shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wanda aka fi sani da hausa novel wanda ni Muhammad abba gana nake rubutawa dan wayar tare da fadakarwa ga mutane a yanayin da muke ciki.

Wednesday 26 August 2015

INSIYA*****12

insiya.jpg

INSIYA 12


********NA**********

muhd-Abba~Gana



yace toh baby na zauna muchi nace masa a'a wallahi na koshi yace to ga sakonki koh shima kin koshi? sai nayi murmushi na ansa tare da cewa na gode nayi ajiye shi a gefe yace a'a insiya lafiya kika ajiye shi sai kace ba wayyay ba kuma kin san in ba ka sha lemo da sanyinsa ba ai ba ka sha komai ba gwara ma ka sha ruwa".
nace to kaci abincinka mana zan sha yauwa baby ko keh fah sai na faki idonsa na dauko shi a karkashin kujera dana boye na aje wancan sai na bude na kama sha sai danayi rabi sannan na aje na zubawa sarautar Allah ido shi kuma yana kallona yana murmushi sai na kama hamma karya babbyna kai dai baccine kike ji? nace yaya bacci nake ji yace toh babbyna aje ayi bacci lafiya sai na tashi na shiga dakina ina tangadi kamar wacce ta sha barasa shi kuma mugun dan iskan sai murmushi yake yi.

na shiga na kwanta kamar mai bacci sai can naji shigowarsa da sanda kamar wani barawo
nikuma sai na dade rufe idona kamar mai baccin sai naji yana kirana nayi mar shuru kamar banji ba sai naji yana cewa .
yauwa tayi bacci bari inyi maxa in cika umurnin hajiya kai ni ma zan sha lagwada wai!!! masha Allah!! tsarki ya tabbata ga wanda yayi wannan yarinyan" yana yi yana cire kaya daman ni ina makale da wukata wanda Abba gana ya ban wanda ya dauko a kicin mai kaifi domin kare kaina daga sharrinsu lolz!


muhd-Abba~Gana


www.abbagana.pun.bz
Share:

INSIYA*****11

insiya.jpg

INSIYA 11



*********NA***********

muhd-Abba~Gana


sallamar jamilu ce ta tsayar da ni daga tunani da nake" amen wa'alaikassalam hajiya insiya lafiya kuwa na ganki kamar mara lafiya??
nace wallahi na tashi ne naji kaina yana yi min ciwo Allah sarki insiyata Allah ya baki lafiya nace"ameen yace bari infita kasuwa daman shigowa nayi na ga ki tashi lafiya sai na tarrar da kanki yana yi miki ciwo Allah ya baki lafiya na kuwa na amsa da ameen yace to me kike so in siyo miki? by muhd abba gana
nace babu yace haba insiya sai kace ba wayayya ba don Allah me zan siyo miki? to ka siyo min alewa yace dame kuma? da lemon wanne iri? sai nace "dew" yace to shikenan babby na sai na dawo,
na ce to a dawo lafiya Allah ya kiyaye hanya Allah ya tsare ka da sharrin karfe yace ameen baby na shiyasa nake dada sonki wallahi,na tafi "to sai ka dawo"

yana fita naji hawaye yana zubomin nan na kada kan gado ina kuka saboda bakin ciki,yau ni insiya naga ta kaina ana zaton wuta a makera sai gata a masaka ni wane irin taimako zanyi wa kaina?
nan na tashi zaune ina tunanin sai wata zuciyar take cewa haba insiya sai ka ce ba mai ilimi ba? ni dai a ganina kawai kiyi maza ki siyo irin lemon da kika ce mai sai ki boye shi idan ya kawo miki wancan lemin to sai kiyi sauri ki canza shi sai ki kama shan naki.ai kuwa hakan akayi raddau
kuma insiya ki kasan ce mai taimakon kanki ga sa min wani abin da xaki ji mishi ciwo sosai dan kar ya aikata komai a kanki.kuma ki kasance mai yawaita addua insha Allah Allah zai kare ki"haka dai zuciyata tata sakesake tunani.......

************************
ina zaune wajen misalin karfe takwas dai dai naji shigowar jamilu nan take gabana yafadi zuciyata ta kama duka uku-uku yau ni INSIYA ina cikin tashin hhankali gashi ba kowa a gidan duk sun fita.
sallamarsa ce ta tsaida ni da tunanin dana ke "sannu da zuwa" yauwa babby na sai na tashi nace bari na kawo maka abinci "toh baby nah na tashi jikina duk yayi sanyi na dauko masa ga abincin....toh fah!!


muhd-Abba~Gana


www.abbagana.pun.bz
Share:

INSIYA*****10

insiya.jpg



INSIYA 10


********NA**********


muhd-Abba~Gana


ai kuwa sai naji hajiya tana cewa "aina sameta ina ta kwantar mata da hankali ina karya mata da kai har ta yarda tana sonka kuma kasan abinda nake so da kai?
yace a'a hajiya sai kin fadi tace to kafin kafita ka shiga dakinta ka zauna kuyi hira sai ka tambayeta mevtake so ka sai mata nan shegiyar xatace maka lemu take so idan ta fada maka to sai ka siyo mata na roba sai ka bude kasa mata wannan kwayar ka jijjiga har sai ta narke sai ka kai mata.
nukuma zamu fita da alhaji amma kafin tara da rabi kasan abin da kayi kaga idan muka yi haka sai muce ai da ita da tanimu mai shara aka kamasu suna tskanci.bayan mun dawo da alhaji sai na shiga dakin ta na gansu,to wallahi ina fada wa alhaji haka sai ya koreta daman yace shi wallahi yarinyannan so yake tabar masa gida,kaga idan ta tafi to dukiya ta zama ta mu sai yadda muka yi da ita".
nan suka kwashe da dariya sai ya ce hajiya wallahi shiya sa nake dada sonki kuma nake alfahari da ke kuma hajiya dan Allah ina so a canza min mota"nan ta kwashe da dariya tace haba jamilu motar mai idan da akwai kudin jirgi ai saina sai maka,ballantana mota kaga tashi yi maza ka je wajenta,to hajiya an gama bari in tafi in sameta da sauri na tafi dakina nikoh abbagana ina biye da ita a baya,tana rawan hiki sai salati nake da neman tsarin wajan ubangiji.Allah ya kare ni da sharrinsu..........



muhd-Abba~Gana


www.abbagana.pun.bz
Share:

INSIYA*****9

insiya.jpg



INSIYA 9



********NA**********


muhd-Abba~Gana




09039016969


nan hawaye ta kama zubowa daga ida nunta jikinta yayi sanyi tsoronta ya kamani zuciyata takama addua domin tasha yi min makirchi ta hanyan yimin kuka dan sai ka rantse da Allah da gaske take.naji maganar hajiya da sauri na dago kaina domin kaina tun lokacin da naxo a sunkuye yake sai naji tace "insiya' nace mata na"amm


insiya dan Allah ki taimaka mana kar ya shiga cikin wani hali dan yace wallahi baxai auri kowa ba idan ba ke ba shiyasa hankalina ya kara tashi dan Allah yata ta kaina ki so shi kinji nace hajiya ba komai kuma na yarda dan ba zaki yi zabar min abinda ba shi da amfani ba
tace yauwa yata saisa nake sonki saboda hankalinki kuma nayi murna da wannan hadin sai dai yanzu kuma na zama suruka ba rashin kunya nan muka kama dariya na ce hajiya bari inje in gyara lafiyata tace Allah yayi miki albarka [hmmmm albarkan muna furchi] nace ameen hajiya ni dai na tashi ina tunani do ni dai ban taba jin irin wannan kyakkawan lafazin ya fito daga bakinta ba in dai ba mugunta zata shirya ba. by muhd abba gana
kuma ni dai abin da yake bani mamaki domin ko wata bakwai ba a yi ba ya yiwa wata ciki da kyar aka kwantar da maganan amma wai shine xai ce yana sona? har hajiya wai ta sa baki a maganar ni abin yana bani mamaki anya ba wata mugunta suka shirys ba? Allah ya kareni da sharrinsa.
bayan kwana biyu da maganar na tashi zan je in gaidar da su abba na shiga dakin abba na tarrar ya fita kasuwa na fito na nufi dakin hajiya aikuwa Allah ya taimakeni nazo a dai dai jinayi suna kulleh wata chakwakiya da jamilu dan haka sai ta labe tare dani abba gana naji abinda zasu ce.hmmmmmm rayuwa kenan!!!!



muhd-Abba~Gana


www.abbagana.pun.bz
Share:

Tuesday 25 August 2015

INSIYA*****8

insiya.jpg



INSIYA 8



********NA**********

muhd-Abba~Gana




nan hawaye ya kama zubo min dan har yau ban taba zuwa gidan abban yusra ba daga ya zo zai tafi da ni sai hajiya ta hana nan na kama tafiyata duk jikina ya mutu.
ina shiga cikin gidan sai ji nayi an rufe ni da duka ke yar iska ana baki wahala zaki bishi koh?? to mai sa baki bishi ba?
na ce ai dan kin hananine kuma wallahi yakara zuwa sai na bishi mari ne ya tsaidani kaji yar iska eh toh ba laifin ki bane kin tsotsi a nono ne shi yasa nace eh wallahi na tsosti amma kuma na alherine nan naji ta rufeni da duka, nikuma gani da taurin zuciya (kamar maryam lol!) nace hajiya wallahi kar kikara dukana
sai naji ta kama sallati'la'ilaha illahu, insiya haka kika koma? nayi banza da ita na tashi na kama tafiyata don ko wahainiya ba zata nuna min tafiyar kasaita ba, ballantana mace mai ji da kanta nan na barta tayi ta sororo kamar wacce kwai ya fashe wa a ciki.
***********************
bayan tabka wannan sai naji hajiya ta kirani "insiya" na amsa mata na"amm tace zo nan mara mutunchi akan jamilu yace yana sonki shine kika zazzage shi? har da ce mai dan iska ke ba a ce mii yar iska ba sai ke ce zaki bude baki kice mai dan iska? to wallahi ko ki yarda ku yi soyyaya nan ko kuma na sakaki a cikin kangi mai wahala(wa'iya zubillah) keh in banda abinki xai rufa miki asiri ya aureki shine har da wulakantashi? haba insiya dan Allah ki yarda ya aureki kinga ni ban taba haihywa ba saboda haka ne na dauko su nake rukon su ga shi yanzu jamilun ya isa aure kuma tun suna yan yara nake tare dasu dalilin haka ne nake tambayarsa akan aure yake ce min wai ke yake so amma kina wulakan tashi".





muhd-Abba~Gana


www.abbagana.pun.bz
Share:

Monday 24 August 2015

INSIYA*****7

insiya.jpg



INSIYA 7



********NA**********


muhd-Abba~Gana



wallahi alhaji bata da lafiya abin data ce dashi kenan yace Allah sarki insiyata shine kika rame haka?

abba ni dai zan bika sai tace haba INSIYA yar baba wani abu muke miki da ba kya son zama da mu? by abba gana tana yi tana dariya tare da hararanta nace A'a hajiya ni so nake kawai in bishi tace to ki bari idan kin sami sauki sai yazo ya tafi da ke jin haka sai nayi shiru ina tunani don ni nasan lafiyata klau sai bakin ciki da ya sani na rame ba dan Allah ya taimake ni ina da tsiwa ba ai da sai dai a dauki gawata kamar yadda aka dauki gawar ummah.


maganar abban yusurace ta tsagaitar min da tunani da nake sai naji yana cewa insiya ki bari idan kin sami sauki sai nazo mu tafi to abba Allah ya kaimu "amin' insiya to hajiya ga wannan dubu goma ki ajiye mata ga kuma dubu biyar naki a'a alhaji baka rabo da abin arziki ba komai hajiys to an gode Allah ya kara arziki "ameen" tace alhaji naji ance wai wannan siyasar ka fito a dan majalisa shugaban kasa? yace eh hajiya muna nan muna nema toh Allah ya bakusa'a ya amsa da ameen hajiya,insiya zan tafi sai na dawo ga dubu daya ki kashe toh Abba na gode sai na tafi na rakashi har motarsa ina ji ina gani ya tada motarsa ya tafi.




muhd-Abba~Gana


www.abbagana.pun.bz
Share:

INSIYA*****6

insiya.jpg



INSIYA 6



********NA**********


muhd-Abba~Gana






to kinga halin da nake ciki nan hawaye ya zubomin Allah sarki tun lokacin da na ke bata labarin sai kuka ta ke nan na share hawayena nace ki tashi ki tafi gida kar dare yayi miki to kawata Allah yaji kanta Allah yayi mata rahma"ameen" ki gaida gida
yau shekara daya da rasuwar ummina ina zaune ina karatun alkurani mai girma sai ga yayan ummina da gudu na tashi na rungume shi ina murna a'a insiyata ya kike??
sai jin hawaye nayi yana zubo min kafin inyi magana hajiya ce ta tari bakina tana dariya wacce ta kunshi kalmomin guda uku,shin ta muguntace,ko ta murna ce ko kuma ta zamu hadu inya tafi? Allah shine masani




muhd-Abba~Gana




www.abbagana.pun.bz
Share:

INSIYA*****5

insiya.jpg



INSIYA 5



********NA**********


muhd-Abba~Gana



sai nake tambayarta amma suna zuba wa ya yan nata da take riko? sai tace eh a rabon ki ake kakkara musu sannan nace ki tafi.by muhd Abba gana

yamma koh tayi an gama abincin dare sai na shiga kicin na zubo abinci na zauna naci na koshi nan hajiya jamila ta karna masifa kuma tace wallahi sai dai abban namu kar ya ci abinci dan sai ta dauko abincin nasa ta bawa jamilu ashe ni abincin jamilu na dauka.aikuwa haka akayi abba ya zo yace ina abincinsa? hajiya ta kwashe abinda nayi harda kari ta gaya mar tana kuka sannan a karshe tace wallahi ta gaji da wulakancin da nake mata gaskiya gwara ya dauki mataki nan ya tashi a fusace yayi dakina ya rufeni da duka kuma yace idan na kara yi mata wani abu sai na bar masa gida har da rantsuwarsa.oh duniya



muhd-Abba~Gana






www.abbagana.pun.bz
Share:

INSIYA******4

insiya.jpg



INSIYA 4


********NA**********

muhd-Abba~Gana


hanan inaji ina gani aka dauki mahaifiyata a makara a wannan lokacin ne na ji na tsani duniya nan na ga an dauketa gudu nayi xan rike makarar kar a kaita.da gudu mutane aka taho a ka rike ni,na fadi sumammiya, hanan abinda ya bani mamaki shine wallahi hajiya jamila tana zaune a lokacin da za a kaita tana tauna cingam da mutane suka mata magana sai tace ai duk wanda ya mutu ya mutu sai dai kuma a yi masa addu'a ranar sadakar uku kuwa unguwa ta tafi wai yau ake bikin kawarta kuma sune masu aiki.by abba gana
hmmm yau shekarata biyu da gama karatu kuma takarduna sun yi kyau amma hajiya taki a bari akaini gs wulakancin gobe daban na yau daban wai yanzu ma sai dai inje kicin in debi abinci a tukunya kuma idan naje kanzo nake gani haka nake kankara wanda na samu delu mai mana girki nake tambayanta ya yanzu ba a bani abinci take cemin hajiya ce ta ce kar a kara baki abinchi wai idan inaso sai naje tukunya in kankari kanzo tunda shima abincine.hmmm Allah karabamu da irin wayan nan iyayen



muhd-Abba~Gana



www.abbagana.pun.bz
Share:

INSIYA*****3

insiya.jpg



INSIYA 3



********NA*********

muhd-Abba~Gana


09039016969


maza ki kawo min ruwa zan sha" to ummina na tashi da sauri na je na debo mata ruwa,kafin in shiga dakin sai naji ummi na yin wani irin numfashi tana salati da gudu na karasa wajenta ,"ummi ga ruwan naji shuru na tabata na ji shuru duk jikinta ya saki.


innallilahi wa'ina ilaihi raji'un" nan na kwalla mata kira da karfi, ummi! ummi!! ummina!!! na shiga uku mutuwa bakiyi min adalciba, mutuwa kin dauke min sanyin idaniyata mutuwa kin sakani cikin kangi mai wahala tun ina yin kukan har kukan ya daina fitowa saboda tashin hankali nan naga yan gidan mu sun fito mahaifina a gaba sai yan aiki da wanda kishiyar babanmu take riko su uku amma ba munafukan abbanmu yana ganin hakan ya dafe kai nan ya kama addua yana cewa Allah yayiwa mace mai hakuri rasuwa Allah ya ji kanta Allah ya yi mata gafara"ammen sukace bakibdaya



muhd-Abba~Gana


www.abbagana.pun.bz
Share:

Sunday 23 August 2015

INSIYA 2

insiya.jpg



INSIYA 2


*********NA**********


muhd-Abba~Gana


insiya ki daina kuka,Allah ne ya jarrabeki da wannan hali da kike ciki" ni ummina kina tayar min da hankali da irin wadannan kalaman masu tada hankalin duk wani mai hankali"
ina kuka ina fada ummina ke ina zaki? ki sani cewa ke ce sanyin idona, ke ce mai share min kukana.ummina kin san mahaifinmu baya sona ya fi son yayan rukon hajiya, to ummina ina cikin wannan tashin hankalin zaki tafi ki barni?
sai gani nayi ummi tana hawaye "insiya ke nan,kina ba ni tausayi a irin kalamanki,amma ki sani cewa ,Allah yafi sonki akan son da nake miki.kuma shi ya jarraba ki da shiga cikin wannan hali................insiya"

"na'amm ummina" insiya Allah yayi muku albarka Allah ya rabaku da duniya lafiya"

""Amin ummi".



muhd-Abba~Gana


www.abbagana.pun.bz
Share:

INSIYA 1

insiya.jpg



INSIYA


********NA**********

Muhd-Abba~Gana

Ranar juma'a ummina ta rasu sakamakon ciwon xuciyar daya same ta,saboda zama da kishiya.ranar da ummina zata rasu ta kasance tana yi min nasiha kamar haka,"fadimatul-insiya dan Allah na roke ki da ki yafe min kuma kiyi hakuri da gidan ku domin gidan ba'a zama na adalci.

kuma ki guji duniya kamar,abinda kika gani a duniya idan dai ba hanyar tsira bace to shirme ce.
kiyi hakuri dan kina cikin tashin hankali insiya ba kuka za kiyi ba, addu'a xa kiyi, dan kin san iyayena yau kimanin shekara hudu kenan ba sa kasar kuma har yanzu ba mu ji labarinsu ba, ga shi wannan dan uwan nawa ba shi da zumunchi kuma ga yayanki daga kai shi makaranta allo an neme shi an rasa sai ji nayi wani irin kuka mai azabar radadi daga idona.



Muhd-Abba~Gana



www.abbagana.pun.bz
Share:

Sunday 16 August 2015

Saturday 15 August 2015

sireenah***********13

samp906c78071de1d454.jpg

sireenah 2*13
(karshen littafi na 2)







*********NA**********



muhd-Abba~Gana

www.abbagana.pun.bz




Sweet sis kiyi hakuri bamu samu haduwa during
birthday party na wallahi budurwata ce tadauke
mani hankali , oh su yaya suhail ashe akwai
lokacinda za'a wayi gari dazaka so wata macce
harta dauke maka hankali? nadauka baruwanka
da macce balle zancen so yashiga tsakaninku,
Sister kenan you sound funny wanake da bazan
so macce? kawai dai komai da lokacinsa abaya
bansamu wacce tayi mani bane shiyasa bana
zancen soyayya but for now my safna is okay for
me duk wani qualities danake bukata da maccce
tana dashi.. Hmm yaya suhail kenan I can see
you are deeply in love with this Safna kadaiyi a
hankali, toh naji sweet sis thanks. Daman nayi
niyyar sanar dakai wani abu amma da alamu
yanzu baka bukatar abin. My Sister just go ahead
kisanar dani duk abinda zai fito daga gareki
nasan is special so zan bukata don haka stop
thinking of that(kibar tunanin haka)..by muhd Abba Gana Hmm nina
san baka bukata duk da haka zan sanar dakai
don abin yadade inayi maka sha'awar wani abu
but it seems is too late(kamar namakaro) burrina
bazai cika ba, hmm sister kenan pleased kiga
yamani mana nayi maki alkawalin taimaka miki
wurin cikar burinki kisan you mean alot to me..
Wata best friend ditace nayi maka sha'awar ka
aureta duk wani abu da ake bukata ga macce
tana dashi batada wani makusa zaku dace da ita,
tare mukazo during your birthday saboda kai
nagayyaceta don nasan tabbas idan kaganta
bazaka san lokaacin da zaka fada sonta, kada
kayi tunanin tarasa masoyane tanadasu bata
kulasu mutum dayane take kulawa, kuma da
dukkan alamu tanasonsa sai dai ni baiyi mani ba
duk da ban taba ganinsa ba koda a photone
kawai inadai jin labarinsa daga bakinta kada kayi
tunanin ta taba ganinsa don ita kanta bestfriend
dita basu taba haduwa da gayen ko sunansa na
gaskia bata sani ba kawai dai haduwar 2go
username dinsa kadai tasani, cikin sauri suhail
yayi magana gaya mani username din saurayin?
mamaki yacika muneerah batasan lokacin da
tajefo masa tambaya "yaya suhail mezakayi da
username din? Kedai sanardani.. Kash namanta
da username din saurayin, alright tau kinada
picture din best friend dinki? Eh yaya suhail inada
more especially wanda mukayi on your birthday,
ok mugansa! Cike da mamakin tambayoyin yayan
suhail muneera tadauko wayarta irin wanda
tabawa Sireenah tabude daidai foldern data aje
pic dinsu cike da kaguwa suhail ya amshi wayar
don yatabbatar da zarginsa... First picturen
dayafara gani safnarsa ce makale da muneerah
sunayiwa juna murmushi baisan lokacin da
yadaga muneerah sama kamar wata yartsana
(teddy) tare da kuuwa don farin ciki. Sister
safnata ce daman kinsanta ne? Yaya suhail
saukeni tukun, bayan yasauketa ne muneerah
tace" yaya suhail watakila kamace kagani don
wannan Sireenah ake kiranta dashi not Safna.
Wallahi sister itace da tufafinnan dake jikinta
muka hadu on my birthday. Yaya Suhail daman
kaine saurayinta na 2go? But how come tace
saurayinta na 2go talakane baiyi zurfi a karatu?
Tabbas batayi maki karya ba don haka na nuna
mata, take yabawa muneerah labarin soyayyarsu
da sireenah da last haduwarsu plus wahalar
nemanta dayayi. Muneerah ta tausaya masa
sosai kafin itama tasoma bashi labarin wacece
Sireenah sannan tagaya masa watakila saboda
yan biyun gidansu yasa taboye masa kanta gudun
kada rauywarta yashiga garari. Suhail
yatausayawa Sireenah sosai kuma yaji son da
yake mata yakaru fiyeda wanda yake mata a
baya. Yaya suhail tare zamu koma Nigeria don
ganin yadda mommy tee zata shiga tashin hankali
with bakin ciki.. Ashe kinsan safnata kuma tana
kusa dani bansani ba, Yaya suhail Sireenah fa not
safna, mantawa nake sister , kinsan itace
sanadiyar fadana da azeema? kullum Azeema
saita ci mata mu2unci muddin suka hadu karshe
azeema marinta tayi, koda yake narama mata
marin, danasan itace funny girl lokacin da azeema
tayabawa aya zakinta, hahaha yayaa suhail dan
soyayya kasan Allah naji dadi sosai dakaine
saurayinta daman ni burrina kenan cikin ruwan
sanyi Allah ya amshi addu'ata fatana yanzu Allah
yanuna mani aurenku. Ameen sweet you are
always special to mE....tab! shin zasu hadu kuwa?? auren zaiyu?^^^ALHAMDULLILAH---karshen littafi na biyu ,ni naku muhammad Abba Gana keh muku fatan alhairi sai mun hadu a littafi na gaba dan neman KARASHI,GERA,TAMBAYA,GWAJIN TAKA DA DAI SAURAN SU GA LAMBATA KAMAR HAKA [09039016969]






muhd-Abba~Gana

www.abbagana.pun.bz
Share:

sireenah*********12

samp906c78071de1d454.jpg



sireenah 2*12



*********NA***********




muhd-Abba~Gana


www.abbagana.pun.bz



Gaskia
amarya tajigata sosai saboda tsakanin Abuja da
Kebbi akwai nisa gashi bata saba tafia mai nisa a
mota su uku kawaine yan rakiyar friend din
amarya da uwanyenta biyu Alhaji bayason aje
dayawa yadda zasu samu makudan kudi don
yasamu"share "mai tsoka don yasan mahaifiyar
amarya bazata damu da wani "share". Wurin
dayan dare suka isa garin kebbi amarya da yan
uwanta kadai aka saukar agidan sauran kuma
gidajensu aka mayardasu daki daya amarya ta
kwana da kawarta while uwayenta suka kwana
daya daga cikin sauran dakunan. Ango bai kwana
gidan ba washagari dasafe yazo da friends dinsa
biyu don gaisawa da yan uwan amarya daganan
amayar dasu. Sashen da amarya take suka nufa,
amarya anci uban kwalliya kamar ba gobe gaskia
tayi kyau na mussaman don tasha gyara friend
din amarya ba'a barta abaya wurin kwalliya itama
koda yake tayi nata kwalliya ne ko zata samu mai
sonta cikin abokan angon balaifi tasamu shiga
wajen wani abokin ango (masu karatu kada ku
manta friends dinsa na canada harwayau basu zo
ba,) karshe dai sunyi barkwanci kamar yadda
yake kasancewa tsakanin abokan ango da
amarya. Hannu sake aka mayarda yan uwan
amarya batareda an basu koda sabulun wankane
friend din azeema kadai tasamu kyauta daga
amarya....... Tsayawa bayanin kayan da akasa
agidan barnan lokacine abinda kadai zan iya cewa
naira yayi kuka.. Daga azeema sai angonta aka
bari a mamakeken gidan duk girman gidan ba yan
aiki maigadi kadaine, kunga zasu sha amarci
yadda suke so batare da an takurasu!

muhd-Abba~Gana


www.abbagana.pun.bz
Share:

sireenah 2*11

samp906c78071de1d454.jpg


Sireenah 2*11






*********NA**********

muhd-Abba~Gana


www.abbagana.pun.bz



An daura auren azeema da shureim wanda
mutane da dama sun halarci taron harda mai
matarba ya halarci taron daddyn Azeema kasa
hada ido dashi yayi har zuwa lokacin da taron
daurin auren yawatse... Biki yayi biki ango da
amarya anyi almubazaranci mahaifin amarya
yamafi kowa almubazaranci don yana tunanin
zaici riba, events kala 10 akayi, ango bai bayarda
kudin events din wasu abubuwa saboda yace
musu friends dinsa na canada su zasu bayar idan
sunzo, manyan baki sunzo daga kebbi, na canada
basu samu damar halartar daurin auren don
ansamu labarin jirginsu na sarauta yasamu
matsala kuma basu hawa jirgin haya(hmm) so
abokan ango bazasu zo suma don daman jirgin
ne zasu biyo. Amma sunyi alkawalin zasu zo
bayan biki daidai angyara jirgin, mahaifin amarya
shi bayarda kudinsa wurin million 3 wanda akayi
sauran event yace bayan biki abokan ango zasu
biyashi kudinsa with interest(harda kari). Daidai
gwargwado hajia Zulfa'u tayiwa yarta nasiha
amma abanza tayi domin kunnen yarta bone
(kashi) ne. Shima Alhaji mai idanun cin naira
ba'a barshi abaya wurin yiwa "yar sa nasiha
wanda bakomai yakunsa banda ta tabbatar tafara
business yada zata kama aiko masa kudin mai
tsoka don maida abinda yakasa wurin yimata
aure.. Toh daddy , kada kidamu za,a cigaba da
dauka maki lectures, exam kadai zaki zo
rubutawa. Nagode sosai daddy...... "Yan daukar
amarya sunzo daga ganinsu kamar wasu
mayunwata mata biyu kadaine keda kyan gani
atamfa mai tsadace a jikinsu while sauran nayaku
bayi ne suka saka ma'ana na talakawa..Azeema
da mutanenta basu kawo komai aransu don sun
dauka ko bayin sarkine akazo dasu. A haka dai
suka kama hanya but abin mamaki ba hanyar
airport aka nufa Azeema takasa hakurin hakan sai
da takira angon don jin ko lafia taga an wuce
hanyar airport an nufi hanyar byepass , kiyi hakuri
sweetheart bansamu nayi booking flight in good
time(cikin lokaci) bane kuma kinsan yana daga
cikin al'adarmu amarya bata kwana awaje
muddin aka daura aure! okay husby badamuwa
zanyi managing with the car since akwai AC
(maleji da motar tunda)cikin car din..



muhd-Abba~Gana



www.abbagana.pun.bz
Share:

Tuesday 11 August 2015

Yadda Ake Hada Sabulu Soulp Asiyar A Samu Riba Mai Yawa

ni.jpg

DASUNAN ALLAH MAI RAHAMA
MAI JINKAI,DA SALATI GA
SHUGABAN HALITTAN ALLAH
ANNABI MUHAMMAD (SAW) DA
IYALANSA DA SAHABBANSA.
DALILIN YIN WANNAN POST DIN
Nayi wannan post dinne don
taimakon matasanmu maza da mata
game da abinda yashafi
SANA'A.Nayi tattaki zuwa wajen da
akeyin wannan aiki badan komaiba
sai don taimakawa al'ummata.
Da farko dolene ka tanaji
wadannan abubuwa....
1.Gishirin Soda
2.Alayyadi
3.Ruwa
4.Kumfa
5.Kala
6.Stati
7.Turare.
Bayan katanaji wadannan
abubuwan, kawai ka auna ruwa
kofi hudu,sai ka auna gishirin
sodannan kofi daya ka zuba
aciki,sai kabarshi ya kwana daya
idan kahadashi kamar da karfe
goma 10:00am to sai karfe 10:00Na
safiyar gobe yayi sannan ka cigaba
da hadashi
Idan ka dauko wannan ruwan daka
hadashi da gishirin soda saika auna
cikin kofi daya,sai ka auna alayyadi
cikin kofi hudu sai kasa sanda ko
muciya karinka juyawa idan kafara
juyawa ya dame to sai kuma kazuba
kumfa sai kaci gaba da juyawa sai
ka zuba kala da turare da statinnan
saika cigaba da juyawa sai ka dauko
container ka zuba idan yasha iska
zakasha mamaki da yardan Allah.
Idan kajika gishirin sodan nan
karkasa hannu dan zai konaka,Idan
kuma Allah ya aikoma ka kone
bakasaniba,kanajin zafi kawai sai
kashafa man Alayyadi a wajen da
ya kone to bazai tashiba da yardan
Allah,Idan kuma akai sakaci aka
sha to za'a fa mutu Allah yakare,mu
kuma sai mu kiyaye mu kaudashi a
inda yara bazasu ta6aba.
DA FATAN ALLAH YASA MUDACE
KUMA MU AMFANA DA ABINDA
MUKA KOYA.
Daga masana'antar muhd abba gana
Share:

YADDA ZAKAI AMFANI DA (FIYA) WAJEN GYARAN JIKI

bana2.jpg



YADDA ZAKIYI AMFANI DA FIYA WAJEN GYARAN
JIKI Amfani fiya ga jiki:
- Ana amfani da fiya ga busasshiyar fata don
kawo danshin fata. Tana dauke da sinadarai
masu yawa wadanda suka hada da bitamin K da
C da Copper da Iron da sauransu.
- Fiya tana dauke da sanadarin bitamin A da
kuma Glutamine wadanda suke taimakawa wajen
kawar da matattun kwayoyin halittar cikin fata.
- Laushin fata: fata takan tsotse man da yake
cikin fiya, wanda hakan yakan sanya man ya
ratsa kofofin fata, inda fata kuma takan tatse
sinadaran da suke dauke a cikin fiya, wannan sai
ya sanya fata ta yi laushi da kuma dadin gani
- Mayar da tsohuwa yarinya: Fiya tana dauke da
sinadaran da suke kone kwayoyin cututtukan da
suke kodar da fata, wanrda hakan sai ya sanya
fata ta rika sheki da kuma laushi, har a rika taken
ta mayar da ke yarinya.
- Hasken rana yana dauke da sinadaran da suke
kodar da fata ko kuma su sanya saurin tsufa,
amma sakamakon sinadarin da fiya take dauke
da shi, sai ya zamanto ta kare fata daga haske
rana.
Idan kika hada fiya da kuma man zaitun zaif
sanya fatarki laushi da damshi da kuma
sheki.Fiya da man zaitun na amfani ga
busasshiyar fata, musamman ma wajen karefata
daga bushewa ko zazzagewa.
Kayan hadi:
>Fiya
>Man zaitun
>Kukumba
Yadda aka hadawa:
* Ki samu fiya babba daya, sai ki cire bayon fiyar,
daga nan sai ki daka ta, bayan nan sai kizuba
man zaitun, sannan ki gauraya sosai,daga nan
sai ki shafa a fuskarki.
* Ki samu kukumba, sai ki daka ta, daga nan ki
shafa a fuskarki. Za ki bari har tsawon minti10.
Daga nan sai ki wanke fuskarki da ruwa mai
dumi, sannan ki yi amfani da tawulmai tsafta
wajen goge fuskarki. 2 Fiya da ayaba namatukar
taimakawa wajen gyara fatar jiki, sukan sanya
fata ta yi sheki da kuma laushi. Kayan hadi:
>Ayaba
>Fiya
>Yogot
>Man zaitun
Yadda za a hada:
1 Daga farko ki samu ayaba, sai ki bare, ki yasar
da bawon, daga nan sai ki samu fiya, ki bare ta,
sai ki zubar da bawon. Bayan nan sai ki hada
ayaba da fiya da kuma kwallon fiyar, sannan ki
daka.
2 Bayan kin gama dakawa, sai ki zuba yogot da
kuma man zaitun. Za ki ci gaba da cakudawa har
sai kin tabbata komai ya gaurayu.
3 Daga nan sai ki shafa a fuskarki ko jikinki har
na tsawon minti 15.
4 Bayan nan, sai ki wanke fuskarki ko sauran
jikinki da ruwa mai dumi.
Share:

SIRRIN KABEWA GA GYARAN JIKIN DAN ADAM

bana.jpg



Za mu dan tabo wasu daga cikin sirrukan
Kabewa. Ita dai Kabewa sinadari ce mai matukaar
muhimmanci da amfani a jikin bil Adama,
musamman ta fuskar Ibadar Aure. Masana a
wannan fagen a Duniya, sun tabbatar da a na da
nau’oi’n Kabewa guda goma sha takwas (18)
sannan A Afrika muna da guda takwas (8), bugu
da kari a nan Nijeriya muna da na’o’inta guda
hudu (4) kacal.
Kuma tana daga darajar miji a wajen matarsa
kuma abinci ce wanda idan ake sarrafata take
wanzar da abubuwa masu dumbin yawa na gyara
da inganci.
A nan ina so na yi amfani da wannan damar a
wannan jaridar tamu mai tarin farin jini in
bayyana amfanin Kabewan a takaice.
Abubuwan da za a tanada sun hada da abubuwa
hudu zan fitar da wasu sinadarai karfafa masu
kwarara da tsare mutuncin lafiya sannan su daga
kwarjininki da martabanki a wurin mijin ki. Ki
zauna abar ambato da yabo a wajen mijin ki,
kuma in kina da kishiyoyi, wato ba cuta ba
cutarwa, wanda ke ce da kan ki za ki sarrafa
babu batun ki je a ci kudinki a banza, babu gaira
ba dalili ba.
1. A markada Kabewa da Guaba da Ayaba, a tace
a dinga shan ruwan jifa-jifa, yana maganin gajiya
da saurin kosawa, sannan yana taimakawa
matuka yayin bukata ko sha’awa.
2. A cire hanzar nan ta Kabewa a zuba a ruwan
zafi, babban kofi daya a rufe, bayan hanzar ta jiku
sosai, sai a tace a zuba zuma cikin cokalin cin
abinci uku a kada har sai ya hadu shi ma a
shanye. Shi ma yana taimakawa matuka wajen
ni’ima da karin kuzari.
Hadin ‘Ya’yan Zogale
1. Ki samu farar shinkafarki, sai ki dan soyata
sama-sama, ma’ana kada ta soyu kwarai za ki
tafasa ruwa sai ki zuba gyada, ki yi sauri ki tace
ta, sai ki shanya idan kin yi daidai za ki ga
bawon gyadar yana cirewa da kansa kafin ta
bushe idan ta bushe sai ki murmushe ta ki
dakata in kin ki daka chukwi da dabino ki cire
‘ya’yan Zogale, ki cire fatar ki shanya a cikin
inuwa idan sun bushe ki hade su da dakakkiyar
soyayiyar shinkafarki da gyada da dabino, sai ki
rinka sha da madara ta ruwa, yana saukar da
ni’ima sosai.
Share:

TSIREN DANKALI

sampea6c1ceaeadfded9.jpg

TSIREN DANKALI
ABIN BUKATA
Dankali isashe
Albasa
Ganyen corriander
Koren barkono 3
Ruwan lemo
Gishiri /dandano
Garin hodar cummin
Garin busashen biredi ko garin shinkafa
Bota
Kwai 1
YADDA ZA AYI
A dafa dankali a bare a murje sai a kawo bota a
zuba a kai da sauran kayan hadin
Banda kwan sai hade a kwabe su gaba daya ayi
masa fasalin zobe ko rawul sai ajiye a fridge
Ya tsumu .
Bayan ya tsumu sai asa a cikin ruwan kwan
sannan abarbada busashen biredi akai sai a
soya.
Za a iya anfani da wannan abinci don karin
kumallo ko yara su tafi dashi makaranta
Share:

sireenah*********2**9

samp906c78071de1d454.jpg

Sireenah 2*9



********NA**********


muhd-Abba~Gana



www.abbagana.pun.bz


Suhail yasauka family house dinsu dake london
wanda nan ne muneerah take zama babban
gidane sosai. Koda Ya'isa garin bai tararda
muneerah a gida, don haka batasan da zuwansa.
Bayan yayi wankansa yaci abinci koda yaduba
agogo yaga dasauran lokaci before the meeting
yakwanta bacci cikin barcin yayi mafarkin sunyi
aure da sahibarsa with four kids suna shaqatawa.
Alarm dinda yayi setting shine yakatse masa da
daddan baccinsa. Baiso tashi ba but bayada
option dolensa yatashi saboda muhimmancin
meeting din so yasoma shiri cikin gaggawa, gama
shirinsa yayi daidai da isowar motar muneerah a
harabar gidan. Shigar suit yayi komai nasa farine
harda briefcase dinsa lifter yayi using wurin
saukowa while muneerah da steps tayi amfani so
basu samu damar haduwa. Madam you are highly
welcome, your brother just left, yar aikin gidansu
ce mai suna Linda take sanarwa muneerah fitar
yayanta, Linda which of my brother? Mr
handsome sunanda yan aikin gidan ke Kiran
suhail dashi. Okay koda ta'isa dakinta tagansa
tacikin securities camera so tayi farin ciki sosai
don haka tashiga hada masa favourite food dinsa
da juice tabata lokaci sosai wurin hada masa
girki Linda ce ta shirya abincin saman dinning
dake babban falo, muneerah taje tayi wanka
simple make-up tasa doguwar riga marar nauyi
kalar sky blue tana jiran yayanta, daman tanadaf
burri akansa sai gashi yazo mata cikin sauki don
haka baza tayi sakaci wurin gaya masa kada
lokaci yakure mata. Masu karatu menene wannan
burrin na muneerah?...........
**************
Salau har ka'iso? Eh hajia ina kwana, lafia lau
salau. Ke sireenah kina ina ga mijinki nan yazo
daukarki, ganinan Mommy tee, sireenah bata zata
an bada ita sadaqa dagaske sai da taga salau
yazo daukar ta gashi bata shirya komai koda take
bawani tufafin arziki ke gareta don haka school
bag dinta kadai tadauka, salau haushi yacika shi
daya ganta hannu sake yazata tunda sunce auren
sadaqa za'a hadota kayan gara, lefe etc but sai
yaga wayam, watakila kudine cikin jakarta haka
Malam salau yake tunanin haka. Shi yahana
yanuna bacin ransa a fili. Drivern mommy tee ne
yatuka su zuwa kasan layin ta wurin da shagon
salau yake Ado nasauke su yawuce abinshi. Ke
shiga ciki nan ne gidanah amma muga jikkarki
meye aciki bamusu ta mika masa yana budewa
yatarar da littafai nan yayi watsi dasu yana fadan
littafai zasu cine da ba'a kawo ta da komai ba,?
Bata kulasa ba ta shiga domin takarewa inda
zata zama kallo bata ankara ba taji an rufe
shagon da karfi hankalinta yatashi sosai don tayi
kokarin fitowa takasa sanadiyar shagon an rufesa
da makulli kuma aikin salau ne tana cikin haka
tatsinkayo muryar salau koda tasaurara taji yana
waya kamar haka:- Alhaji gatanan nazo da'ita
yanzu haka tana cikin shagon da aka dauki haya
na rufeta. Kada kadamu salau su iro suna cikin
unguwar yanzu haka kadan yarage su'iso daidai
wurin. Toh Alhaji yasauran balance dina? Tareda
balance din suke. Nagode sosai Alhaji. Sireenah
ta tsoratah dajin haka hawaye yasoma fita daga
idanuwanta amma bakinta bai goshe da addua
tasan Allah kadaine zai kubutar da ita daga
sharrin salau. Tafita hannu azzaluma tafada
hannun masu sayarda mutane, yaa ubangiji
kafidda ni daga wannan bala'i tayi kokarin
guduwa ba hanya. Ba'afi minti biyar dagama
wayar sai ga su ir0, babu alamun sassauci tare
dasu fuskarnan tasu a murtuke kamar basu taba
dariya, Salau tana INA? cikin shagon take, toh ga
sauran balance dinka katabbatar ka tattara
kayanka zuwa kauyenku. Ai daman kayana a
shirye suke, yauwa salau suna bude kofar
sireenah tayi yunkurin guduwa suka wasa mata
powder a fuskarta take tasome, suka dauketa sai
cikin mota dasaurinsu suka bar unguwar. Nan
salau yarufe shagon yasani inda dare yayi masa
yana mai mamakin me ALHAJI zaiyi da wannan
mumuna yasan muddin kudi za'ayi da ita tabbas
kudin zasu yi muni. Oh su salau kenan ko
inaruwansa bayan yasayarda yar mutane.. Wane
Alhajine aka sayarwa sireenah? Mezaiyi da ita?
Sai mun hadu ana gaba........

muhd-Abba~Gana


www.abbagana.pun.bz
Share:

sireenah********2**8

samp906c78071de1d454.jpg

Sireenah2*8


********NA***********


muhd-Abba~Gana



www.abbagana.pun.bz


Ya tafi dake bayan sati daya zanzo nadauke ku
daidai kungama cin amarci. Murmushin takaici
sireenah tayi kafin tace mommy tee nagode sosai
Allah yatabbatar da alkhairi. A zuciaryata kuma
tana mai rokon Allah daga sharrin su domin bata
taba ganin Inda akayi aure ba sadaqi ba waliyi
sai nata.. Karshe su biyu aka bari falon lokacin
sireenah tasamu damar magana. Malama
sireenah kenan duk gudunki dai yau nazamo miji
agareki sai yadda nayi dake gobe warhaka kina
gidana nayi farin cikin hakan sosai ga dukkan
alamu ko hajia ma tagaji dake shiyasa tabani ke
sadaqa Allah yasaka wa HAJIA da alkhairi ki
zauna cikin shiri gobe zan zo mutafi. Salau kaji
tsoron Allah kataba ganin inda akayi aure babu
magabata da sadaqi? Yoo ni ina ruwana wannan
keta shafa daman aini ko kwandala bazan iya
bayarwa a wannan fuskar taki mai kamada
kashin kare( wai kwando kecewa rariya na yoyo).
Sireenah kasa furta masa komai tayi tadai bude
idanuwa da kunne tana sauraron cin mutunchin
da salau keyi mata Wanda bakowa yaja mata
face mommy tee bataga maizata yi dashi koda a
kafa aka daura mata kwanceshi zatayi tagudu
batagama zancen zucci taji yace ga naira 100
nan ayi gyaran amarya kila zakiyi daman kallo
Idan nazo. Tirkashi jama'a kuna ganin wannan
auren yadauro? Malam salau yasamu sireenah a
banza kenan? Ya suhail zaiyi idan yadawo daga
London? Kubiyoni a sannu don jin amsar
tamboyiyinku daga naku har kullun muhd Abba Gana
masu satar Mani littafi suna sa sunansu a ciki
suyi tayi bazan ce su daina ba but kada su
manta karya bata fure sannan akwai daren gobe
kiyama.......

muhd-Abba~Gana

www.abbagana.pun.bz
Share:

Monday 10 August 2015

sireenah*******5,6,7

samp906c78071de1d454.jpg

Sireenah2*5




*********NA**********


muhd-Abba~Gana

www.abbagana.pun.bz




Motarsu suhail ya lalace saman hanya, daidai
gwargwado sun iya bakin kokarinsu motar yatashi
amma motar kamar batasan sunayi ba gashi basu
san meye matsalarba a karshe dai they decided
to call mai gyara(mechanic) cikin kankanin lokaci
mechanic din yagyara motar.
**********
Haba manager kashanyamu haka kamar kayan
wanki? munyi takira anace mana number busy.
Hajiya sorry kinsan yanayin garin namu sai a
hankali hold up yatsaidani, kutashi yanxu muje
office, Sai da suka zauna manager harda dauko
masu drink a fridge bayan sun shane yasoma
bayani kamar haka: ina sireena Sadam Saraki
take, gani nice.. ,lokacin yakai dubansa ga
sireenah tabbas itace pretty tacikin passport
saidai ta dan kara girma sannan tafi kyau a fili,
wow hajiya itama wannan yarki ce? eh manager
yatace. Gaskia tafi sauran kyau ko zaki bani ita?
wani kololon bakin ciki yatasowa mommy tee
batasan sanda tace anrigaka don tana da mijinta
aurenta cikin satin nan za ayi auren. Sireenah
idanuwa tabude saboda mamakin wannan karya
da mommy tee tashirga duk da manager baiyi
mata ba amma taji haushin hakan. No wonder
hajia naga tasa hijabi dogo da alamu mijinta zaiyi
kishi, koda yake banga laifinsa macce irin wannan
dole ayi kishinta, Allah yatabbatar da alkhairi.
Okay manager back to our business, Alright hajia,
bayan fitarku jiya nakara bincike sosai gameda
account din. A binciken danayi nasamu wata
takarda wanda Alhaji ya aiko da wata takarda
wanda yayi bayani kamar haka:- "Ni Alhaji
saddam Saraki dukkan tarin dukiyar dake account
dina mallakin 'yatace sireenah bayan rasuwata ita
kadai zata tayi operating account din ko matata
hajia fati ban amince tayi amfani dashi ba!
Akarshe bazata fara amfani da account din sai
lokacin da mallakin hankali kanta which is after
tayi aure!
Wani gumi yatasowa mommy tee, manager ban
fahimta kana nufin ni hajia fati banida right ga
account din mijina? tabbas haka yake hajia,
kenan sireenah sai bayan aurenta zata fara
amfani dashi? kwarai hajia haka mahaifinta
yace... Sireenah tayi farin cikin hakan sosai
tagodewa Allah daya sama mata mafita atleast
basu samu biyan bukatarsu, suka tashi jiki
sanyaye, motarsu yana gab da barin harabar
banki sai ga nasu suhail yashigo kamar ance
masa yadaga idanuwansa yayi tozali dana
safnarsa yazata ko gizo take yimasa but daya
rufe idanuwansa yabude yaga tabbas itace bashiri
yace Nazir ga funny girl can cikin mota don Allah
yi parking naje nasamesu kafin su wuce. Suhail
for God sake calm down mana bawai muje
musameta ba why not mubisu a baya muga gidan
da zasu shiga kaga yafi. Is better musan
gidansu.. Okay toh muje nazir kada su kubuce
mana, sun yanke shawarar binsu abaya, sireenah
bata gansu ba dayake motarsu suhail tinted ce.
Suna biye dasu har suka isa unguwar sa'ar su
daya ba hold up. Saida suka tabbatar nan ne
gidansu safnar saboda tambayar dasukayi kafin
suka bar unguwar zuwa inda aka aikesu, zasu
dawo zuwa anjima daddare he want to suprised
her............by muhd Abba Gana



www.abbagana.pun.bz



Sireenah 2*6




********NA***********


muhd-Abba~Gana



Azeema naga wautarki kina abu kamar bajina ba
irin wannan bai kamata kitsaya jamasa ajiba, ke
kanki kinsan bazan hana 'yata abinda takeso ba
daman ni can bawani son aurenki nake da suhail
don dai naga baki samu wanda yafishine amma
yanzu tunda kinsamu dole ayi da wannan, aini
abin farin ciki nane 'yata tazama sarauniyar wani
country bama gida nigeria, dagani akwaishi da
sakin hannu, kinga irin kyautar dayayi a tashin
farko. Daddy daman abinda yasa nace sai nayi
tunani shine baikon suhail dake kaina kada nazo
dashi kace bakasan da zancen, Suhail din banza
da wofi mena taba ci nasa dazanyi amansa, daga
yau na soke baikon dake tsakaninki dashi. Idan
kinada numbersa(shureim) kirashi kice masa kin
amince kinsanfa hausawa sunce abari yahuce
shike kawo rabon wani. Daddy banida numbersa
yace dai zai kirani dakansa. Toh shikenan kada
kibari ya kubuce maki. Zulfa'u kina ina ne wai?
gani tafe daddyn azeema, kinji abin farinki daya
samu yarki ko? wane abin farin ciki kake magana
daddyn azeema? badai yaudarar da kuke shirin yi
bane abin farin ciki? inajin duk zancen dakuke
banason saka kaina ne don ba'asa dani ba, wato
ku butulu kunje wurin mai martaba da kokon
bararku ya amince da auren suhail dana azeema
wato yanzu don kunga wanda yafi suhail din
shine zaku ci amanarsu? Dakata ke! cikin tsawa
yayi maganar, ni na kiraki shiyasa kike son ci
mani mutunci. Daddyn azeema kayi hakuri amma
wannan ba zancen cin mutunci bane gaskiace! Ki
rike gaskiarki bama so, nakula zulfa'u kema kina
cikin mahassada, wato kina bakin cikin hanyar
karuwana toh kisani daki amince da karki amince
sai azeema ta auri shureim. Yi hakuri daddyn
azeema bahaka bane Allah yahuci zuciarka yasa
kagane gaskia yakuma bada sa'a. Yanzu naji
abinda nake son ji ko kefa ai addua kadai
yakamata kiyi, idan baikon suhail yasa kike tada
jiyoyin wuya haka anfasa nasan yadda zanyi da
mai martaba yanada saukin kai. Nidai yar kalloce
baruwana daddyn azeema..
*******************
Lale maraba da Nazir ashe tare kuke da
mutuminka, saukar yaushe? hajia barka da
hutawa jiya nadawo. Madalla natayaka murna
suhail yace mani kungama karatu yanzu sai aure
ko sai ka tsaya ruwan ido irin na abokinka? Eh
hajia mungama, ai aure lokacine kidai tayamu da
addua samun macce tagari matan yanzu sai
ahankali, shima suhail ba ruwan ido yatsaya ba
lokacinsa ne baiyi ba amma ai nasamu labarin an
kusa aurensa shima da azeema. Eh hakane wurin
ruwan idonsa aka hadasu Allah dai yatabbatar da
alkhairi.. Ameen hajia, Yauwa nazir meka bawa
abokinka nagansa yau sai wani farin ciki yakeyi?
Hajia komai ban bashi ba watakila Allah yaakusa
amsar adduarsa ne. Toh Allah yasa. Ameen
hajiyarmu. Zan tafi suhail zanzo rikaya zuwa
gidansu safnar around evening time. Ina gaida
mami please... Bayan suhail yadawo wurin
rikayar nazir, take yawuce sashensa wurin zaba
tufafin dazai saka don burge sahibarsa zuwa
anjima but unfounately mai martaba dakansa yaje
sashen suhail. Alhaji barka da warhaka. Yauwa
suhail kashirya yanzu zuwa london akwai meeting
dinda za ayi cikin gaggawa na companing mu
wanda kai nakeso ka wakilceni flight dinku zai
tashi in the next 20mnt. Toh alhaji suhail bai
tsaya bata lokaci ba yasihrya cikin kankanin
lokaci mai martaba yana cikin mutanenda zasu yi
masa rakiya zuwa airport... A ranar suhail yabar
nigeria gashi baisamu damar zuwa gidansu
safnarsa. Ko nazir bai tarar dashi koda yadawo
daddare kamar yadda suka shirya
****************
Malama....malama... salamun Alaikum bayan
sallamar data amsa bata kara furta masa komai
sauri take ta isa gida shikuma mutumin yakafe
yaki tafia sai famar biyarta yake, gudu-gudu hadi
sauri kamar zata fadi kasa tasamu tashige cikin
gida, shigarta cikin gidan yayi daidai da isowarsu
yan biyu, cikin zafi nama Hussaina tafito daga
motar tana mai tambayarsa bawan Allah lafia?
metayi maka daka biyo wadda tashiga cikin gida
yanzu? Eh toh hajia lafiar takawo haka yarinyar
data shiga gidan yanzu nagani nake so kuma ni
da aure nake sonta amma taki saurarena..
Yasunanka? Sunana Salau hajia ina tsayar da
shayi a karshen layinnan. Okay malam salau
kadawo zuwa anjima zata saurareka kada kaji
komai. Salau yashiga washe korayen hakoransa
yana mai godia, ga wani uban silifas dake
kafafuwansa wanda yasha liki da leda,silifas din
yasade da kodaddar rigarsa ga dukkan alamu
fama yake dakansa bakine sosai bayada jiki
amma akwai tsawon wuya kamar marakin lema
inshort salau baya da kyan yau balle nagobe.
Yatafi da maganar zai dawo anjima, Hussaina
meye haka kin wani shanyani cikin mota nazata
gate zaki bude amma kin wani tsaya kina zance
daa wancan banzan almajiri.. Dadina dake
hassana saurin fushi ai kya saurari uzurina tukun,
baki kula lokacin da sireenah tashiga ciki bane?
taya zan kula bayan my attention yanaga driving.
Ok wannan dakike gani wurinta yazo nan ta
sanarda hassana yadda sukayi da sallau. Kai
hussaina gaskia naji dadin wannan lamari shine
don bakin ciki irin nata taki saurarensa bayan
tasan munyi kwanaki muna nema mata wanda
zai aureta bamu samu ba saboda bakin jini irin
nata, don bakin ciki shine zata koresa wallahi tayi
kadan.. muje ciki mommy tee tasan me ake
ciki.......toh fah!!!




muhd~Abba~Gana


www.abbagana.pun.bz
Share:

sireenah*****2 ,4

samp906c78071de1d454.jpg

Sireenah 2. 4



********NA**********


muhd-Abba~Gana


Nazir kaine yau agari kodai mafarki nakeyi!
kaganka kuwa yadda kacanza tamkar ba karatu
kajeyi' spain dinnan ya karbeka fatar kazo mana
da mai jar kunne? hahaa suahail baka rabo da
tsokana masu jan kunne ma nazo dasu,daman i
wanted to suprised shiyasa naki sanar dakai zan
dawo bayan gama wayarmu a daren jiya flight
dinmu yatashi, you really suprised me kayi mani
wayo gashi kagama karatun ka kodayake, karatun
kasashen waje yafi nagida nigeria sauki. Hakane
suhail sun bani offer a wani asibitin can nace
musu a'a kasata zanyiwa aiki yadda zasu karu
dani. hakan yayi kyau nazir ashe nigeria zata
samu babban likitar kwakwalwa. suhail mubar
wannan zancen whats wrong with you naga duk
karame idanuwanka sun firfito waje kamar wanda
yayi shekara daya yana jinya? Ina funny girl?
nazata by now koda zan dawo kunyi aure?
anfasa ma suhail ciwon dake damunsa
idanuwansa sun canza kala zuwa ja kamar wanda
zaiyi kuka" Nazir bari kawai duk tunanin funny
girl ne yayi mani yawa nafara zargin aljanacel,
yau kusan wata daya da haduwarmu bankara
sakata a idanuwana ko a 2go chat nadaina
ganinta, the worse part ko picture dinta banida
balle narage makaina wani radadi but balaifina
bane itace kehanani muddin natambayi pic dinta
zata kawo mani excuused, kasan nagaya maka
birthday dina muka hadu banga laifinta data
hanani picture dinta course she is so sweet
tsabar kyan dake gareta bata kama da yan niger,
her skin,pointed nose shape lips etc abin burgewa
ne more especially her romantic voice, nazir naso
kaganta nasan zakace nafi kowa dace. Hmm lallai
abokina kayi nisa baka jin kira' nagaya maka illar
relationship online kaki saurarena, ina tunanin
wannan yarinya dakake ta lissafawa haka ba
mutum bace ko tafiyarta baka gani ba lokacin
haduwarku kace ko tafiayarta baka sani ba koda
kajiyo baka ganta is this not enough for you to
know ita aljanace? mafita daya ne suhail kayita
addua kayawaita kai kukanka gun ubangiji. Haka
hajia tace, lah suahail muje nagayarda hajia kafin
tasan ina nan, a'a nazir muje karani banki first
idan mundawo kaje gayarda hajia mai martaba
tun jiya ya aikeni banje ba rashin jin dadin jikina
yahanani zuwa, a'a mutumina kadaice rashin
ganin funnygirl waini yama sunanta nagaske?
Safna. Nice name, ina labarin azeemarka? mtws
nazir you just spoilled my day na tsani naji an
ambaci sunan. Meyayi zafi suhail? Namanta
bansanar dakai anyi mani engage da ita in
3months times za'ayi aurenmu wai. Wow you are
so lucky suhail shiyasa ka tsaneta? nibanga
matsalar hakan atleast tana da kyanta daidai
gwargwado ga iya make up da kwalisa dadin abin
kasanta tun tasowarta. Mstw nazir Allah zamu
bata idan baka daina yimani zancen azeema
banga abin so a tattare da ita batada qualities
danake bukata ga diya macce! suhail kenan
aljana safna tarufe maka eyes dole kayi
condeming din azeema. Eh naji mutafi. Motar
nazir suka shiga bakine sosai harda glasses din
motar da dukkan alamu sabuwace bansan sunan
motar ba(lols) but motar is one in town! maigadi
yawangale musu gate tuki suke a hankali tamkar
masu tausayin kwalta.
*****
mommy tee barta hakan muje kawai tufafi kala
biyar kenan tana sakawa kina mayar da'ita lokaci
zai kure mana ne. hussai shegiyar ce da abin
haushi duk shigar datayi yana amsarta gashi
tufafin bamasu tsada namu tufafin yafi nata
tsada but tafi kyau,cikin batayi kwalliya a
fuskarta ba kenan idan tayi sai yaya? yan biyu
kunsan meke bani haushi gareta? a,a mommy sai
kin fada. gashi kanta tun ina askeshi har nagaji
nadaina muddin na askeshi zaifito fiyeda wanda
na aske. yauwa cikin tufafin da ku ka kwashe
nata akwai hijabai har kasa a ciki ku zabo daya
kubata, okay mommy tee zafi yahanamu sakawa,
haka akayi hijabin aka bata har kasa amma bai
hana kyanta fitowa ba yau dai babu shoe shiner a
fuskar sireenah ko wannan kadai abin farin ciki ne
gareta. Sun kama hanyar zuwa banki sireenah na
mai rokon Allah mafita, su mommy tee farin cikin
dasuke ciki baya misaltuwa, don sunyi planning
kawai idan sunje banki sireenah tamayar da
komai hannunsu. Sun isa bankin but kash basu
tarar da manager mommy tee kamar ta tsuke don
haushi gani take manager bazai dawo ba sannan
bataji zata iya bari zuwa gobe course tanason
sireenah tabar dunia kafin goben idan burinsu
yacika. So sun shiga zaman jiran manager........!


muhd-Abba~Gana


www.abbagana.pun.bz
Share:

Saturday 8 August 2015

sireenah**********---book2 no 1,2&3

samp906c78071de1d454.jpg

sireenah book 2 *no 1

********NA***********

muhd-Abba~Gana
Zuwan yan biyu banki ne aka basu tabbacin "yar
Alhaji Saddam kadai ke iya fitar dakudi a account
din koshi sai tazo dakanta sunganta anyi mata
snapping din picture saboda amsar kudi masu
yawa a banki dole ne ayi photo incase, sun sha
jinin jikin su dajin hakan, mu mafa ya yan Alhaji
ne manager ko kallon su baiyi ba haka suka fice
daga bankin jiki sanyaye..
Allah ya isa tsakanina da Alhaji nizaiyiwa haka?
Alhaji yasha zagi da tsinuwar mommy tee, yan
biyu dagaske ne anhana ku karbar kudin ? yan
banki nan sun fara hauka ne bayan nasan duk
zamana da alhaji bai taba furta mani sireenah Ce
next of kin dinsa ba hasalima ya akayi yacanza
signature don a iya sanina inada right ga account
dinsa shiyasa duk wani dukia ta account din
mahaifinku nake turawa, yaci mutuncina wato
sireenah kadaice yarsa shiyasa baisa daku ba
koda yake nikuma zanyi amfani da sireenah na
amshe dukiyar, gado na ubanku ne dole na kwato
maku hakkinku! Sireenah tsorona take,tanayin
duk wani abu dana umurceta so dolenta ne ko
wannan karon tayi mani biyayya zamuje da ita
banki ta amshi kudin daganan musan yadda
zamuyi da shegiar! Hassana je kira mani sireenah,
toh mommy tee , munafuka , yar aiki, kina inane
mommy tee nakiranki da hassana taji shirun yayi
yawa bata amsa mata kaisaye tashiga dakin
daman sallama ba dabi'arsuce bude labulen dakin
keda wuya tayi arba da Haddaden waya saman
shaffen katifar sireenah tsabar yadade yakoma
kamar anshifada tabarma, what! mena ke shirin
gani yarinyar nan tafara sata kenan mommy tee
tagama ganin wannan wayar tafice daga dakin
with wayar a hannunta, sireenah dake cikin
bathroom bata san meke faruwa saboda karar
shower dake bude fitowar tane taga ba wayar kan
katifa, hankalinta yatashi,salati tayi tajerawa
innalillahi..... shikenan yau asirina ya tonu,yaa
Allah kayi mani kariya daga sharrin mutanen nan
bata gushe ta wannan addua mommy tee suka
shigo dakin, jikin sireenah yashiga kakkarwa.
Munafuka, dayake kinsan bakida gaskia shine
kika tsorata haka? ubanwa yabaki wayar nan?
mo....mmy tee kyautace daga muneera, rufe mani
baki you big liar, har yaushe muneerah tayi kudin
sayen waya irin wannan? tsadar wayar daidai
kudin wani mota, Ko kin manta muneera
matsiyaci yace bata iya tsinana ma kanta komai
balle wani, kyautar ta na dubu biyune.. Ki gaya
mani kin fara satane? Allah mommy bana sata,
kina biyar maza kenan? Bana kodaya. Koma
kinayi keta shafa abin farin cikine agareni
matsalar dayane tsani ganinki da duk wani abin
ka ruwa don haka yanzu ma rabaki zamuyi da
wannan kafin haka yan biyu ku daketa son ranku.
Saida sukayi mata likis kafin suka barta kwance
kasa dakyar sireenah ta rarrafa zuwa bathroom
don tagyara jikinta daman haila yarisketa shine
taje dubawa a yauce koda Hassana tashigo
dakinta, dayake ta fitar da wayan ne don kiran
mommyn muneera kafin ta mayar dashi
maboyarsa, farin cikinta shine basu gano itace
safna Mrs(pinky) kamar yadda su twinsa ke
kiranta! Bayan dukan dasukayi mata mommy tee
tayi danasanin barin yan biyu dakinta saboda
yanzu ne ta tuna da batun banki! fuskarta ya
kumbura sanadiyar dukan da akayi mata ba halin
zuwa banki dole sai an bari fuskar takoma daidai
don kada a zargesu , sireenah tagodewa Allah
asirinta bai tonu ba, haushinta dayane rashin
kiran mommyn muneeera tsohuwarta wayarta
data duba ba number mommyn muneerah!
***
Maraba da aminina (daddyn axeema) yau kaine a
gidan nawa? Kasan idan mutum yana neman
biyan bukata dole yazo dakansa balle ku
sarakuna komai naku nadaban ne! Oh zancenka
kenan amma aini ko aike makayi mani koma
mene zanyi maka kafin karfin komai a wurina , a
a Mai martaba maganar tawa na mussaman ne
gwara zuwana, toh Alhaji tunda kace haka kai
nake sauraro , daman magana ce ta "ya "yanmu,
azeema tazo mani da zancen tana son auren
suhail ko nace suna son auren junansu dayake
kowa yasan soyayyar tasu dadden abune, Haka
ne Alhaji sai dai ban katse maka hanzari suhail
din da bakinsa yace mani yadau azeema
matsayin yar uwarsa ba zancen soyayya tsakanin
su! Haba Alhaji koda hakanne ba soyayya
tsakaninsu ai yadace muhada "ya "yan mu aure
ko don karin dakon zumunchi, maganarka haka
take amma yaron nawa yazo dazancen yasamu
matar da zai aura! Mai martaba kenan ai koya
samu Wacce zai aura bazai hana akara masa da
yar uwar tasa, yana da right na auren mata hudu,
dahaka har mai martaba ya aminta da bukatar sa
ko banza baya iya jayayya da babban amininsa
sun rabu cikin farin ciki kafin su rabo saida akayi
baikon SUHAiL da AzEEMA ! Zancen yabi gari na
baikon suhail da azeema mutane sai tofa
albarkacin bakinsu suke gogan yashiga tashin
hankali ,yana yiwa mahaifinsa biyayya sosai baya
tsallake zancensa! Mahaifinsa Kuma kaifi dayane
baya canza magana idan ya yanke hukunci,
menene mafita?
Zai aureta? yazaiyi da safnarsa?


www.abbagana.pun.bz



[10:28AM, 8/08/2015] Sireenah2*2

********NA***********

muhd-Abba~Gana

www.abbagana.pun.bz
Gaskia mai martaba banji dadin hukunci daka
yanke batare da ka shawarcemu, nasanar dakai
suhail baya son yarinyar nan yadauketa kawai
matsayin yar uwane, yariga samu Wacce yake
kauna, Hajia dakata nasan ban shawarceku ba
but inada right tafiyar da duk abinda nake so ko?
Hakane mai martaba, toh nariga na yanke
hukunci kuma ba maganar canji don bagirmana
bane, tun yaushe muka bashi dama yana mana
yawo da hankali? Karshe yace yasamu wacce
yake kauna amma har yau ba a kara jinlabarinta ,
nagaji ban hana masa kara aure ba idan yana ra
ayi muradi yayi adalci, kema kamata yayi kiyi
supporting dina bawai kizo mani da wani zance
nadaban, shikenan maigidanah kayi hakuri sanin
kanka ne ban isa na tsallake maganarka ba haka
yaranka ko yanzuma zumu cigaba da yi maka
biyayya muna sane baxaka taba cutar damu!
Yauwa uwar "ya "yana Allah yayi muku albarka
baki daya, shiyasa kullum nake kara sonki saboda
kina bina sauda kafa bana tsoron yanke hukunci
don nasan bazaku taba watsa mani kasa a
idanuwa..haka dai suka canza hirarsu zuwa
na...........
Ba nasara ga suhail banda yayi hakuri
yacigabada addua hakan takasance garesa kullum
cikin neman safnarsa yake, baya zancen azeema!
*********
wow azeema kalli waccan mota kamar ta nan
zatayi parking? Friend ashe kingani tun shigowar
motar nake kallo kamar bama mukadai ne ke
kallon motar ba, all eyez on the car' nima
Abba gana motar nake kallo! Subhannallahi
azeema kinga nacikin motar? dashi da motarsa
bansan wanda yafi haduwa ba, azeema
............axeema anya kina tare dani Kuwa, hmm (mata ikon Allah)
qawata bari kawai nashiga duniar tunani ne ashe
akwai masu kyau haka komai nasa abin burge
wane yasoma fin suhail dakomai! Haha azeema
kodai kin kamu ne? Allah qawata kamar kinsani
but matsalar anyi baikona da suhail mtsw dana
san zan...... azeema yi shiru gashinan tafe wurin
mu, dole tayi shiru bata karasa maganarta ba.
Assalamun Alaikum yan mata cikin siririyar
muryasa yayi sallamar tamkar baya son magana
daman akwaishi da maake voice kamar macce!
Azeema shiru tayi taki amsa sallamar friend kadai
ta amsa , Malama azeema kinyi shiru baki amsa
sallamata , azeema bude idanuwa tayi cikin
mamaki da alamar tambaya ina yasan sunanta,
Nasan zakiyi mamakin ina nasan sunanki amma
ba abin mamaki bane idan kikayi la'akari da
popularity dinki bama sunanki kadai nasani ba
nasan komai dangane dake idan nace komai I
mean everything about you! Bakomai yasa nayi
bincike akanki ba tsabar sonda nakeyi makinr
nahadu dake a wani supermarket da kike
shopping ne, naso nabiki baya zuwa gida amma
emergency kira yazomani nazuwa Thailand harkar
business na dayan company na dake can, ban
dawo ba sai jiya kafin tafiyana nasa ayi mani
bincike kanki wanda harda labarin anyi maki
engaged da suhail nayi bakin ciki sosai but duk
haka nace sai nazo na gwada tawa bajinta ko
banza ba aurenki yayi ba inada tabbacin bazai
kadani ba, yadda yake takamar jinin sarauta ne
haka nake bana tunanin yafini arziki koda yake
kada nacika malama azeema da surutu By the I
am prince Shureim Suraaj by name daga
masauratar Canada, Azeema wadda dadi duk
yasa takasa magana, malama are my not
accepted ko don kinga am not from your country
idan shi kike tsoro munada yan uwa a Nigeria!
Hmm dakyar tasamu tace a a bahaka bane amma
kabari har nayi tunani! Toh zan tafi kafin ya tafi
sai da yabasu 50k each wai su sha ruwa.
Tafiyarsa keda wuya su azeema suka hau shewa
plus daria, Friend Allah yataimake ni ban auri
suhail dana cuci kaina, azeema duk da haka you
are engaged bai kamata kifasa aurensa afterall
har manya sun shiga tsakani, friend matsalata
dake baki iya cin arziki, bani kudin idan baki son
shuriem, Ayi haka azeema kudine fa? nima
inasonsa Allah ya nuna mani aurenku! Haha
shegiya friend mai idanun cin naira! Haka dai
suka rabu cikin farin ciki azeema tama fi kowa
farin ciki don tasan ajinta yakaru and when it's
come to money daddynta baya wasa, yafi suhail
da komai arziki mulki, a kyau ne takeganin
zasuzo daya.......

[10:28AM, 8/08/2015] Sireenah2*3

*********NA************

muhd-Abba~Gana
www.abbagana.pun.bz
Ki aje aikinan, yau zamuje banki go and get ready,
don't forget kishafa powder dinki a fuska kada
muje manager yace yana sonki, mommy tee
mezamuje yi a banki? Ni da kin barni gida ma,
Shegia har kin isa kitambayeni toh ubanki zamuje
yi kuma dole kibimu ko kin ki maza je kishirya ina
jiranki. Jiki sanyaye tayi shirinta cikin minti biyar,
Suka kama hanya tana takure gidan gaba tareda
driver su mommy tee ana baya!
*************
Suhail baxa kaje banki karbo kudin da mai
martaba yace ka amso ba kasan fa mabukata zai
rabawa, Hajia yau banajin dadin jikinane sai dai
zuwa gobe zanje, assha autana kasha magani?
ka kira family doctor yazo yadubaka mana, a a
Hajia idan nasha magani zai sakeni, tashi kasha
yanzu sannan please karage tunani Allah yana
sane da halin dakake ciki insha Allah very soon
komai zai daidaita! Nagode Hajia...
************
Banki cike yake dajama'a kallon su mommy tee
kadai ake bawai sun burge mutane ba, a'a
sireenah ce suke mamakin baki irin nata kamar
bayan tukunya, dasuka cema manager ga wadda
suke son gani nan manager korasu, sanayyar
dake tsakaninsa da mommy tee yahana yasa
akama su, don shi ganin yake sun maida shi
shasha yazasu zomasa da macce blacky bayan
passport dinda kegaresa fara ce cikin shiga ta
alfarma tsabanin wannan. Shigarsu mommy tee a
mota a hanyar koma warsu gida sireenah tagano
mesuke son aiwatarwa a zancensu but bata da
bakin magana dolenta shiru tayi tana maganar
zucci wannan karon ne right time dazan Kwaci
yancina but tayaya? Yaa Allah gani gareka, har
suka kai gida batasani ba sai da Hussaina ta ran
Kwasheta a kai tareda fadin yar kauye sai asamu
damar fita daga motar ko? kafin tadawo duniyar
thinking, Suna pallor zazzaune sai cin better
sukeyi karshe suka yanke Shawaran gobe idan
zasu koma banki xasu bata tufafi sabbi and
bazata saka powder ta(shoe shiner! Wanda yayi
daidai da gobe ne yarima suhail shima zaije
bankin, Kuma banki daya suke. Masu karatu
muhadu wata rana idan Allah yanufa muna cikin masu
rai da lafia!.....
muhd-Abba~Gana
Share:

Friday 7 August 2015

ZUWA GA MATAN AURE



Ya kamata duk matar da ta tsinci kanta
adakin aure, awannan zamanin da muke
ciki,ta gode ma Allah. Ba don komai ba,
idan ta
duba zata ga wasu 'yan-mata irinta, sunfi
ta kyawun halitta da iya ado, amma har
yanzu basu samu mijin aure ba.Don haka
zai fi alkhairi agareki ki Qudurce
acikin zuciyarki cewa GIDAN MIJINKI
NAN NE WAJEN NEMAN ALJANNARKI.Ki
rike mijinki hannu bibbiyu, ki kula da
tsaftar jikinki da tsaftar Muhallinku.
Kuma ki
zama ko yaushe ashirye kike domin
biyan bukatar mijinki ko da bai nema ba.
Ki kiyaye MUGAYEN QAWAYE... Ba zasu
rasa yi miki hassada ba. Tunda ke kin
samu miji,su kuwa basu samu ba... Dole
suyi miki hassada.Ki kiyaye sirrin mijinki,
kar ki gaya ma kowa..
Musamman ma kawayenki zasu so suji
abinda yake faruwa.. Don haka kar ki
gaya musu.Idan kuna da 'ya'ya to ki kula
dasu, ki kula da
tsaftarsu. in ma 'ya'yan kishiyarki ne, to
ki kula dasu kamar yadda zaki kula da
'ya'yanki. Ki kiyaye dukkan amanonin
mijinki.
musamman ma iyayensa da 'yan uwansa
da dukiyarsa.
Allah Ya bamu ikon kiyaye Hakkin iyalan
mu.
Share:

SIRRIN ZAMA DA MIJI

bana.jpg

Yar'uwa ga wasu sirruka wanda in har
kinyi amfani dasu tabbas zaki zauna
lafiya da mijin ki, amma fa sai kin daure.
1.Ki guji binciken wayan mijin ki
completely inda hali kar ki taba masa
wayan shi sau dai in shi ya saki.
2.Ki guji zargi akan mijin ki na neman
mata,ki sa a ranki ko wane lokaci mijin ki
na da daman kara aure tunda addini bai
hana ba,maimakon ki ta bin diddigin yana
neman mata,ki dage dayi masa addu'an
kariya daga zina.
3.Ki dena yawan sa ido da bin diddigin
me mijin ki yake yi dan 99.9% na maza
suna son privacy, sa musu ido kan haifar
da matsala tsakanin ku
4.ki guji yawan korafi anyi mun
wannan,an mun wancan.da yawan fushi,
ki bari se an miki laifi kin tara sosai
sannan ki aje shi cikin ki karanta mishi
amma fa ba da gadara ko bada umarni
ba.
Share:

NA KARBI KUDINSA, AMMA NAQI ZABARSA.

bana.jpg

Assalamu alaikum, Malam Dan Allah inada
tambaya kamar haka:
Dan siyasa yabani kudi yace na zabeshi na
karbi kudin, kuma ban zabe shiba.
Menene matsayin kudin da naci ???
Amsa:
====
DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAIJIN
QAI.
To Gaskiya a fahimtata, idan ka tabbatar
bazaka zabe shiba, bai halatta ka amshi
kudinsa ba, saboda Annabi (s.a.w) yana
cewa:
"Musulmai Suna kan sharudansu"
Kamar yadda Bukhari ya ambace shi kuma
Albani ya inganta shi a Irwa'ul galil hadisi
mai lamba ta: 1743.
Sannnan kamar yadda ya haramta aci
dukiyar musulmai ba bisa hakki ba, haka
ya haramta aci dukiyar arne ba bisa hakki
ba, gashi kuma yaudara alama ce daga
cikin alamomin munafuki, kamar yadda
hadisai suka tabbatar.
Yana daga cikin ma'anonin dimukuraddiya
zaben wanda Kakeso, don haka babu
bukatar 6oye-6oye.
Allah shine mafi sani.
Share:

INDAI KINSAN KINA SOYAYYA TO KIKULA DA WANNAN SAQO KI KARANTASHI.

banna.jpg

A MATSAYINKI NA MACE BUDURWA
INDAI KINSAN KINA SOYAYYA TO KIKULA
DA WANNAN SAQO KI KARANTASHI.
(1) ki tsayar da saurayi guda daya tak na
kirki bisa la akarai da ayyukan sa da
halayensa na zahiri.
(2) kitabbata kina sonsa sosai kuma shima
yana sonki sosai.
(3). Kada ki yarda kidade da saurayi, ko
kishaqu dashi ko ki nuna masa tsananin so
batare da iyayensa sun gana da iyayenki
ba.
In yaqi turosu kirabu dashi tunkafin
yagama sace zuciyarki.
(4). Kizama mebin shawarar iyayenki, da
neman shawararsu a harkar soyayya, kada
kibi shawarar Qawaye ko saurayi kobin
shawarar zuciyarki.
(4). Kada kiyarda a kawo miki gulmar
saurayinki ke kuma kidauka koki kama
zargin sa.
A'a sai kinyi bincike na adalci ko kingani
da idonki.
(5). Kada ki kuskura kiyiwa saurayinki
qarya kizama me fada masa gaskiya ,da
yimasa bayanin komai iya saninki.
(6). Kizama me yawaita addu'ah da bawa
Allah zabi a dukkan lamarinki..
(7). kikiyaye zargi da binciken laifinsa
matuqar ya sanar dake komai bai 6oye
miki gaskiya ba.
(9). kidauka dan adam tara yake bai cika
goma ba, kinga zai iya kuskure, dan haka
sai kiyi masa afuwa.
(10). kizama me kare mutuncin kanki ,da
kuma kulada matsayinki batare da girman
kaiba ko jan aji ga masoyi...
JAN AJI A SOYAYYA BA ABIN DAYAKE
HAIFARWA SAI NADAMA.
idan saurayinki ya tsaneki ko yagudu
yabarki ko kin rasa wani abu da yake baki,
kiyi haqury kada kijuya masa baya, kisa
masa shakka a ransa yadinga tunanin anya
kuwa kina son sa da gaske ???
KEDAI KAWAI KI KARE MUTUNCINKI DA
IYA TAKUNKI
(11). Kada kiyarda ki sakarwa saurayinki
fuska yana shigo miki da kalmomin da
basu daceba ko dabi'u.
kamar yace zai samiki zobe, ko zaiga awar
waronki ko zaisa miki jaka, ko zaiga
fulawarki ,ko zai auna kaurinki dadai
sauransu.
SABODA HAKA KIZAMA ME BATA RAI
ADUK SADDA KIKAGA HAKA, KODA
YATAFI KIRABU DASHI, DAMAN BA
NAGARI BANE, SOYAKE YA BATAKI.
Wakilin shaytanne.
(11). Kizama me yiwa saurayinki Al-
qawarin nuna masa soyayya bayan
aurenku, sannan dayi masa biyayya dai dai
gwargwadon
iyawarki.
KISANI DAYAWAN SAMARI AKWAI
MAKIRCI.
Wani yasan ba aure zaiyi ba amma zaizo
yabata miki lokaci.
Wani soyake yakoyi zance sai kawai yazo
wajenki yayi tayi miki qarya batare dakin
fargaba zai dasa miki ciwon so, YA KORAR
MIKI SAMARIN KI NAKIRKI.
Wani kuma kawai so yake yana zuwa
wajen fati dake.
Saboda haka zaina saya miki kaya kala kala
yana fira da ke zai fake da cewa SAI
YAGAMA School KO SAI BAYAN YAGAMA
KARATU ZAI TURO KUYI AURE.
Duk fati ko fikines zai daukeki kutafi.
Wani kuma soyake kawai yana taba jikinki
yaji dadi koda bai kwanta dakeba, saboda
haka zaita binki sauda qafa yana
soyayya dake.
Wani kuma so yake ya bataki.
Irin wadannan samarin sunfi kowanne
hatsari.
Idan yaganki yana sonki yana fara karantar
halayenki IDAN YAGA KE USTAZIYACE TO
ZAIYI SHIGAR USTAZAI HARDA
LITTAFIN SA A HANNU ,HAKA ZAITA KAFA
MIKI TARKO HARSAI KIN FADA.
Idan yaga 'yar BOKOCE zai fito miki a dan
boko.
Idan yaga ke yar duniya ce toshima a
hakan zai fita.
Irin wadannan samarin har kayan mungani
munaso suna kaiwa budurwa, har
iyayensu suna turowa daga qarshe daya
kwanta dake shikenan yabiya buqatarsa,
bazai bari kisami cikiba zaibaki qwaya da
zarar yaga baki da ciki yasan yayi free
tunda yasami abinda yake nema, zai
Qirqiri laifi yalaqa miki domin ku6ata a
karbo kayan sa daga gidanku, koma yabar
miki kayan...
Irinsu akwai makirci da nuna tsagoran
soyayya ga budurwa, domin sukanyi kukan
hawaye a gaban budurwa duk da sunan so
amma yawanci domin ya raunana zuciyar
kine.
Yakan maqale miki har unguwa yana
rakaki koda yaushe.
YAR UWA IN SOYAYAYYA TAI GARDAMA
WAYE YAFI SHAN WUYA DA
TOZARTA ???
SHIN ANAIWA NAMIJI CIKIN SHEGENE KO
BUDURWA AKEWA ???
IDAN ABIN KUNYA YAFITO WAYE ZAI
ZAUNA A GIDA KO MAQOTA BAI ZUWA
DAN KUNYA NAMIJI KO MACE ???
MEYASA NAMIJI ZAI IYAYIWA YAN MATA
BIYAR CIKI BATARE DA AURE BA AMMA
INYAZO NEMAN AURE SAI ABASHI ???
IDAN KUWA MACE TAYI CIKI SAU DAYA
DA
KYAR TAKE AURUWA KOMA SAI TABAR
GARIN ???
MEYASA MACE INTAI CIKI AGIDAN SUMA
TSANARTA AKEYI ,AMMA NAMIJI DAYA
KAWO RAGO DA KUDIN ICE SHIKENAN ???
MATA NAWANE SABODA CIKIN SHEGE
SUKABAR GARINSU KO RAYUWARSU
TA GURBATA AMMA SHI NAMIJI
KAMARMA BAIYI KOMAI BA ???
KO KAMUWA KIKAI DA MUGUN CIWO
WAZAI KULA DAKE YABAKI KUDIN
MAGANI DUK WATA ???
KINTABA GANIN ANSA WUQA A
WUYAN NAMIJI ANCE INBAKA FADI
WACCE KAYIWA CIKIBA SAINA
YANKAKA ???
AMMA WA AKEWA HAKA ???
'Yar uwa kada dadin soyayya, ko dan kudin
da saurayi zai baki kodan zai saki a gaban
mota ,kodan wasu yan riguna dazaina saya
miki HAKAN TASA KIBASHI DAMA HAR
YASANKI 'YAMACE WALLAHI KIN KADE.
IN HAKAN TAFARU TO KITUBA GA
ALLAH (S.W.T) DOMIN SHI MAI
GAFARANE.
FATAN "TAFARKIN TSIRA" ANAN SHINE,
ALLAH YASHIGA TSAKANIN NAGARI DA
MUGU.
ALLAH YAHADA KOWACE YA MACE DA
SAURAYI NAGARI DA ZATA KAISU
GA AURE NAGARTACCE.
MUMA MAZAN ALLAH YABAMU MATA
NAGARI.
Share:

sireenah************--13 (karshen littafi na 1)

samp906c78071de1d454.jpg

sireenah 13



********NA**********


muhd-Abba~Gana


www.abbagana.pun.bz



Azeema yau kika samu damar
shigowa school? Nayi ta dubanki wurin birthday
din baki zo ba? Why kina nufin baki sauko daga
fushin dakike dashi? Kedai friend bari mani zance
birthday din dayaso nazo dole zai nemeni ke
kanki kinsan yadda nake ta kudiri akan birthday
din amma wanda nake dominsa baima san inayi
ba! Yau ma naga an kwana biyu bangansa ba
shiyasa nace bari leko school kozamu hadu dashi
kinsan ba'a wani lectures sosai shiyasa nadaina
zuwa dayake munkusa fara exam! Allah sarki
azeema kindamu da suhail sam bana tunanin
yadamu dake, meyasa kika Ce haka friend?
Banso kiji zancen a bakina but da zaman ki cikin
duhu gara na fitar dake! shigowarki school bakiyi
noticing ana kallon ki? Friend kina wani zance
kamar bakisan yan campus dinnan dolene suka
kalleni saboda sanin kanki ne nafisu haduwa, iya
kwalliya saka tufafi masu tsada etc (Yabon kai
jahilci azeema kibari mu yabeki ko yakukace?).
Azeema Allah kin iyasa mutum dariar takaici toh
wannan karon kallon da ake maki yasha babban,
Friend bangane ba yimani bayani dallah-dallah
yadda zan fahimta! Ina nufin kallon da ake maki
na shashane wadda batasan metakeyi ba saboda
zancen yafito fili suhail baya sonki matsayin
kawa(Friend) yadauke ki! Azeema dake zaune
saida ta mike tsaye cikin zare ido tareda fadin
what..! kinsan mekike fada Kuwa? Tabbas nasan
abinda nake fada Suhail dinki yasa anyi
announcement a TV da nan school din ma..
Announcement fa? baya sona yace? Lallai yaci
mutuncina yagama dani... Calm down Azeema
bahaka yace ba kibari nayi maki bayani mana,
zance yafito fili suhail yadade yanason wata
safna, basu taba haduwa ba sai a birthday dinsa,
a farko ma su yan biyune suka gansu inda yake
da safnarsa sun dauka yar uwarsa ce(jinin
sarauta) saboda tayi shigar "ya "yan sarakuna,
ashe bahaka abin yake ba, announcement dinda
akayi ne aka gano basuda alaka, ance dai safnar
tana karatu a wannan school baisan wane faculty
take ba, yayi alkwalin duk Wanda yasamu
labarinta ko yaganta zaiyi masa kyauta na
mussamman da million biyu bayada photon ta
amma yasa anyi masa zanenta yamanna ko ina
cikin school din! Da alamu yarinyar bakaramin
kyaune da'ita zanen yayi kyausosai inaga da
ansaka real picture dinta a lot people will fall for
her. Tirkashi wallahi bai isaba nizai wulakanta a
idon jama'a? Mena rasa daizaiyi mani haka?
Friend don Allah kalleni da kyau kiga mai narasa,
Azeema baki rasa komai ba kiyi hakuri Kawai
Allah zai sama maki wanda yafishi.(structure na
azeema yanada kyau doguwace, tanada jiki.
yanayin jikin nata yayi mata kyau course irin jikin
'yan lukuta tanada gashi daidai ita inshort balaifi
tana cikin mata second class but babu halin
kwarai kamar wata anan) Friend ma shiru tayi taki fadan gaskia
don tafi kowa sanin azeema bata Kirki gudun
tashin hankali yasa tace batayi lacking anything!
Wanda yafishi fa kika ce bana tunanin akwai kina
ganin zan samu mai kyau, arziki mulki kamarsa?
Azeema sai yanzu nagano bama son kwarai kike
masa baki tunanin kyawo mai gushewa ne? Arziki
ma zai iya karewa ko baki taba gani ba nasan
kinsha jin labaran masu kudin da ke talauce wa,
mulki dakike ganin baizamo lallai zaiyi sarautar
ba mai yiwu ya mutu kafin lokacin! Ke ni rabani
da wani zancen banza naki, dazan samu Wanda
yafi shi dukkan abinda na lissafa zan hakura da
suhail, yanzu dai Nasan ta yadda zan bullowa
lamarin, bai'sa ya ruguza mani plans dina never...
Gamu gani Azeema lashe money(lols)....
******************** Sireenah duk ta rame
batasan tana kaunar suhail sai da ta kaurace
masa, a nata tunanin idan tayi hakan zata cireshi
a rayuwarta kullum sonsa karuwa yake a
zuciyarta more especially idan tagansa school.
Kullum cikin tunani take ba mai lallashinta
sometimes takanyi niyyar gayawa suhail itace
yake nema but tsoron abinda zaiyi biyo baya
takeyi wa gudu idan takalli yanayin shigarta
gakuma bakin dake fuskarta, taya ma zai yarda
itace bayanshi wadda yagani yar hutu Ce gata
fara kyakkyawa, bazai bata damar yin explanation
zai wulakanta ta. Karshe dai ta yanke shawarar
kiran muneerah kozata sama mata mafita saidai
kash bata amshi numberta na London yanayin
yadda rabuwarsu takasance. dabara yafado mata
na kiran hajiar muneera,Ohh bari na kira Hajia
mama(mommyn muneerah) tana dailing number
taji wayar kashe dama ka'idar Hajia mama ne
idan 10pm yayi kashe wayar take! Ko banza
goma da rabi ne yanzu so she decided tabari
zuwaa dasafe. Dataga barci yaki zuwa dolenta
tashi domin yin wasuu ayyuka. ****** Mommy
tee yau munje banki withdrawing kudi a account
dinki bamu tararda komai ciki. Hakane my twins
jiya suka sanardani namanta bangaya muku ba,
daman tun bayan rasuwar Alhaji kudin da natara
ne nake amfani dashi banso nafara amfani da
kudin alhaji yanzu ba nayi musu dogon burri
sosai nadakatar da maikata sanyen duk wani abu
dasuke sarrafawa (raw materials) kawai aikinsu
su sayarda abubuwanda sukayi{Goods) sai sun
tabbatar da komai yakare ankai kudade cikin
account din Alhaji, su sanar dani! Kunga lokacin
nikuma zan samu damar kwashe gabadaya kudin
Alhaji nasayar da companies dake garesa hadi da
duk wani properties nasa daganan kawai mukoma
England dazama! Na samu labarin saura kadan
su sayar da komai na companies din, burrina
yakusa cika! Amma zancen auren dayanku da
suhail inason yatabbata shine target dina a
yanzu. Ga wannan check kuje account din
mahaifinku ku amso kudi naira million dari yadda
zan samu damar yin wasu missions ciki! Wow
mommy tee mungode sosai Allah yabar mana ke
yazamuyi da sireenah¡ trust me now kuna zance
kamar baku sanni ba zan kasheta kamar yadda
kashe uwarta! Mommy tee aji tsoron God. Kuna
ganin zataci nasara? Tsakanin Azeema, Yan biyu
da Sireenah wazai auri suhail? Idan Asiri yatonu
Sireenah zata tsira da ranta? yamaganar sauran
companies na alhaji sadam saraki dake outside
countrie wake tafiyar dasu? Find out in Sireenah
2.. Alhamdullah muhadu a littafina kashi nabiyu 2
Naku har kullum muhammad Abba Gana (sharifin~zamani)! Don gera, karin bayani,gargadi,jan hankali,nasiha,kauna,tambarin girma,KARASHI da dai sauran su call or Whatsapp me @ (09039016969)
Sadaukarwa: My sweet Mommy (HADIZA)
wish you long life and prosperity. Godia ga
dukkan yabo ga sis Surayyat Suraaj(admin
na mu2unci page) on facebook! Jinjina gareku
members na: Duniyar marubuta, Hausa novels!.
Ban manta daku ba members na groups dina,da
Sirrinmu (1,2 & 3) & Zumunchi(1,2&3). Gaisuwa
na mussamman gareku HAUSA NOVELS & OTHERS,HAUSA NOVELS
WRITER'S & Darul Qur'an! A karshe Allah yajikan
yayanah, dasauran yan uwa musulmi
dasuka rigamu gidan gaskia! Love You allmy well
wishers. Happy jumma'a @ kareem



muhd-Anba~Gana

www.abbagana.pun.bz
Share:

sireenah************--12

samp906c78071de1d454.jpg

sireenah 12



********NA*****n*****


muhd-Abba~Gana


www.abbagana.pun.bz




Suhail gaskia nida mahaifinka mungaji da wannan
hali naka idan baka da lafiane sanar dani munyi
maka alkwalin sai inda karfin mu yakare wurin
nema maka magani bawai kayi ta yawo mana da
hankali kullum excuse dinka bakaga wacce kake
so ba bayan ga mata nan birjik mun hada maka
birthday ko zakaga wacce kake so amma har Yau
shiru kakeji, karshema shiga kayi cikin damuwa
ga ramar dakake famanyi tun bayan birthday din
kaki fadin meye matsalarka.
Hajia don Allah kiyi hakuri, ki kwantar hankalinki
lafiata qalau, bahaka bane nasamu wacce nake
so yanzu. Alhamdullah autanah ko kaifa har kasa
naji duk wani bacin ran dake tattare dani yagushe
Allah yayi maka albarka, yasunanta? Yar gidan
wace? wane gari take? yasunan unguwarsu? a
ina kuka hadu? Waye mahaifinta? sanar dani
autanah Alhaji nashigowa zansa yaje ayi tambaya
gidansu yarinyar ko ya aika mutanensa. Sunanta
Safna tana karatu a makarantar mu.... Kayi shiru
suhail kai nake sauraro, gaskia Hajia bansan
waye mahaifinta ba! Subhanallahi shegiya Ce?
A'a Hajia bana tunanin shegiace abinda nake nufi
shine bansan gidansu ba, I don't have her
address munhadu a 2go chat bansan wane course
take karatu ba, kinga bahalin zuwa gidansu,
Kullum naje school sai na yawata makarantar
baki daya but ban taba cin karo da'ita ko mai
kama da'ita bana gani, har nafara tunanin KO
aljanace idanma ba aljana bace ina hasashen
bata sona ne may be am not her typed!, tun ran
birthday tadaina hawa 2go chat din,she is always
offline, banida number wayarta balle nakirata,
dalilin hakane yasa naki gaya maki nasamu
wacce nake so! Watakila rashin lafia yahanata
hawa online.Hajia idan batada lafia zanji a jikina.
Suhail anya bagamo kayiba? Wannan abu akwai
boyayyen al'amari da rikitarwa cikinsa zuciata ya
shiga raya mani kodai aljana ce, abin tambaya
anan shine kun taba haduwa ne?. Eh Hajia a
gidannan ma muka hadu wurin birthday partyn
nine nayi inviting dinta. Yanzu dai abinda nake so
dakai shine ka yawaita addua ko Allah zai sa
kaganta nima zan cigaba dayi maka addu'a
yakamata ayi sanarwa ko Allah zaisa a dace,
karage sa damuwa a ranka zaka ganta cikin
sauki insha Allah idan safnar takasance bil'adama
. Kozaka duba cikin pictures dinda akayi na
birthday din da video coverage may be zaka
ganta kagani daganan sai muyi tracing nakusa
da'ita koda sun Santa?, Batanan koda mai video
coverage yazo kinsan yayi lattin zuwa pictures
kuma family members kadai akayiwa bayan
tafiyarta ne mukayi dasauran mutane bana
tunanin tana ciki ko families din ma nasaura
akayi dani koda su Baba karami(daddyn
muneerah) sukayi nasu bana nan har suka wuce
bamu haduba, Tabbas wannan haka yake
muneerah tayi ta nemanka alokacin bata ganka
ba taso ku gaisa da wata kawarta akayi rashin
sa'a bata ganka ba naji haushi sosai don naso
kanemi Kawar muneerah din don da alamu zatayi
hankali. Allah sarki muneerah harna manta da'ita
bamu hadu ba koda takoma London amma insha
Allah zanje London idan mukayi Hutu, Hajia
kinadaina zancen wata nariga nayi zurfi ason
safna. Shikenan autanah tashi katafi zamu
tattauna da Alhaji zuwa anjima idan yazo..


muhd-Abba~Gana


www.abbagana.pun.bz
Share:

sireenah**********---11

samp906c78071de1d454.jpg

Sireenaah 11


********by**********

muhd-Abba~Gana


www.abbagana.pun.bz


! Munafukar tsiya mekika tsaya kallo, yi sauri
kigama aikin dana sakaki kifece daganan kafin na
makeki mayyar banza idanuwa kamar na mujiya,
cikin rawar jiki tagama aikin datakeyi tabar
sashen mommyn!by muhd Abba Gana Allah sarki sireenah kada ki
damu" What surely goes up most surely comes
down " Ko ba haka bane masu karatu?...by muhd abba gana Haka
dai mommy tee da yan biyunta suka cigaba da
mugaye plans dinsu basu san wacce sukeyi domin
ita tana jinsu kuma tasha alwashin bazata yarda
su san Itace suke nema domin tsira da rauywarta
ko kunga laifinta. ********* Azeema kwantar da
hankalinki babu wanda ya'isa ya wulakanta mani
ke muddin ina numfashi a doron kasa, akan wata
talakar banza zai mareki har yace kun rabu yayi
kadan wallahi shidin nawa yake? Nayi maki
alkwali karshema sai ya aureki kin juyashi son
ranki kamar masa(waina) naga karshen
wulakantaki! Daddy idan hakan takasance zanyi
farin ciki sosai dakaga mani komai dunia. Kada ki
damu azeema share hawayenki kinji,Toh daddy!
Zamu ci riba biyu idan akayi aurenki dashi, hada
iri da mai martaba Yahya ribane sosai hanyar
karin samuwar arzikina ne, bana kaunar hada da
iri datalakawa, meye amfanin kabayar ba'a maida
maka? Gaskiane daddy daman ni inason aurensa
ne don nunawa dunia gwarzon namiji one in town,
zancen arziki ba'a magana ko banza shi kadaine
namiji wurin mahaifansa nasan idan mai martaba
yarasu shine za'a sakawar ragamar dukiyar! Kunji
jahila kamar tasan wanda zai riga wani mutuwa!
Haba Daddyn azeema kazauna kana biye ma
shirmen azeema nasan suhail bazai sa hannu ya
mareta muddin balaifi tayi masa ba, Kerufe mani
baki daman nasan bakya son yata kin haifeta
kawai ne amma baki kaunarta, haba daddyn
azeema wazaiki dan cikinsa naga rashin dacewar
halin nata ne tadaina wulakanta talaKawa da son
abin dunia wannan rashin gode wa Allah ne, haka
kaima naji kabawa suhail kyautAr motar naira
million 50 Wanda nasan badon Allah kayi kyautar
ba kayine idan birtday azeema yatashi a linka
maka fiyeda hakan wallahi kuji tsoron haduwa da
ubangijinku ku yawaita gode masa kudaina
hangen abin wani. Yayi malama uwar addini idan
kingama yi mana wa'azin sai kibace mani
daganan, nasha gaya maki idan bazakiyi
supporting kan abinda nakeyi da" yata ba kidinga
samana idanu! Zulfa'u ki guji randa zaki kaini
bango! Yi hakuri daddyn azeema Allah yahuci
zuciarka nadaina saka kaina cikin issue dinku sai
dai fatana gareku Allah yashiryeku yasa kugano
gaskia! Ke tashi kifice kafin ki kara tunzurani,
Haka zulfa'u ta fice jiki sanyaye. Shi Kuma yaci
gaba da bawa "yarsa hakuri da muguyen
shawarwari. Ashe azeema wurin mahaifinta duk
tayi gadon rashin son talakawa (like father like
daughter) Allah yakyauta. Daddyn azeema(Alhaji
Bello) yakasance irin marassa godewa Allah ne
abin dunia yarufe masa idanu shi kullum burinsa
yaga yafi natare dashi duk yakasance cikin jerin
manyan attajiran garin Abuja amma a banza.
Baya sadaka,zakka don yaza masa dole yake
fitarwa muddin yayi kyauta toh zaici ribane
matarsa batada irin halinsa tana son talakawa
haka tana kyautata musu itace silar arzikin
mijinta, ya aureta a lokacin da baya da wani aiki
mai tsoka, kudin gadon da aka rabane lokacin da
mahaifinta yarasu tadauki nata kason tabashi
don yaja jari Allah yasa masa hannu har yayi
wannan arzikin amma don batulci irin nasa shine
ke kyamar talaka a kullum bayada magana banda
yace talaka bayin sune(attajirai) don su bauta
(aiki) mana akayosu, Allah yasaita daddyn
azeema kozai gano gaskia "Matsayin talaka da
mai arzikin duk dayake a wurin Allah" Wanda yafi
wani wurin Allah shine Wanda yafi tsoronsa" Allah
yayi masu arzikin da talakawa don su bauta
masa" Yana sane da halin da bawansa yake ciki.
Zulfa'u bata isa tacewa "yarta ga abinda yadace
kiyi ba saboda "yarta axeema tasamu grantee
daga mahaifinta what ever she wish to do zatayi
babu wanda ya,isa yahanata. Yadauka ko sone
baisan lalaci bane, zamu gani idan zai haifa musu
da mai ido....mu hadu a kashi na gaba ************


muhd-Abba~Gana


www.abbagana.pun.bz
Share:

sireenah**********--10

samp906c78071de1d454.jpg

Sireenah 10



********NA***********
muhd-Abba~Gana



Funny girl lafia? Daman kinsanni ne? Naga kamar
kin tsorata daganina, Ko kinfasa so nane? Please
funny girl talk to me. Dakyar sireenah amsa masa
da uhm...mm a' a bakomai cikin jerin tambayoyin
da yayi mata. Okay toh zauna mana ga wuri nan
dana tanadar miki! An kayata wurin swimming
pool din sosai, ruwan cikinsa yanada haske
tamkar ba'a shiga cikinsa! Kujerun shakatawa sun
zagaye ruwan, ta bangaren ruwan akwai
matsakacin rumfa wanda a karkashinsa akwai
kujeru biyu da table saman table din akwai
furanni da kayan motsa baki Wanda kamar lover
boy ne ya tanadawa sireenah. Bayan sun zauna
ne yafara bayani kamar haka:- Nasan zakiyi
mamakin sosai akaina, abinda nake gaya maki a
chat bashine kika gani a zahiri ba, yanuna mata
cewa shi dan dako ne, primary school kadai
yakare baisamu damar cigaba karatunsa saboda
halin rashi na mahaifansa dalilin haka yabar
karatun don ya tallafa masu a karshe shine ke
dawainiya dasu. Gashi Taga tsabanin abinda
yafada mata fatarsa da tufafin dake jikinsa kadai
sun isa kasan koshi waye, balle shi sannanne ga
mutane, sireenar ma tayi masa farin sani. Nasan
ko asalin suna na baki sani ba koda yake
laifinane bangaya maki ba kema baki nemi sanin
sunan nawa, bansan meye dalilinki ba sai dai ni
inada nawa dalilin bakomai bane face nasamu
mai sona tsakani da Allah, sanin kankine dakyar
nasamu mai sona idan zan nuna ni wani. Dayake
Allah maijin rokon bayinsa ne yahadani dake
wanda nake ganin tamkar nafi kowa sa'a duniya
samun macce irinki sai an tona, fuskarki kadai na
gusar da bacin rai, muryarki koda zan sauraresa
daga safe zuwa daare bazan gaji ba gaskia
Alhamdullah. Ni suna na Suhail Yahya Yusuf
nasan bazaki rasa sanin waye ni muddin a garin
Abuja kike zama but never the less ni haifafen
dan kebbi ne ina karatu a Nile university studying
medicine mun kusa gamawa gidanmune nan, nine
ake yiwa birthday ,haka yacigaba dagaya mata
koshi waye batace masa uffan ba har yakare
already tasan koshi waye but bana tunanin suhail
yaganeta amma kamar yana zargin muryarta
kamar yataba jinsa sai dai yakasa tunawa,
yabukaci sireenah tabashi labarinta wanda tayi
alkwalin bashi duk randa suka hadu sai gashi
haduwarsu ba'a yadda tayi tunaninsa bane, nan
tasoma bashi wani labari daban inda tace masa
sunanta Safnah tana karatu a Nile university zata
cigaba da labarin kira yashigo mata koda taduba
mommy tee Ce cikin rawar jiki ta amsa kiran,
"kitabbatar kindawo gida cikin mint 15 ko baki
gama lectures din ba i dont care, akwai abinda
zakiyi mani kada kifi 15mints baki dawo ba
muddin kikara ko minti daya cikin 15mnts din
kinsan saura! Ganinan tafe mommy insha Allah!
Tana gamawa kiran muneerah yashigo Sireenah
kizo mutafi yanzu aka kirani gobe dasafe zamuyi
test Kuma idan nayi missing zanyi kari over dinsa
anyi mani booking flight in 20mnt jirgin zai tashi
so hurry up please kizo mutafi. Gani nan tafe
yanzu nima mommy tee tasanar dani tana nema
na cikin gaggawa. Suna gama wayar yayi daidai
da suhail shima yana waya and his attention
yanaga wayar saboda mahaifinsa ne yakirasa
yabata baya! So sireenah bata da choice than tayi
tafiyarta batare da sunyi sallama ba don ta kagu
ta'isa gida. Tafiyar ta keda wuya yagama wayar
da yakeyi koda ya juyo baiganta ba ya dudduba
ko'ina banganta ba har ta gun da ake birthday
din,motocinsu tuni sun dade da barin harabar
gidan , baiji dadin hakan ba gashi baisan address
din gidansu ba, har aka gama birthday din he was
sad.
**********
Tun a mota tafara canza tufafinta daman dashi
taxo, tagoga shoe shiner dinta inshort takoma
yadda take a baya duk wanda yaganta baxaice
itace sarauniyar kyau ta daxu totally takoma
blacky. Sun yi ban kwana da muneerah cikin
kewar juna suka rabu. Allah sarki kawayen basu
damar hira ba balle sireenah tagaya mata wane
lover boy.
Koda sireenah taje gida bata tarar da mommy tee
a parlour ba shiya bata damar hiding tufafinta na
birthday a dakinta kafin taje sashen mommy tee,
abin haushi bawani aikin Kirki bane tea zata
hadamata da indomie wanda yan aikin ma zasu
iya. Tana cikin aikin ne yan biyu suka shigo
ransu a bace da alamu kwalliyar tasu yatashi a
banza. Oyoyo my twins yanaga kamar ranku
abace kodai banasara ne? Mommy tee kedai bari
wata banza tayi mana kwacensa da alamu jinin
sarautace, muna cikin zagaya wa da Hussai muka
hangoshi da wata munso muje ganin wacece
securities din gidan suka hanamu karasawa!
Tabdijan ko wacece tadebo ruwan dafa kanta tayi
kadan tayi sharing saurayi with my twins. Abinda
nake so daku find out yar gidan uban waye
nikuma zansan yadda zanyi da ita karshe ma na
salwantar da rayuwarta . Duk abinda suke fada
akan kunnen sireenah ta tsorata sosai gudun irin
rikicin nan yasa taki gaya masa asalin sunanta
tana sane da bakin hali na mommy tee mugunta
abune mai sauki a wurinta. Yanzu menene
mafita?....


muhd-Abba~Gana


For more vist

Www.abbagana.pun.bz
Share:

sireenah**********--9

samp906c78071de1d454.jpg

sireenah 9


********NA**********

muhd-Abba~Gana




Yarima suhail cikin shigarsa ta alfarma yake,
tufafin sun kara fitar da zatinsa ,damacan shi mai
kwarjini ne gashi da iya tsara kwalliya tamkar
macce shiyasa mata ke kara likemasa (mata
sunfi son namiji wanda ya iya tsara kwalliya
komai rashin tsadar tufafi da tsabta) tare yake da
wasu abokansa biyu suna tafia a nutse sai daidai
inda ake birthday din mawaka naganinsu suka
fara yimasa waka. wurin birthday din yakoshin
mutane different types na garin Abuja da mukota
Yashiga gaisawa da mutane kafin ya zauna kusa
da mai martaba aka soma gudanar da partyn
cikin tsari ba haya niya, Yan biyun mommy tee
sun zo balaifi duk da tufafin nasu mai tsada ne
basuyi wani kyau cikinsa ba sunyi make up over,
ga jikin daman yasha bleaching, ga uban
attachment (gashin doki) din da suka saka, komai
nasu is new but a banxa sukansu sun raina
kwalliyarsu, saboda akwai mutanen da suka fisu
kwalliya etc,wacce tagaice su tayi kwalliyar kece
raini itama sun haadu sai rawar kai sukeyi kamar
don sanda dasu Bakowa bace tagaiyace su face
Kawar Azeema ( gayyar-gayya Keenan) Banga
Azeemar ba ko lafia?... birthday din yayi nisa
kafin muneerah suka samu damar hallara dayake
da nisa tsakanin gidan su, sun ka saance yan
uwan mai martaba ne, don haka harta gefen da
ake birthday din aka bar motocinsu, gabaki daya
jama'ar dake gurin kallo yakoma gun motocin
suna jiran suga su waye ciki? bodyguards suka
fito cikin sauri domin bude motocin Alhaji da hajia
ne farkon fitowa kafin muneerah then sireenah a
hankali suke tafia cikin kasaita ko banza suna
sane basuda makusa,.. aka shiga yiwa Alhaji
kirari irin na jinin sarauta mutanen wurin sun
kagu daganin fuskokin "yan matan but ba hali
saboda kwalliyar alkibbar ya rufe fuskarsu.
Daman wurin zamansu yana kusa da mai
martaba sai dai kash basu tarar da yarima nima
bansan inda yake ba, muneerah sun bude
fuskokinsu bayan zamansu inda aka tanada
musu, duk wannan abu da ake yan biyu Mommy
tee basu samu damar ganin fuskokin su sireenah
tsabar yawan mutanen gun , mutane da dama
sunyi tsabbatun kyawo irin na "yan matan bama
kamar sireenah ba wacce mutanen wurin sukayi
wa lakabi da sarauniyar kyau! Ciye ciye da lashe
lashe akeyi saboda anyi abinci, abinsha kala kala
daidai bukatar mutum! Muneerah lover boy yace
naje ta wurin swimming pool yana jira na acan,
hala ina ne gurin? Lah ai banisa muje na nuna
maki amma gaskia bazan isa ba saboda so nake
nashiga cikin gida nemo Yaya suhail kinga kafin
mutafi ina son kugaisa zanzo dashi ta nan! toh
muje please I am so eager to see him wallahi, Oh
su sireenah miss Luv mutafi na kaiki, yauwa
muneerahta.by Abba gana
Bayan sun kai daidai gun muneerah bata tsaya ba
kamar yadda tace cikin gida ta wuce! Yabada
baya dalilin haka batasamu ganinsa ba dayake
Kuma kan sireenah a kasa yake isarta inda yake
tsaye, kafin ta daga kanta tare da saukar da
hullar alkibar wanda yayi daidai da juyowar lover
boy.. What daman kaine lover boy ta tsorata
sosai daganinsa gashi ta saka shi cikin mamaki
da tsorata Kyanta kodai aljannace nayi gamo
da'ita?! Wanene shi? Sun san juna daman ne.
Nabarku a haka Sai gobe insha Allah....


muhd-Abba~Gana
Share:

Tallata Kayanka

Guide Tricks Blog

Be With Me Technology

Popular Posts

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Blog Archive