcin murmushi tayi tare da cewa almira kwanan ki nawa rabonki da barcin rana. Mama ma da ta shigo tashin ta fasawa tayi dan taga da alama barci ya mata dad`i mama ce tayi girkin. Cikin firgici Abba ya shigo gidan hankalinshi tashe mama naganin haka tasan ba lafiya tace abbansu meya faru yace ina pherty mama tace tana barci yace alhamdulillah sanninta ne kawaii babban tashin hankalin xuri'ar mu. Mama tace meke faruwa wacce irin magana kake yace AISHA bai tab`a kiranta da sunanta ba sai yau cikin kid`ima ta ke kallonshi yace Allah yayi ma abdallah rasuwa yanxu a hanyar shi ta dawowa gida daga abuja. Yana juyowa yaganta kwance ta suma tashin hankalI wanda ba'a samashi rana kafin yayi wani yunk`uri dady ya shigo bai lura da mama dake kwance k`asa ba yace mustapha ina phertymerh yace tana barci sai lokacin ya kula da mama dake k`asa kwance fidge ya nufa tana farfadowa suka nufi gidansu abdool. Koda suka shigo gidan sun tarar da gawar har ankawo ummie aysha da momy nata kuka kamar ransu xai fita momy tace ina pherty akace tana barci cikin kuka tace Ku gaggauta kimtsashi akaishi makwancin shi tun kafin ta tashi. Dai-dai wannan lokacin ta tashi tana tashi agogo ta kallah cikin sauri tayi wanka Tasha kwalliya amman sai taji gidansu shiru kamar ba kowa a gidan aranta tace kila ma yah abdool ya shigo suna gidan cikin sauri ta gama shiryawa farar shadda ta saka tasha aiki pink ta yafa pink din gyale sai kuma taji gabanta na fad`uwa ba k`ak`autawa. Har takai k`ofa xata fita kuma bugun k`irjinta ya tsananta cikin ranta tace k`ila ma yah abdool ne ya dawo tunda duk lokacin da yayi tafiya inajin irin haka in ya dawo but na yau dai ya tsananta. Gidansu abdool ta nufa tana shiga harabar gidan bata ga mai gadi a k`ofa ba tace yau baba ko ina akayi d`aga kan da xatayi sai taga ABULACE a harabar gidan ga mutane sunata alwallah nan take taji gabanta ya sake fad`uwa. Tana kaiwa k`ofar falon taji dady nacewa indai har aka kai gawar abdool pherty bata saniba ba'ayi Mata adalci ba yaseer jeka ka taho da ita taga gawar sah ko addu'a tayi mai d`agowar da yaseer xayyi yaga pherty tsaye tana kallonsu. Fuskar nan tayi wani iri ba annuri haka ta k`arasa shigowa falon momy ta nufa tare da cewa momy ina yah abdool ya iso ina barci ko? Kasa bata amsa tayi sai kuka juyawa tayi gun ummie tace ummie da gaske ne wai abinda naji dady na fad`a da gaske yah abdool ya rasu nan ma bata samu amsa ba gun Abba ta nufa tace Abbah yah abdool ya mutu da gaske cikin dauriya da nuna jarimta Yayi Mata nuni da bayanshi tare da cewa ya rasu phertymerh ga gawarshi nan je kima masoyinki addu'a. Cikin sauri ta isa gaban gawar tana budewa sai taga kamar yana murmushi kawaii sai taga abin kamar a mafarki ta fara karanta Mashi suratul yasin tayi mai addu'o'i sosai tana gamawa, Dady yaxo ya Kama kafad`unta tare da mik`ar da ita tsaye kusa da momy ya xaunar da ita har lokacin bata gasgata yah abdool ya rasu ba kamar an tsikareta ta tashi ta nufi gawar abbah ya rik`eta ta fusge tana isa gun ta yaye likafanin tana shafa fuskarshi. Tace yah abdool tashi ka fada musu mafarki nakeyi kamar daga sama taji yaseer na cewa miemie ba mafarki kike ba abdool ne ya rasu da gaske bai rufe baki ba saiga hakeem cikin kuka kamar yaro pherty na mik`ewa taji k`afarta bata daukarta sai lokacin kuka yaxo Mata mai tsuma xuciya tare da cewa, Haba yah abdool ya xakamin haka ya xa'ayi ka tafi ka barni bayan kasan baxan iya rayuwa babu kai ba kowa na falon sai da ya xubar mata da hawaye cikin sauri ta goge hawayen fuskarta tare da tashi tsaye ta gyara gyalenta tace yah abdool tashi mu tafi nasan baka mutu ba Juyawa tayi tace Ku dena kuka wallahi abdool dina bai mutu ba yanxu ne ma dai`dai lokacin dawowarshi ni wllh mijina bai mutu ba kowa na falon kuka yake abba yace ku dauke shi Ku kaishi masaukin shi cikin hargowar pherty tace wanne makwanci wllh Abba bai mutu ba dak`ar su momy suka rik`eta aka fita da gawar tana gani aka fita dashi. Cikiin kururuwa take cewa dady karku tafi dashi ban sake ganinshi ba sake rik`eta su momy sukayi wani k`arfi ne yaxo Mata ta fusge kanta daga hannunsu tafi su Abba da gudu dady ne Yayi mata kyakyawan ruk`o a kunnenta ya rad`a Mata kiyi hak`uri pherty nasan kinyi rashin masoyi ya kamata ki sakama xuciyarki dangana duk da nasan xayyi wuya hakan. Abdool bai cancanci kuka daga gareki ba addu'a xakiyi maii bai gama maganar ba yaji ta sulale k`asa a sume cikin sauri yace mama ku taimaka mana da ruwa cikin sauri suka runk`a xuba mata ruwan sanyi amman ba alamar rai a tare da ita...... ©Sadteeyeesh😘 Www.muhdabbagana.blogspot.com Www.abbagana.pun.bz Www.abbagana.blogmr.com [9/25, 9:04 AM] Sadeeya Luv: 111-20 PHERTY NA HALEEMATU LAWAL BALA (Serdeeyerh😘) Da sauri ta sake shi tare da sake duba hoton da sukayi da abdool sake kallon fuskarshi tayi tare da girgixa kai cikin d`aga murya tare da kuka take cewa nashiga ukku waii meke shirin faruwa dani ne?, Wannan wane irin mafarki ne nakeyi wanda idanuwa na sukaki bud`ewa har yanxu. Yaseer bai san lokacin da hawaye masu xafi aula xuba daga idanuwanshi ba tayi matuk`ar bashi tausayi cikin sanyi jiki ya isa gabanta tare da d`ago kafad`unta yace miemie kiyi hak`uri ba mafarki kike ba haka kuma ba barci kike ba. Cikin firgici take kallonshi tace yah yaseer da gaske yah abdool ya rasu? Kai ya d`aga mata kafin yace ya rasu phetymerh kiyi hak`uri munsan kinyi rashi wanda dole ya tab`a jikin ki amman ki yarda da k`addara da jaramtar da Allah yayi miki kowa da irin jaramtar da Allah yake mashi ke taki da rashin abdallah taxo miki. Sauraren shi kawaii take hawayen idanuwanta sun k`afe wata dauriya ce da natsuwa suka saukar mata hannunta ya kama tare da fitowa da ita daga cikin part din abdool. tafiya take amman bata ganin gabanta ko ina saka k`afarta takeyi har falon dasu momy suke ya kaita ya xarce d`akin momy yace momy bamu hijab a saka ma miemie "tace ka shigo da ita ciki" to yace tare da fita bayyi 5mnt ba ya shigo da ita. Kan gado momy ta xaunar da ita tare da saka mata hijab pherty jinta takeyi kamar ba mutum ba kamar ba ita ba har lokacin tana tantama da mutuwar abdool tana xaune hakeem ya shigo yayima momy gaisuwa yana kuka yana juyowa gun pherty itama hawayen takeyi kafin yayi magana ta rigashi "Yah hakeem da gaske dai yah abdool ya tafi ya barni" hakeem yace tafiya ko ta har abada pherty munyi babban rashi a xuri'ar mu amman bamu da yarda xamuyi haka Allah ya tsaro kuma yafi mu sown shi cikin kuka yake maganar. Share hawayen fuskarta tayi tare da cewa, ALLAHUMMAH FIRLAHU WARAHAMHU WAJ'ALIL JANNATA MUK`ALLABKA WA MASWAAKA YAH ABDOOL ALLAH YA HASKAKA MA KABARIN KA. Duk jama'ar dake d`akin suka amsa da amin momy ta share hawayen idanuwanta tare da kwantar da pherty a jikinta. BAYAN WATA BIYU Pherty ce kwance a part d`in abdool tana kallon d`akin cikin natsuwa wata irin rama naga tayi duk ta koma kamar ba ita ba sallama taji kamar daga sama cikin sauri ta juya yaseer ta gani cikin tsoro take kallonshi, Murmushi yayi mata tare da cewa miemie ya k`arin hak`urin mu cikin fad`uwar gaba tace Alhamdulillah cikin sauri ta janye idanuwan ta a kanshi inta ganshi gani take kamar taga abdool. ©Sadteeyeesh😘 [9/25, 9:04 AM] Sadeeya Luv: 101-110 PHERTY NA HALEEMATU LAWAL BALA (Serdeeyerh😘) Sai da aka xuba mata roba d`aya na ruwa sannan ta farfad`o wanda yayi dai-dai da lokacin da aka ida fita da gawar abdool daga cikin falo wani irin kuka ta saka mai tsuma xuciya wanda yasa kowa na falon kuka tare da cewa ya xakamin haka yah abdool bai dace ka tafi ka barni ba. Juyawa tayi tare da kallon momy tace momy dan Allah kice karsu tafi dashi wallahi bai mutu ba baxai iya tafiya ya barni ba momy saboda yasan numfashina tare yake tafiya da nashi cikin kunnenta momy tace ya kamata ki yarda da k`addara da irin jarabbatar da Allah ya miki ta rashin masoyi ki ringa yima abdool addu'a kuma kisani abdool ya amsa kiran ubangiji kuma xaki rayu.......bata k`arasa ba pherty ta saki wani ihun da ya rikita kowa tare da cewa ki dena momy bana sow. Can kuma tayi lamo tare da rufe ido kamar tana barci wanda yayi dai-dai da gama yima gawar sallah (Allahu Akbar) suna fita da gawar kamar an mitsini pherty ta xabura ta tashi xaune tare da fara surutai, Reality ya xakamin haka ka tafi ka barni? Haba yah abdool ba haka mukayi dakai ba kada kamin haka cikin kuka tace ma mutanen falon dan Allah kuce su dawo dashi wllh xai tashi. Kukane yaci k`arfinta amman duk da haka bata fasa surutun ba. Dan darajar Allah kuce su dawo dashi wane hali kake tunanin xanshi ga in na rasaka yah abdool nasan kana jina. Kalamai take wad`anda duk wanda ya ji xai san mutuwar ba k`aramin tab`a ta tayi ba dan ko iyayensu basuji mutuwar kamar yarda take jinta ba duk wanda yaji kalaman da takeyi yasan ba k`aramar kauna ke tsakaninsu ba. Cikin kuka ummie aysha tace kiyi hak`uri pherty kiyima yah abdool addu'ar samun rahama cikin masifa da kuka tace uban waye yace miki yah abdool ya mutu sai kuma ta fashe da kuka wallahi ummie mijina bai mutu ba wayyo Allah yah abdool. A hankali taji an dafa kafad`arta tare da rufe mata baki tayi shiru amman a xuciyarta tana tunanin duk Wanda ya rufe mata baki bai yi mata adalci ba yarda ya hanata ambatar sunan GUDAN JININ TA danme xa'a rufe mata baki bayan ansan tayi babban rashin jigon rayuwarta. Cikin sauri ta jiyo tare da buge hannun da aka rufe Mata baki dashi juyowa tayi cikin sauri mamaki ne ya lullub`eta duk da k`arancin muhallin hakan a wannan lokaci Halimcy ce tsaye fuskarta cike da hawaye sakin baki pherty tayi sai hawaye dake xuba daga idonta cikin rawar murya take magana muyi hakuri pherty wannan babban rashi ne mukayi kiyi hak'uri Allah ya jik`an abdool. Kalma mafi d`aci kenan da pherty ta tsani a fad`a mata kawaii sai taga raunin sown da Halimcy ke abdool rasa kome xata cema halimcy tayi sai Kama hannunta da tashi ta sauke shi daga kafad`arta guri ta samu ta xauna bata sake magana ba haka hawayen idonta sun k`afe har maxan suka dawo tana xaune kan gadon abdool (da yake can aka mayar da ita) Dady ne yace ma yah yaseer yaje ya taho mashi da ita yana shiga ya sameta da wayarta a hannun tana kallon hotunan da ummie tayi masu daren da xai tafi dubai hawaye ne ke xuba a idonta amman fuskarta murmushi takeyi. Gabanta yaseer yaje ya tsaya tare da cewa meimei da sauri ta d'ago kanta suna had`a ido ta tashi da gudu ta rugume shi tare da cewa daman nace musu baka mutu ba yah abdool amman sunata yimin musu ni nasan masoyina bai mutu ba.. TOFA KU BIYONI DANJIN YARDA XA'AYI PHERTY TA YARDA ABDOOL YA RASU. ©sadteeyeesh [9/25, 9:05 AM] Sadeeya Luv: 131-40 PHERTY 👯 NA HALEEMATU LAWAL BALA (Serdeeyerh😘) Yana fita ya d`au hanyar abuja cikin awa ukku ya isa birnin tarayya kayanshi ya had`a yaje yayi baking jirgi xuwa u.s gab da xai tashi ya kira Abba a waya tare da ce mashi wata tafiya ta kamashi yanxu xuwa u.s haka ya kira dady sukai mashi fatan sauka lafiya Ba tare da sunsa shi kadai ya tafi ba wanda mamansu pherty kawaii ta sani dan ita dashi tunanin su d`aya suna tsammanin ta ba abdool kanta. Tana kwance a inda ya barta tana ta barcinta cikin kwanciyar hankali tana mafarkin abdool d`inta. Kamar an mintsineta ta tashi tare da juyawa a iya tsawon rayuwarta bata taba shigowa part din nan ba nan ta fara tambayarta to meya kawoni nan kallon falon ta fara yi tana wani naxari ta sake juyawa, Gani takeyi kamar tasan falon tak`amemen hoton yaseer ne ya bata amsar abinda take nema da kakinshi na soja fuskar nan a d`aure kamar ba hoto xa'ai mai ba. Hakanan kawaii taga ya burgeta matsawa tayi kusa da hoton tana kaiwa kusa da gadon ta buge wani abu durk`usawa tayi da niyar d`auke ko miye abinda ta gani ne yasa ta daskarewa gun tare da tunanin meya kawota d`akin nan ma?. Wani photo ne tagani ita da yaseer da mutum yaga hoton xayyi tunanin tare sukayi shi hoton Yayi bala'en kyau kuma dukkansu dariya sukeyi a jikin hoton gani tayi ma dariyar batayi mar kyau ba d`auke hoton tayi tare da fitowa. Tana fitowa dady nayin parking din motarshi binta da kallon yake cike da mamaki dandanan fuskar shi ta sauya tare da cewa wato ni yaseer xai toxarta kenan in d`aura mashi aure da yarinya gudu, Sannan saboda tsabar raini ya kirani yacemin wai tafiya ta kamashi lallai yaseer..... Pherty ce ta katse mai tunanin shi tace dady sannu da xuwa tare da kamo hannun shi da d`ayan hannunta sukayi cikin gida. Babu Wanda ya sake maganar yaseer tunda Abba yaba dady hak`uri tare da cewa yayi mashi uxiri tunda da amincewar sa aka d`aura auren badan dady yaso ba yayi shiru ita kam hajiya pherty batama damu ba kawai daii tasan tana like din yaseer saboda kamannin shi da abdool. Kuma kullum yana kiranta a waya suna gaisawa wata ranar har su d`anyi firar karatunta sabo mai tsanani ne ya Shiga tsakaninsu dan har ta saba da lokacin kiranta yayi xata xo gaban wayar ta xauna. ©Sadteeyeesh😘 [9/25, 9:05 AM] Sadeeya Luv: [8:27PM, 7/27/2016] Aunty serdie luv😘: 141-150 PHERTY👯 NA HALEEMATU LAWAL BALA (Serdeeyerh😘) AGURGUJE BAYAN WATA UKKU Pherty na kwance tayi lamo kamar tana barci waya takeyi inba ka kasa kunnenka kusa da bakinta ba baxaka ji abinda take cewa ba amman da gani tana cikin nishadi wanda koni bansan dalilin shi ba (amman xanje gulma) Murmushi tayi tare da cewa nidai aa yah yaseer ban girma ba fa kaga yah abdool baimin irin maganar.......cikin d`aga murya da tsawa yace stop it miemie ya isheki hak......kafin ya k`arasa maganar ta kashe wayar tare da dafe k`irji. A ranta tace d`an bala'en mutum wannan bala'en baxaka saukeshi a kaina ba ka rasa da wanda xakayi kishi sai mattace kuma d`an uwanka ni baxan iya jarabar nan ba sa'a kaci dan yah abdool yamin magana a mafarki da tuni na kashe auren nan. Sake kiranta yayi tana gani tak`i picking message ya turo mata taki dubawa kuma tayi delete yaji shiru ya sake kira nan ma shiru Wani dogon tsoki yaja mtswwww tare da cewa yarinyar nan na neman rainani yau ko saina koma gida banda yarda xanyi da aurenta tunda ina sownta baxan iya rabuwa da ita ba xan rayu da ita amman ba rayuwar aure ba baxan iya kusantar ta ba. Cos baxan iya rayuwar aure da wacce k`anina ya sani ba duk sown da nake mata am so sowrie miemie and i luv u so much. Cikin sauri ya had`a koma tsanshi sai katsinan dukko tudu garin d`an marna ta malamai da gid`ad`o. [8:32AM, 7/28/2016] Aunty serdie luv😘: Fitowar ta daga wanka kenan tana goge jikinta da towel bata lura da mutum ba. Tana zama gaban madubi tana sharce kai tahango mutum zaune da kakin sojoji. Zaro ido tayi arude ta bude baki zatai ihu ya balla mata harara tareda daura hanunshi akan lebenta alamun tamai shiru. Kama bakinta tayi gam jikinta na mugun rawa. Ya taso cikeda tafiyar kasaita ya tsaya a gabanta haryanajin bugawan kirjinta yace"uban wa kika share?bakiga kirana ba kikaki dauka? Ta girgiza mai kai tana hawaye takasa magana. Fisgota ya sake yi ta fad`awa jikinshi ya rugumeta sosai tare da d`ago fuskarta halshen shi ya saka ya Fara lashe hawayen da ke fuskarta har ya gangaro bakinta nan take ya fara bata hot kiss ko motsi kasa yi tayi hannunshi nata yawo tsakiyar bayanta can kuma taji yana Neman xame towel din jikinta da k`ar ta fusge bakinta cikin sark`ewar murya ta fara magana. _plx yah abdool ka dena bana sow....._ bata k`arasa ba taji ya jefata kan gado da k`arfi. ©Sadteeyeesh😘 [9/25, 9:05 AM] Sadeeya Luv: 121-130 PHERTY👯 NA HALEEMATU LAWAL BALA (Serdeeyerh😘) Kusa da ita ya sake matsowa sosai kallonshi ta ringa yi gaba daya ya rikid`e mata ya koma mata abdool da sauri ta karaso gabanshi. Fad`awa tayi jikinshi tayi mai kyakyawar runguma har yana jin laushin dukiyar fulanin ta na take yaji jikinshi yayi sanyi tare dajin wani irin abu ya tsarga shi cikin kuka take cewa daman nace musu baka mutu ba yah abdool hakanan akamin musu, Cikin sanyi jiki ya d`ago hab`arta tare da cewa miemie abdool fa ya rasu ya kamata ki fuskanci rayuwa hawaye ne ke xuba a idanuwan ta tana girgixa kai tace nidaii aah wllh I missed ur yah abdool cikin sauri ta sake fad`awa k`irjin shi. Wani shock yaji ya kamashi dan wannan karon kab k`irjinta ya baje a jikinshi dandanan ta rikitashi har fuskarshi ta fara sauyawa hannu yasa yayi mata wata kyakyawar rugumar da sai da ta saki wata yar k`ara. Hannunshi ta kama cikin sauri har tana sark`ewa take cewa xo muje yah abdool muje gun dady nidai a d`aura mana aure yanxu. Kallonta kawaii yake dan ta riga ta gama kashe mai jiki gaba d`aya ta rikita mar lissafi a haka ta jashi har falon dady cikin murmushin da suka dad`e basu ganta dashi ba take magana. Dady munxo a daura mana aure ne wallahi ina sown shi cikin mamaki dady ke kallonta ya dad`e yana kallonta sannan ya fara kallon yaseer bai ga alamar komai a tare dashi ba sai dai reaction dinsa daya sauya wani murmushi dady ya daki tare da cewa to Alhamdulillah. Wayarshi ya dauka ya kira abbanta yayi mashi bayani tare da cewa yanxu in muka fita sallahr axahar sai a daura auren gobe yaseer din xai wucce sai ya tafi da matarshi tunda Allah ya kawo mana saukin wannan abun. 02:30 aka d`aura auren phertymerh da yaseer Allah sarki pherty matar mutum kabarin sah tana lik`e da yaseer tunda ya dawo daga d`aurin auren tana kwance kan k`irjinshi tana barci. Shikau duk lokacin da ta tab`a jikinshi wani mugun shock yakeji a jikinshi har yana tunanin Ashe haka abdool keji shiyasa kullum yake lik`e da ita Ashe haka jikinta yake matsalar d`aya ce abdool ya rigashi ga komai a gunta dandanan fuskarshi ta sauya A ranshi yace abdool ya fini sanin dad`in jikinki kenan meyasa na amince da wannan auren bayan nasan yarinyar nan saura ce sauran ma ta k`anina duk sown da nake miki dole in barki miemie. Cikin d`aga murya yake magana meke shirin faruwa dani yarinyar da nake sow kamar in mutu gata yau a matsayin matata but baxan iya rayuwa dake ba phertymerh sai dai kiyi hak`uri cikin sauri ya xameta daga jikinshi tare da fita daga d`akin. Part dinshi ya nufa ya fara had`a kayanshi cikin yan mintuna ya gama had`a kayan ko sallama baima kowa ba yayi tafiyar shi TOFA MASU KARATU MEKE SHIRIN FARUWA DA PHERTY NE ??? ©Sadteeyeesh😘 [9/25, 9:05 AM] Sadeeya Luv: [10:25AM, 7/28/2016] Aunty serdie luv😘: [10:08AM, 7/28/2016] Aunty serdie luv😘: 151-160 *PHERTY*👯 *NA HALEEMATU LAWAL BALA* (Serdeeyerh😘) Cikin masifa yake cewa wallahi duk ranar da na sake yi miki wani abu kika ambaci sunan abdool saina k`arya ki sakarya kawai baki ban amsata ta dalilin k`in d`aga wayata ba da rashin mayar min da amsar sak`ona ba wato ke kin girma ko. _shiru tayi dan ya riga ya gama tsorata ta_ [10:08AM, 7/28/2016] Aunty serdie luv😘: Badake nakeba?! Hanunta na bari tace ai bana wurinne. Zaro ido yayi yace duk randa na kiraki baki dagaba saina karyaki waeiya kawai. Sa kaya mutafi gidanmu Dad yace natafi dake. A firgice tadau kayanta zata shiga bayi yace dawo kisasu anan. Hawaye ya cika idonta hakanan ta juyamai baya tasa bra da kayan yanata binta da kallo. Ya rike mata hannu suka fito sukaima Dad da Mum sallama. Mum takirata gefe tabata magunguna tasha dana shafawa sanan tafito tasameshi a mota suka tafi gidansu dake cikin garin kasancewan dare yayi ya tsaya ya saimata abinci ahanya. Suka wuce batare daya kulata ba itakuma tai shiru. Hanyar government house taga sun nufa ita dai batace komai ba sai hawayen da takeyi gabanta na bugun tara-tara sai da suka wucce gidan gwamnati kad`an taga ya nufi wani get da ta hango sojoji da yawa a gun. [10:36AM, 7/28/2016] Aunty serdie luv😘: Gab da xai shiga get din ya juyo yana kallonta cikin harara yace xaki share hawayen nan ko sai na sakaki kukan mai dalili cikin sauri ta share hawayen tare da gyara mayafinta kallonta yayi tare da girgixa kaii. Tun a get taga anata sara mashi a ranta tace _dole yah yaseer ayi girman kaii irin wannan abu haka kamar wani shugaban k`asa._ Gida ne mai kyau sosai gidan ya burgeta kwaraii sai dai ba color din da take sow bane kitchen din ne kawaii ya yi mata d`akinta ya nuna mata tare da cewa bana sown k`axanta dan haka ki xage kiyi aiki dan amaryar da xan k`aro taxo ta samu gidanta yarda take sow. ©Sadteeyeesh😘 [9/25, 9:05 AM] Sadeeya Luv: *161-170 PHERTY👯* *NA HALEEMATU LAWAL BALA* (Serdeeyerh😘) Kallon shi kawai tayi tare da girgixa kai ta shige d`akin nan tasha kallo tare da mamaki dan babu abinda ya bambanta bedroom din da na gidanta wanda abdool ya bata daren da xayyi tafiya. Kwanciyarta tayi akan gado tare da daukar wayarta tana kallon pic'x dinsu da yah abdool wani inta gani tayi dariya wani tayi murmushi wani kuma tayi hawaye na k`arshen ne da ta gani wanda ta mak`alk`ale mai wuya suna dariya batasan lokacin da ta fashe da kuka ba. Da sauri ya shigo d`akin gunta ya nufa tare da ansar wayar hoton ya gani wani dogon tsoki yaja tare da fita da wayar tunda ya fita bai dawo ba sai da daddare ya shigo da take away na abinci da kaxa inda ya barta nan ya tarar da ita da yake tana fashin sallah. Fuskar nan tashi a d`aure yake mata magana ke bakya sallah ne kina kwance kamar wata mai yaron cikin koda yake ba xa'a iya ganewa ba shiru tamai kamar bataji ba gabanta yaxo ya xauna tare da shafo bobbs a firgice ta mik`e ta nufi karshen gado harda guntun kwallanta. Hararar ta yayi tare da cewa miye haka dan na tab`a miki abinda kika dad`e ba'a tab`a ba. Kallon shi kawaii tayi tare da cewa bangane ba yace baxaki gane ba kuwa tab`e baki tayi tare da cewa nifa gaskiya yah yaseer ka dena tab`amin jiki danni jikina na yah abdool ne tunda bai samu ba babu wanda xai samu. Wani kallon raini yake mata tare da cewa me xanyi dake saura face Allah ya rufa miki asiri kika rufama kanki da kikace kina sowna dan kinsan babu wanda xai dauki sauran wani saini da na xama dolenki. Kallon shi take fuskarta tab da hawaye tace Alhamdulillah kace na xama abar alfahari tunda har naba masoyi na abin alfahari na jarimin jarumai jikina na tabbata ko a haka aka tsaya mubar tarihi xuri'arm.........wani kyakyawan mari ne ya hanata k`arasa maganar. Kallonshi take hawayen idon ta har ya k`afe wani murmushi tayi mai ciwo tare da cewa Allah sarki yah abdool yanxu ne nasan nayi rashi na tabbata da kana raye bamu mai min wannan wulak`ancin Tana gama fad`ar haka ta fita daga d`akin. Tana fita yaji duk bai ji dadi ba koba komai k`anwarshi ce matsalar d`ayace baxai iya bata hak`uri ba. A d`akin ya kwana Dan karma ya fito tayi tunanin lallashinta yaxo yi ita kuma tun a daren ta dauka key motarshi da yake tintac ne jikin motar harta fita security's din suna sara mata duk a tunanin su yaseer ne. Sardauna estate ta nufa babu inda ta xame sai gidanta da abdool ya bata haka ta shiga cikin gidan tana sharar hawaye tana shiga falonta taci karo da hular abdool da ya ajiye ranar da sukaxo. Daukar hular tayi tare da kaita hancinta tana shinshinar kamshin turaren abdool wani kuka ta saka mai tsuma xuciya tare da cewa. _ya Allah ka kai haske kabarin yah abdool ka sada shi da rahmar ka._ *Agurguje* sai da tayi sati d`aya a gidan babu neman da ba'ayi mata ba amman shiru ba labarinta haka yaseer ya baxa yaranshi ko ina dan neman saboda dady yace indai bai nemota ba kotu ce xata raba su ba karamar nadama yayi ba, Dan duk ya fits haiyacin shi gashi ko ina bayan samun sauk`i mama ce mai kwantar mai da hankali ita kuma yanxu kunyarta yakeji gani yake kamar tana mai kallon marar adalci kamar yarda mum dinshi kemai. ©Sadteeyeesh😘 [9/25, 9:05 AM] Sadeeya Luv: [8:15PM, 7/29/2016] Aunty serdie luv😘: 171-180 *PHERTY*👯 *NA HALEEMATU LAWAL BALA* (Serdeeyerh😘) Yunwa ce ta isheta dan bata da abinci a gidan daga mult sai cake shima a estate d`in take siya saboda ta samu kud`i a motar yah yaseer ga ciwon kai dake damunta kasuwa taje tayo _shopping_komai da xata buk`ata. Harta d`auko hanyar dawowa gida kome ta tuna oho sai ta juya tana tafiya tanajin wak`arta _banky w yeso_tana bin wak`ar cikin kwanciyar hankali harta isah wani k`aton asibiti mai suna *Fiddausi Sodangi special hospital* da gani kasan na kudi ne saboda tsaruwar shi tunda ga waje shiga tayi tagama abinda takeyi nidai ina waje ina jiranta. Mamaki ne ya kamata ganin harabar asibitin cike da sojoji duk sun yi tsaitsaye gun motarta cikin isa da gadara ta isa gaban motar tana wani cin magani tana xuwa xata bud`e motar taga sun taso mata gaba d`ayansu sun xagayeta. Bata wani damu ba ta bud`e motar ta shiga suma kuma basu ce mata komai ba harta jefe motarta a titi tana shan sweet tanajin dadin sweet d`in kuma k`amshin sweet d`in na tuna mata k`amshin bakin yah abdool ranar da yayi mata kiss murmushi tayi tare da bugun sitiyarin motar. Tana shiga cikin gidan ta rufe k`ofarta Amman ko bada baya batayi ba taji ana kwankwasa kofar mamaki ne da tsoro suka dirar mata bata ida tsorata ba sai da taji maganar yah yaseer cikin d`aga murya yake cewa in baxa'a bud`e k`ofar ba Ku karya ta mana cikin masifa ta fara magana Wallahi duk wanda ya karyamin k`ofa kotu ce xata rabani dashi kuma baxan bud`e ba aii gida nane masoyina ya bani. Tunda ta fara maganar yake murmushi dan shi dariya take bashi. Yace plx ki bud`emin miemie wllh muna cikin tashin hankali anata nemanki gashi gobe ne auren Hakeem da ummie aii da gudu ta tashi ta bud`e tana budewa ya bita da sauri ya shiga tare da rufe k`ofar. Kallo ya bits dashi riga da wando ne jikinta na pakistan ta rufe kanta da gyalen kayan iya kashi wuyanta yaga yadda rigar ta matse bobbs dinta har ana gani shatin bra ta. Cikin ido yake kallonta tare da cewa da auren nawa kike yawo haka saboda kin xama yar iska ko ke gaki kinsan dadin maxa wane shegen ne ya kawoki gidan nan tsoro ne ya hanata magana dan ya matseta a bango fisgo hannunta yayi suka shigo cikin gidan yana kallon gidan ciki da bai sake fisgota Yayi suka fito daga gidan. Har suka fito harabar gidan inda yake cike da sojoji suna tsaitsaye kowan ne da bindiga turjewa tayi tare da duk`ushewa k`asa cikin hargowa yake magana wallahi inbaki tashi ba xan d`aukeki yar iskar ban........cikin masifa ta katseshi wllh ni ba yar iska bace Allah ya had`a ka da yar iska [8:47PM, 7/29/2016] Aunty serdie luv😘: Mugu kawaii bakinta ya buge har saida ya fashe tare da cewa xaki tashi ko saina d`auke kine banxa tayi maii sungu marta yayi sojojin na ganin haka da sauri suka bud`e mashi bayan mota yana rugume da ita suka shiga motar. Sun d`an fara tafiya kadan ya fara goge mata hawayen tare da share mata gefen bakinta da jini ya fito akan cinyarshi ya d`aura mata kanta fuskarta ya fara shinshina tare da d`ago kanta ya fara kissing dinta ko ina a fuskarta har yaxo bakin ta shiru tayi mai kamar bataji ba. Bobbs dinta ya fara shafawa tare da hankad`e mata riga ya xura hannunshi gaba d`aya yana murxawa da k`arfi wani ihu ta saki tare da cewa ka bari na gayama ni ba yar iska bace wallahi xan tarama mutane. ©Sadteeyeesh😘 [9/25, 9:05 AM] Sadeeya Luv: 181-190 *PHERTY*👯 *NA HALEEMATU LAWAL BALA* (Serdeeyerh😘) Bakin shi ya saka cikin nata ya fara tsotsa da karfi yarda yasan xataji xafi tare da matse bobbs dinta tayi wani wahalallen ihu cikin masifa yace dallah malama yimin shiru munafuka abinda kika Saba ana miki ne nayi maki xaki ringa pretending bayan kin saba da komaii babu abinda baki sani ba kina tunanin xan iya yin wani Abu dake ne famko kawai dake. Batace komai ba tayi shiru saboda xafin da bakinta keyi kamar ta cireshi ta yar gashi har lebanta yayi jaa haka suka isa gida tun a mota yayi ma dady waya tare da fad`a mashi suna tare da pherty sunma wucce gida. Tana shiga d`akinta ta saka ma k`ofar key tare da sulalewa gun ta fara kuka da k`arfi har yana jinta daga falo da sauri ya isa k`ofar amman yajita gam yaita kwankwasawa tak`i bud`ewa sai ma wani sabon gunjin kukan da ta fara haka tayi mai isarta har barci ya d`auketa . Sai gab da magrib ta tashi daga barcin wanka tayi tare da yin sallah ta d`auko wata yar ficilar rigar barci bak`a bata da bambanci da gidan sauro ko pant bata saka ba bare bra haka ta fito falo. Tana tafe tana girgixa jikinta yana kallonta har ta shiga kitchen da wak`a ta fito a bakinta wakar faty nijar ta DUNIYA a inda take cewa, _in na kalli sama wataran xanga babu tauraro ko cikin mutane wani mai gida akwai gwaro_ Yana jinta yasan da shi take k`afa yasa mata takusa fad`uwa ya chapkota d`aukarta Yayi babu inda ya sauketa sai kan gadon d`akinshi rigar jikinta ya fara k`ok`arin cirewa yana cewa ni xakiyi ma iskanci wato kin kwana biyu bakiji namiji a jikin kiba xakixo kinamin habaici. Tanaji tana gani ya cire mata riga bobbs d`inta ya tsaya kallo tare da kai bakinshi yana tsotsa kamar ya samu sweet wani hot kiss ya fara bata har ya gangaro cibiyarta da sauri ta kwala ihu yayi banxa ya kyaleta. Sai da ya tabbatar da ta gama jigata sannan ya fara neman hanyar shigarta amman abin mamaki yaga babu hanyar haka ya fasa ta da k`arfi wanda yayi Sanadin suman ta sai dai kawai yaji bata lumfashi. ©Sadteeyeesh😘 [9/25, 9:05 AM] Sadeeya Luv: *191-200* *PHERTY*👯 *NA HALEEMATU LAWAL BALA* (Serdeeyerh😘) Sai da ya gama abinda yake sannan ta kula da bata lumfashi da sauri ya tashi fidge ya nufa ya d`auko robar ruwa ya shiga yayyafa Mata amman ina babu alamar xata farfad`o. Ruwan wanka yaje ya had`a mata ya sungumeta toilet ya nufa da ita yana sakata cikin ruwan tana jan ajiyar xuciya da k`ar ta bud`e idonta dan wani irin ciwo kanta ke mata tana gananin shine ta rufe idonta gam. Yaseer yayi wata irin nadama wacce take sashi jin kunyar ta saboda xargin da ya rik`a yi mata ga ita kuma tun daga ranar bai sake ganin ko da k`afarta falo ba yana sown xuwa amman kunya ta hanashi sai da sukayi kwana ukku a haka. Ranar da suka cika kwana ukku ta fito xata kitchen daga ita sai wata yar best iyakarta cinyarta gashi ta kamata sosai haka ta fito tana kallonshi sai da ta shigo tsakiyar falon tukun tace ina kwana cikin sauri harda hard`ewar harshe ya amsa. Lafiya lau miemie ya jikin ki shiru yaji koda ya d`ago kanshi harta bar falon tashige kitchen murmushi yayi kawaii dan yasan xai shawo kanta da lallashi da darajar kamanninshi da abdool. Haka dai ya riga binta kullum har yasamu kanta tana d`an sakewa dashi shak`uwa mai tsanani ta shiga tsakaninsu haka dai suka fara soyayya. *BAYAN WATA BIYU* Kwance take a jikinshi tana wasa da hannunshi take mai magana plx yah yaseer ka barni inje dinner su yah hakeem yace no king fa baki lafiya kawai ki hak`ura da dinner nan shiru tayi kamar baxa tayi magana ba can kuma tace to shikenan tare da mik`ewa ta nufi hanyar fita cikin xafin nama ya tashi ya ruk`ota tsayawa tayi cak batayi k`ok`arin kwatar kanta ba dan batasan dalilin ruk`o da ya mata ba. Sai da ya rugumeta sosai tukun yace fushi kikayi tace fushin me yace na hanaki xuwa dinner mana tace uhm-uhm ko daya aii ra'ayinka ne ka barni ko kar ba barni ban damu ba kawaii dai banji dadi ba dan na tabbata inda yah abdool ne k`afata k`afar....... Bakinshi ya saka cikin nata hakan ne ya hana k`arasa maganar. A gurguje Bayan shekara d`aya pherty ce xaune da wani baby boy a hannunta tanata faman yi mashi wasa shikam yanata dariyar shi ta jarirai yaseer yaxo ya xauna kusa dasu tare da cewa miemie kinga ba Xaki b`ata abdool da k`uya ki dena Mashi wasa dariya tayi tare da cewa. Wallahi sai nayi mai wasa yo kawai sai in k`i yima yayana wasa inma xaka Lura ban fiye sown ana daukar min yaro ba kallonta yake tayi yana murmushi.. ALHAMDULILLAH SADAUKARWAR LITTAFIN TAKU CE MAKARANTA SHI. GINGINA GAREKI AYSHA MUHAMMAD (MAMAN ABD SHAKUR) BAN MANTAKI BA MUM ALBANY GAISUWARKI NA KUSA KAUSARA DA UMMIE AYSHA. KINFI KOWA JIRAN NOVEL DIN NAN TEEMAH LUFF. BANXAN MATAKU BA PHERTY DA MISS AYSHER INA MIK`A SAK`ON GAISUWATA GAREKU MASOYA NA A KO INA KUKE A FAD`IN DUNIYA NA GODE ALLAH KUMA YA SADAMU DA ALKHAIRINSAH BAN MANTAKU BA MEMBERS D`IN GROUP'S D`INA ⓂMUK`ARU DA JUNA YAN UWA AND ⓂATAN KWARAII TAKU DAICE AUNTY SERDIE LUV Www.abbagana.pun.bz Www.abbagana.blogmr.com Www.muhdabbagana.blogspot.com
Share:

Tallata Kayanka

Guide Tricks Blog

Be With Me Technology

Popular Posts

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).