shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wanda aka fi sani da hausa novel wanda ni Muhammad abba gana nake rubutawa dan wayar tare da fadakarwa ga mutane a yanayin da muke ciki.

Tuesday 11 August 2015

Yadda Ake Hada Sabulu Soulp Asiyar A Samu Riba Mai Yawa

ni.jpg

DASUNAN ALLAH MAI RAHAMA
MAI JINKAI,DA SALATI GA
SHUGABAN HALITTAN ALLAH
ANNABI MUHAMMAD (SAW) DA
IYALANSA DA SAHABBANSA.
DALILIN YIN WANNAN POST DIN
Nayi wannan post dinne don
taimakon matasanmu maza da mata
game da abinda yashafi
SANA'A.Nayi tattaki zuwa wajen da
akeyin wannan aiki badan komaiba
sai don taimakawa al'ummata.
Da farko dolene ka tanaji
wadannan abubuwa....
1.Gishirin Soda
2.Alayyadi
3.Ruwa
4.Kumfa
5.Kala
6.Stati
7.Turare.
Bayan katanaji wadannan
abubuwan, kawai ka auna ruwa
kofi hudu,sai ka auna gishirin
sodannan kofi daya ka zuba
aciki,sai kabarshi ya kwana daya
idan kahadashi kamar da karfe
goma 10:00am to sai karfe 10:00Na
safiyar gobe yayi sannan ka cigaba
da hadashi
Idan ka dauko wannan ruwan daka
hadashi da gishirin soda saika auna
cikin kofi daya,sai ka auna alayyadi
cikin kofi hudu sai kasa sanda ko
muciya karinka juyawa idan kafara
juyawa ya dame to sai kuma kazuba
kumfa sai kaci gaba da juyawa sai
ka zuba kala da turare da statinnan
saika cigaba da juyawa sai ka dauko
container ka zuba idan yasha iska
zakasha mamaki da yardan Allah.
Idan kajika gishirin sodan nan
karkasa hannu dan zai konaka,Idan
kuma Allah ya aikoma ka kone
bakasaniba,kanajin zafi kawai sai
kashafa man Alayyadi a wajen da
ya kone to bazai tashiba da yardan
Allah,Idan kuma akai sakaci aka
sha to za'a fa mutu Allah yakare,mu
kuma sai mu kiyaye mu kaudashi a
inda yara bazasu ta6aba.
DA FATAN ALLAH YASA MUDACE
KUMA MU AMFANA DA ABINDA
MUKA KOYA.
Daga masana'antar muhd abba gana
Share:

15 comments:

  1. gaskiya mungode daga jabir dan uwa www.jabir dan uwa

    ReplyDelete
  2. farmer abubakar17 May 2016 at 07:48

    naji dadi na daina sayen sabulu kuma zan taimaki jama'a.na gode

    ReplyDelete
  3. Allah Yakara Basira

    ReplyDelete
  4. Aishatu abubakar4 June 2016 at 12:00

    Mungode allahsa nuyi aiki da abinda muka iya.

    ReplyDelete
  5. Kabir Muhammad27 June 2016 at 08:23

    Dan Allah ina tambaya, menene kala? Kuma a'ina ake samunsa shi da gishirin soda?

    ReplyDelete
  6. Wanne kalar cup babba ko karami

    ReplyDelete
  7. Don Allah sabulun wanki ne ko kuwa ?

    ReplyDelete
  8. Thank so much

    ReplyDelete
  9. muna godia.inada tambaya minene alayyadi

    ReplyDelete
  10. To ta kaka zan samu In saye wanan kayak hadin?

    ReplyDelete
    Replies
    1. zaka same su a kasuwa wajen da ake siyar da kayan chemicals nasu man shafawa

      Delete
  11. Ina koyon yadda ake yin sabulu don Allah a taimaka mini

    ReplyDelete
    Replies
    1. Shin ka karanta gaba daya abinda mukayi jawabi akai?

      Delete
  12. More power to ur elbow Mal Abbagana,Allah yayi albarka

    ReplyDelete

pls drop down your comment......
dan Allah ku ajiye comment.

Tallata Kayanka

Guide Tricks Blog

Be With Me Technology

Popular Posts

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Blog Archive