Assalamu Alaikum barkanmu da warhaka barkanmu da sake saduwa daku a cikin sabon shirin namu wadda yake zuwa muku kai tsaye daga shafin “Abbagana Novels”, Kuna tare da jikan Marubuta Muhammad Abba Gana. Kuma insha Alllahu yau zamuyi jawabine akan yadda zaki mallake zuciyar mijinki cikin sauki.
Sunday, 6 December 2020
Wednesday, 20 February 2019
SHAWARWARI GUDA 7 DON INGANTA TARBIYYAR YARA - SIFFOFIN UWA TAGARI 12
Tarbiya wata kalma ce da take nuni ga yadda ake kula da ‘ya’yanmu da kuma na kasa da mu. Hakika, girma da muhimmancin kalmar 'tarbiyya' sun wuce yadda muke anfani da ita a yau da kullun. Tarbiya ta banbanta da daga al’umma zuwa al’umma, ma'ana, abinda ke da kyau ga wasu mutanen ba lalai bane ya zama yana da kyau ga wasu. Amma a gani nan a kwai wasu abubuwa da za su da ce da kowa, kuma sune na kawo a nan zan yi dan sharhi a kansu, musamman hanyoyin da za’a bi don inganta tarbiya yara.
1. Abu na farko shine cusa wa yaro tsoron Allah. Hanyar cusa wa yaro tsoron Allah kuwa shine shine sanar da shi Allah din da abinda Ya yi umarni da abinda Ya yi hani. A duk lokacin da yaro ya zama mai tsoron Allah da kokarin yin abinda Allah Ya yi umurni, da barin abinda Ya yi hani, tarbiyarsa zai zamo mai sauki a wurin iyayensa, ko yaro na tare da su ko ba ya tare da su.
2. Cusawa yara son ilimi. Kasancewar ilimi shine ginshikin rayuwa, to hakkin iyaye ne su muhimmantar da ilimi wajen tarbiyar ‘ya’yan su. Su yi wannan ta hanyar maida hankali da ilmantar da ‘ya’yan nasu da kuma su kansu iyayen. Ya kamata su dauki ilimi a matsayin haske mai haskaka rayuwa ta ko wani fanni ba wai kawai don neman aikin abin duniya ba.
3. Dole iyaye su kasan ce abin koyi ga ‘ya’yansu. Ma’ana a nan duk wani abinda iyaye za suyi, ya kasan ce irin abinda suke son ‘ya’yansu suyi ne, domin shi yaro yafi koyon abu a aikace fiye da abinda za’a gaya masa. Misali in har uwa bata son yaran ta su koyi zagi da tsinuwa to ta kiyaye zage-zage.
4. Yawan kula da abinda yaro ke yi. A matsayin mu na masu kula da ‘ya’yanmu ya zama lallai mu kula da duk wani abinda suke yi. Na san yana da wahala amma wajibi ne in har ana son a yi tarbiya ta kwarai. Kula ba yana nufi hana su sakewa, sai dai yana nufin kasancewa kana/kina sane da inda suke ko abinda suke aikatawa dai dai gwargwadon iyawa a kowani lokaci. Wannan zai ba da ikon sanin halin da yaro ke ciki, sannan in yayi ba daidai ba za a gyara masa.
5. Iyaye su guji yin munanan kalamai a kan yara. Kowa ya sani a addini mugun baki bai da kyau ga ‘ya’ya. Yaro idan ya sosa wa wasu iyayen rai, musamman iyaye mata, sai ka ji ana “Allah wadaran ka wane” ko “la’a nanne,” da dai sauran munanan kalamai, wanda suna iya binshi, sai ka ga yaro ya shiga yin taurin kai ba zai saurara wa kowa ba, ya zamanto bai da muntunci bai gani wani da mutunci, kuma daga karshe a rasa yadda za’ayi da shi. Allah ya sauwake.
6. Koya wa yaro girmama na gaba da shi. In ka ga yaro na girmama na gaba dashi to ya gani a na yi ne. Iyaye dole su nuna wa ‘ya’yan su muhimmanci girmama babba ko da daga ina mutuminnnan yake, daga kauye ne, birni ne, talakane shi, mai dukiya ne, addinku daya ko ba daya ba. Idan iyaye suka yi haka a aikace to yaro shima zai yi.
7. Koyawa yara kyauta ta hanyar aikatawa. Tarbiya ta kunshi rayuwa ce gurungundumarta, sabo da haka komai ya kamata yana ciki. Kyauta aba ce mai kyau da yara ya kamata su fahimci cewar mutun ya zamanto mai yawan bayarwa ba wai mai yawan tsammaniba. Iyaye su kasance masu kyauta don nuna wa yara mahimmancin kyautar, misali ta hanyar aikensu su kai kyauta gidan dangi ko makota ko dai abokan arziki. Kuma kar a yarda a rika yin gori idan ambayar, sabo da yara suna jin duk abinda iyaye su ke fada, kuma su ma in sun tashi haka za su yi.
Allah Ya ba ku ikon tarbiyartar da 'ya'yanku ta hanya madaidaiciya.
SHIN KO KUN SAN LADAN DA MACE KE SAMU A GIDAN MIJINTA? - SIFFOFIN UWA TAGARI 11
Albishirinku matan aure. Zaman gidan miji da kuke yi da yi wa mazajenku hidima, Allah ya tanada muku lada mai yawa. Ga kadan daga cikin irin garabasa dake tattare da aure ga mata.
*Daga lokacin da kikayi aure idan ki ka yi sallah, Allah zai baki lada dubu
*Idan kika kalli fuskar mijinki kika yi farinciki Allah zai baki ladan zikiri dubu
*Idan kika bashi ruwa ya sha Allah zai baki ladan azumin shekara daya
*Idan kika dafa masa abinci mai dadi duk girki daya Allah zai baki ladan hajji da umrah.
*Idan kin samu ciki kullum za'a rubuta miki ladan azumi shi kuma mijin a rubuta masa ladan kiyamul laili, har ki haihu
*Idan kika fara nakuda duk numfashi daya Allah zai baki lada kaman kin yanta bawa daya.
*Kina haihuwa Allah zai gafarta miki zunubanki, kin koma kamar lokacin da a ka haifeki ma'ana duk zununbanki Allah ya gafarta miki
Ya Allah ka bawa mataye ikon yin biyayya ga mazajensu domin samun gwagwgwaban lada.
Friday, 25 January 2019
SHAWARWARI 52 ZUWA GA MATAN AURE, ZAWARAWA DA 'YAN MATA - SIFFOFIN UWA TAGARI 10
Shakka babu, a wannan zamani
'yan mata da zawarawa kai harma da matan aure suna cikin zullumi da tsoro da
rashin kwanciyar hankali, saboda yadda auren su yake yawan mutuwa, bayan kuma,
an dauki dogon lokaci ana soyayya a tsakani, kafin a yi auren. Ga wasu shawarwari
40 wadanda idan matan suka yi la'akari da amfani da su da yardar ALLAH za'a
samu kyautatuwar zaman aure.
1. Aurenki ya zama domin neman
yardar ALLAh kikayi ba dan tara abin duniya ba.
2. Kada ki zama mai kwadayi
wajen zaben mijin Aure.
3. Ki zabawa 'ya 'yanki uba ta
hanyar Auren wanda ki ka yarda da addininsa da dabi'unsa harma da
dangantakarsa.
4. Ki zama mai hakuri da
halayyar mijinki.
5. Ki zama mai matukar biyayya
ga mijinki.
6. Ki zama kin iya barkwancin
magana wajen baiwa mijinki dariya.
7. Kada ki zama mai rainuwa a
cikin duk abinda mijinki ya baki.
8. Ki dinga wanke bakinki da
safe da yamma da kuma lokacin kwanciya barci.
9. ki zama mai tsaftar jikinki,
gidanki, abincinki, da sauransu.
10.Ki dinga girmama Iyayan
mijinki da 'yan uwansa da abokansa.
11.Kada ki zama mai satar kayan
mijinki.
12.Kada ki zama mai satar fita
unguwa.
13.Ki guji Leke a gidan
mijinki, dan yana daga cikin abinda yake raba Aure a tsakanin Hausawa.
14.Ki dinga godewa mijinki a
cikin abinda ya baki.
15.ki kiyaye abinda mijinki ya
fi so.
16.ki kiyaye abinda mijinki ya
fi sonci da safe, rana, dakuma dare.
17.Ki dinga yabawa mijinki
kwalliyarsa.
18.Ki dinga yawan neman
shawarar mijinki akan duk wani al'amari da zaki yi.
19.Kiyi kwalliya ki tsane tsaf
kafin dawowar mijinki.
20.Lallai ki yi kokarin gama aikace-aikacenki
kafin dawowar mijinki.
21.Kada ki bari mijinki ya dawo
ya sameki gaja-gaja, ki sani kazanta tana haifar da kiyayya.
22.Ki zama mai yawan canza
zanen kunshin kafarki da kuma zanen kitso.
23.Kada ki ce mijinki sai ya
saya miki abinda ba shida ikon saye.
24.Lallai ki yi amfani da ilimi
wajen yanke dukkan wani hukunci.
25.Ki yi shiru a duk lokacin da
mijinki yake yi miki fada ko Nasiha.
26.Kada ki zama Al-mubazzara
mara tattali.
27.Kada ki tara kayan wanki da
yawa a daki, naki ko na mijinki suna wari.
28.Ki kula da yanayin da zai
nuna miki cewa mijinki yana cikin Nishadi ko Damuwa.
29.Kada ki ringa baiwa
kawayanki labarin sirrin dake tsakaninki da mijinki.
30.Idan zaki yiwa mijinki
magana kiyi masa da tattaunsan harshe, da murya mai karya zukata.
31.Idan kika samu sabani da mijinki
ki bashi hakuri ko da kuwa kece da gaskiya.
32.Ki zama mai tattali a cikin
dukkan abinda kika mallaka a gidan mijinki.
33.Kada ki zama mai yin dare
wajan girki.
34.kada ki zama mai yawan fada
da makwabtanki.
35.Kada ki kasance mai yawan
zagi ko Ashariya.
36.Kada ki ringa baiwa Iyayanki
Labarin laifin da mijinki yake miki.
37.Ki zama mai hakuri da juriya
da halayyar Iyayan mijinki da 'yan uwansa.
38.Kada ki ringa daga murya
sama idan kuna sa-in-sa da mijinki.
39.Kada ki ringa baiwa 'yan
uwan mijinki labarin laifukansa.
40.kada ki ci wani abu da
mijinki baya son warinsa misali tafarnuwa.
Allah ya bada iko wajen kamanta da aiki da shawarwarin.
Allah ya bada iko wajen kamanta da aiki da shawarwarin.
NASIHA ZUWA GA MATAN AURE - SIFFOFIN UWA TAGARI 9
NASIHA ZUWA GA MATAN AURE
Ki kasance mai yi wa Allah biyayya a bayyane da boye, shi zai hana miki cutar da wadanda kike tare da su, mutane ne ko dabbobi, ki sanya wadannan sunaye hudu na Allah a tare dake koda yaushe, su ne kamar haka: “Assamii’u – Albasiiru – Al’aliimu – Alqadiiru”. Idan ki ka sa wadannan sunaye a gaba gare ki, to zaki rabauta a duniya da lahira, domin zaki bauta ma Allah kamar kina ganinsa.
Ki kasance mai gudun duniya kada ki qwallafa wa kanki wannan duniyar, domin ida ki ka lura da ita, za ki ga cewa masu wadatar cikinta mafiya yawa ba su samun wadatar sai bayan shekara ar’abin ko makamancin haka, sai mutuwa ta dinfare su. Wadanda kuma suka same ta a lokacin quruciya sai ka ga nan da nan mutuwa ta zo masu. Amma idan ki ka guji duniya, ki ka fuskanci lahira, sai ki ga kwanakinki sun zo maki a cikin sauqi.
Ki kasance mai qanqan da kai ba mai alfahari ba, domin ki sani duk inda ki ka kai wajen wadata ko mulki akwai wacce ta fi ki, domin mafiya yawan mata akwai su da ji – ji da kai da taqama, kuma wannan ba dabi’a ba ce mai kyau.
Ki nisanci kwalliya da sanya turare yayin fita, ba ina nufin kada ki yi tsafta yayin fita ba, a’a, a yau mafi yawancin mata idan za su fita unguwa ko asibiti ko gidan suna su ci kwalliya suna bayyana adonsu, koda ko sun sanya hijabi har qasa sun sanya niqabi. Za ki gan su sun bayyana adonsu ta wurare da dama; ta wajen idanunwansu, da daurin niqabansu, da hannayensu, da qafafuwansu, tare da cewa sun kulle jikinsu duka, saboda haka ki kasance mai tsafta koda yaushe, amma ki nisanci bayyana ado yayin fita, domin wannan shi ne zama lafiya gareki.
Ki yi amfani da lokacinki wajen abin da zai amfane ki duniya da lahira, ta hanyar karatun alqur’ani, zuwa makaranta, sannan ki nisanci gulma, hirar banza, yawan surutu da dai sauran su, domin wadannan abubuwan baza su Haifa maki da mai ido ba. Kiyi amfani da lokacin ki wajen abin da zai amfane ki ya kusantar dake zuwa ga Allah.
Ki zamanto mai qarancin Magana ba mai yawan surutu ba, ki zamanto babu wata kalma da za ta fita daga bakinki sai alheri, kada a ji maganganun banza a bakin ki.
SAKO ZUWA GAREKU MATAN AURE - SIFFOFIN UWA TAGARI 8
Aure dai sunna ne na manzon
Allah S.A.W, don haka a kowace sunna akwai lada matukar dai an yi ta kamar
yadda manzon Allah S.A.W ya koyar. Don haka shi ma aure yana da nashi ladan
idan aka yi shi kamar yadda Manzon Allah S.A.W ya koyar. Manzon Allah S.A.W ya
yi bayanin irin ladan da ya kamata mace ta samu wajen biyayyan ta ga mijinta. Duk
matar da take kyautata ma mijinta, tana faranta masa rai, tana kwantar masa da
hankali, tana taya shi farin ciki a lokacin farin ciki, ta kuma taya shi bakin
ciki a lokacin bakin ciki. To babu shakka itama xata ga farin ciki a duniya da
lahira, Allah ya sa mu dace, amin.
Ya zo a cikin hadisin
AbdurRahman Bn Auf, Allah ya kara masa yarda inda yake cewa Manzon Allah SAW ya
ce "idan mace ta yi sallar ta guda biyar, kuma ta azimci azimin watan
Ramadana, kuma ta kama kanta daga zina, kuma ta yi wa mijinta biyayya. A ranar
lahira za a ce mata ki shiga aljanna ta kofar da kike so. Imamu Ahmad ya
ruwaito wannan hadisi, kuma Albani ya inganta shi acikin SAHIHUT-TARGIB. Don
haka ya kamata matan aure su kula da yin biyayya ga mazajensu. Akwai wata mata
da mijinta ke bada labari: yace wata rana ya bar Abuja inda yake aiki zuwa
Kaduna inda iyalinsa suke, koda ya zo sai ya kunna fanka don ya sha iska, har
bacci ya dauke shi, sai aka dauke wuta, matarsa na ganin haka sai kawai ta
dauko kujera da mafici ta zauna kusa da mijin tana masa fifita har sai da gari
ya waye.
Da aka kira sallah sai ta
tashe shi domin ya yi sallah, da ya ganta a zaune sai ya tambaye ta me ya faru
take zaune kusa da shi? Sai ta ce masa ai yana kwanciya sai aka dauke wuta, don
haka ita kuma tunda a wajen nemo masu abinci ne ya gaji, kuma gashi yana so ya
yi barci amma zafi ya hana shi, to bari ita ta bar nata barcin don shi ya samu
ya yi barci. Allah ya yi ma wannan mata albarka, Allah ya baku ikon yin koyi da
ita. Dan duk matar da mijinta ya shede ta akan wani abin kirki, to lallai Allah
ma zai yabe ta. Allah kasa ku kasance cikin mataye nagari. Amin.
Sunday, 11 March 2018
SIFFOFIN UWA TAGARI 7
KYAUTATA ZAMANTAKEWAR AURE BA TARE DA ZUWA WAJEN BOKA KO DAN DUBA BA.
Ki
sani ya `yar uwata, akwai hanyoyi da dama da mace za ta bi, domin ta kyautata
zamantakewarta ba tare da zuwa wajen boka ko dan duba ba. Ki sani yake `yar
uwa, idan ki ka gyara zamantakewarki zaki samu rabon duniya da na lahira, shi
ko boka ba shi da abin da zai qare ki da shi a gurin Allah, shin me ya sa ba za
ki tsaya ki lura da kyau ba, ki san cewa boka babu abin da yake yi face ya yi
sanadin da zai rarrabe kawunan mutane, babu abin da yake yi face ya shiga
tsakanin mata da miji, boka babu abin da yake yi face ya raba ki da dukiyarki
idan kin yi ganganci har da Imaninki, ya sa ki sami zunubi mai girma, shin, me
ya sa ba zaki tsaya a tafarkin Allah ba, ki yi rayuwar aure mai kyau, wanda
muka koya daga koyarwar Annabinmu Muhammad (Sallallahu Alaihi Wasallam) da
sahabbansa, da muminai baki daya. Domin hadisin Manzon Allah (Sallallahu Alaihi
Wasallam) yana cewa: “Lalle Allah madaukakin sarki yana cewa ranar alqiyama,
ina masu soyayya don neman yardata, a yau zan sanya su cikin inuwata, ranar da
babu wata inuwa sai inuwata”. Shin `yar uwa ba za ki tsaya a tafarkin Allah ku
yi soyayya don Allah ba? Kin je wurin boka idan da gangan ne, kin zama kafira,
kin zama mushrika, kin zama `yar wuta, subhanallahi. Haqiqa `yar`uwa idan ki ka
tsaya ki ka lura da kyau, zaki gane cewa boka da dan duba ba su amfana ma kowa
da wani abu, face su raba mutane da dukiyarsu da imaninsu ga wanda ya yi
ganganci, domin hadisin manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) yana cewa: “Duk
wanda ya je gurin boka da dan duba ya gasgata abin da yake fada, haqiqa ya
kafirce wa abin da Manzo ya zo da shi”. Boka ba ya iya cecen mutum a lahira, ba
zai iya cecen ki ba, Idan ya ga za a sanya ki a wuta, ba shi da wani amfani a
duniya da lahira, boka ya zama shahararren me hada fitina da husuma a tsakanin
mutane, domin Alqur’ani mai girma yana fada mana cewa; “…shaidanu su ne
kafirai, suna karantar da mutane sihiri… kuma ba su sanar da kowa ba, face su
ce lalle mu fitina ne a gare ku, kada ku kafirta, suna neman ilimin abin da ke
rarrabe tsakanin miji da matarsa…”. Saboda haka wannan ya sa mai sihiri ba shi
da wani rabo a lahira alhali yana sane, kuma tir da abin da suka sayar da
rayukansu da shi, alhali suna sane. Shaidan shi ne dukkan wanda ya san gaskiya
kuma ya qi yin aiki da ita, mutum ne ko aljan. Haqiqa `yar uwa ki lura, ki
fahimci abubuwan da za lissafa, zaki samu ki gyara zamantakewarki ba tare da
zuwa wajen boka ko dan duba ba, domin ba zasu amfane ki da wani abu a wurin
Allah ba.
Abu
na farko, shi ne girmama mai gida, haqiqa girmama mai gida yana da matuqar
muhimmanci, ki yarda cewa mai gida yana da wani matsayin da zai sa ki abu, ki
yi, kuma zaki girmama shi, ki dinga ba shi matsayi da girma a matsayin mijinki,
amma yanzu wasu matan ba su gane ba, sun dauka cewa idan suka je wurin boka ya
mallake masu mai gidan, ya zama na sai dai ta ba shi umarni, ya bi, shi ne
matar, ba mijin ba, ya zama kamar yaronta, wai tana ganin kamar ta birge, ita
ce wadda ta yi sa’a, to wallahi ba haka ba ne, Abu na biyu shi ne mace ta
kasance mai lura da tarbiyyar `ya`ya lura da tarbiyyan yara, ya kan sa namiji
ya qara son mace domin tana kula mashi da `ya`ya, yadda ya kamata, koda ba ita
ta haife su ba, da sun wuce a dinga shi mata albarka, ana cewa kalli yarannan
yadda aka yi tarbiyyarsu, kuma abin mamaki ba `ya`yan ta ba ne, riqo ta yi, amma
ta ba su kulawa mai kyau, ki zama kowa na miki addu’a sabo da wannan, inko
`ya`yanki ne, su zama abin kwatance a cikin al’umma, a dinga cewa kalli
`ya`yannan ba ruwansu da shaye – shayen banza, da duk dabi’un banza, duk dabi’u
na banza basa yi. Amma wannan ya gagara, kun kasa ganewa ku mata, haqiqa na
miji ba ya so a ce `ya`yansa sun zama na banza koda shi din na banza ne, ya fi
so a ce ga `ya`yansa sun samu tarbiyya mai kyau, iyaye mata da dama su suke
koya ma `ya`yansu dabi’u na banza, misali sai ku ga ana fada da mahaifiya a
cikin gida, sai ta je ta dauko `ya`yanta, wai su rama mata, ba za ta nuna wa
`ya`yan cewa su ma mutanen gidan na da girma da daraja ba, koda an taba ta, sai
ta yi haquri ta nuna wa `yarta, ta saba da haquri, amma a’a, ko da `yarta aka
taba, sai ta yi ta masifa wai ita an taba mata yarinya, sai ku ga yara sun taso
ba abin da suke yi sai rashin kunya, su taso cikin rashin kunya, su taso ciki
rashin tarbiyya, su taso a wulaqance, babu mai cewa su bari, abin haushi abin
takaici wai sai ku ga iyaye an taso sun zo gurin malamin Islamiyya, sun zo
tambayan dalilin da ya doki yaro, kuma zaku ga yawancin masu yin haka iyaye
mata ne, idan malami ya yi Magana su ce su sun san zafin haihuwa, shin wane
irin wulaqanci ne wannan? Kuma idan kuka bibiya zaku ga yaran ne keda laifi,
domin wasu yaran yadda suka taso cikin rashin kunya idan sun je makarnata haka
suke yi, kuma iyaye sun fi yin haka a makarantun Islamiyya, basa zuwa
makarantun boko idan an taba `ya`yansu, in banda rashin tunani, ta yaya wanda
ya karantar da danki yadda zai bauta ma Allah, amma shi ne idan ya daki danki
ko `yarki zaki sanyo hijabi ki taho wai kin zo ganin malamin da ya taba maki
yaro, Wal’iyazu billah
Thursday, 25 January 2018
SIFFOFIN UWA TAGARI 6
TAKA CECIYAR NASIHA
==> karki
nemo kowa wurin warware matsala tsakaninki da mijinki, ku warware ku biyu ba
tare da wadansu sunji ba, koda iyayen ku ne.
==> Karki
sashi abinda bai da ikon yinsa.
==>Karki
zauna a gidansa da kazanta.
==> Karki
manta da bukatun mijinki.
==> Karki
zagesa don yana da wani matsala.
==> Karki
bari wani ko wata su shigo masa gida batare da izininsa ba.
==> Karkiyi
masa gori akan taimakonsa da kike yi.
==>Karki ki
yafe masa akan laifin da yayi miki.
==> Karki
dauka fansa akan abinda yayi miki kice sai kin rama.
==> Karki
tona masa asiri a wurin yan’uwansa da koma waye.
==> Karki
ringa kawar dashi akan bin Allah da Mazonsa (S.A.W).
==> Karki
dauki iyayensa a matsayin iyayen miji ki daukesu a matsayin kema iyayenki ne.
==> Karki
dauki ‘yan uwansa a matsayin yan’uwan miji ki daukesu a matsayin kema yan’uwanki
ne.
Da fatana Allah
(S.W.T) ya bada zaman lafiya tsakaninku da mazajenku Ameen.
Monday, 27 November 2017
SIFFOFIN UWA TAGARI 5
LALLE
Yar’uwata ki sani lalle kwalliyace ga duk ya mace kuma mace idan ta bar hannunta ko kafarta ba lalle to ba’a iya banbance ta da namiji. Kuma kowace irin kalan lalle da mata sukeyi kema kiyi da zaran ya goge sai ki biyoshi da wani kala domin cika siffarki ta ya mace.
BANGAREN ADO
Yar uwa ki sani kirkire kirkiren adon zamani wajibine akanki a gidan mijinki harma da irin naki salon adon, kuma duk wata dressing da mata sukeyi a duniya dolene ki rinka yiwa mijinki matukar bai sabawa addinin musulunci ba, sannan kiyi masa ado da duk irin kayan da kika mallaka.
KISISINA DA KARERAYA
Ya yar’uwata mace bata cika mace ba idan bata iya kisisina irin ta mata ba, kamar su kareraya, yanga da rigima. Kuma ki sani irin wadannan dabi’un su suke daukaka martabar mace a wurin mijinta acikin dukkan alamuran su, Magana ko tafiya ko kallo da makamantansu.
DAMUWA DA DAMUWARSA
Yar uwa wajibine ki karanci halin mijinki sosai kisan mijinki acikin halin farin ciki da kuma bakin ciki kuma ki lura da yanayin sa a lokuta kamar haka:
ร Lokacin fita nema
ร Lokacin dawowa daga nema
ร Lokacin gajiya
ร Lokacin farin ciki
ร Lokacin bakin ciki
ร LOKACIN FITA NEMA: A wannan lokaci yar’uwata ki sani dolene ki tabbata mijinki ya fita daga gida cikin kwanciyan hankali da natsuwa. Akwai wani dabi’a da matan magabata sukeyiwa mazajensu, su kan shirya bayan sunyi wanka da kwalliya sannan sai su raka mazan su har kofar gida ko kofar daki, sannan suna tafiya suna taku daddaya da rangwadi kuma su kan yimusu addu’a sannan su basu wasiyan cewa idan Allah yasa ka samu halal ka kawo mana, idan kuwa baka samu ba zamuyi hakuri da azabar yunwa akan azabar Allah. Bayan ya fita yayi nisa sai ki kirashi da wani sunan soyayya mai dadi sai kiyi masa Kiss da hannunki. Sai kice masa Allah ya bada sa’a. Allah ya sa mudace Ameen.
ร LOKACIN DAWOWA DAGA NEMA: Ki sani yar’uwata miji yana dawowa gida a halin gajiya kafin ya dawo kin shirya ma dawowarsa.
ร LOKACIN GAJIYA: A wanna lokaci ki sani zaki nemi ruwa mai dumi a lokacin sanyi idan kuma lokacin zafine, sai kinemo ruwan sanyi ki kai masa wurin wanka bayan ya gama wankan ya dawo daki ki bashi abinci
ร LOKACIN FARIN CIKI: Yar’uwata a wannan lokacine zaki baje kolin shagwabar ki da rungumarsa
ร LOKACIN BAKINCIKI: Yar’uwata a wannan hali babu wasa babu tsokana a tsakaninku har sai kinji mai ya bata masa rai, idan ya fita bai samo bane sai ki kwantar masa da hankali, sai ki nuna masa kullum Allah yana basa sai kawai don yau baka samo ba sai muyi hakuri mu godewa Allah. Idan kuwa wani ne ya bata masa rai, sai ki bashi hakuri da kuma kwantar masa da hankali, sannan idan ya dawo miki cikin tashin hankali sai ki warware masa bayan kinji mai ya faru dashi. Idan ba zaki iya warware masa ba sai ki kaishi inda za’a warware masa damuwarsa.
1. MACE TAGARI ITACE WACCE IDAN MIJINTA YAYI RANTSUWA AKANTA ZATA BARRANTAR DASHI: Yar’uwata ki sani wajibine idan mijinki yayi miki rantsuwa sai ki barrantar dashi misali idan yace wallahi yau sai kin yafe min laifin da nayi miki, kawai sai ki yafe masa don ki barrantar dashi.
2. MACE TAGARI ITACE WACCE IDAN MIJINTA BAYANAN KOKUMA YAYI TAFIYA SAI TA KIYAYE KANTA KUMA TA KIYAYE DUKIYARSA: Yar’uwata ki sani idan mijinki bayanan dolene ki kiyaye kanki da dukiyarsa, kuma karki yarda ki nuna adonki ko kwalliyarki ma wani kuma karkiyi almubazarranci da dukiyarsa. To yar’uwata idan kika cika wadannan sharuda wallahi kin zama mace ta gari injin Manzon Allah (S.A.W). da fatan Allah (S.W.T) ya baki ikon cika wadannan sharuda Ameen.
1. MACE TAGARI ITACE WACCE IDAN MIJINTA YAYI RANTSUWA AKANTA ZATA BARRANTAR DASHI: Yar’uwata ki sani wajibine idan mijinki yayi miki rantsuwa sai ki barrantar dashi misali idan yace wallahi yau sai kin yafe min laifin da nayi miki, kawai sai ki yafe masa don ki barrantar dashi.
2. MACE TAGARI ITACE WACCE IDAN MIJINTA BAYANAN KOKUMA YAYI TAFIYA SAI TA KIYAYE KANTA KUMA TA KIYAYE DUKIYARSA: Yar’uwata ki sani idan mijinki bayanan dolene ki kiyaye kanki da dukiyarsa, kuma karki yarda ki nuna adonki ko kwalliyarki ma wani kuma karkiyi almubazarranci da dukiyarsa. To yar’uwata idan kika cika wadannan sharuda wallahi kin zama mace ta gari injin Manzon Allah (S.A.W). da fatan Allah (S.W.T) ya baki ikon cika wadannan sharuda Ameen.
Saturday, 18 November 2017
SIFFOFIN UWA TAGARI 4
SIFFOFIN MACE TA GARI
Yar uwa mai karatu ga kadan daga cikin siffofin mace ta gari, idan kuwa baki da wadannan siffofin, to sai ki rungumi wannan su zamo dabi’unki. Allah yasa mu dace Ameen
1. Itace idan mijinta yayi mata umurni zatayi masa biyayya.
2. Itace idan mijinta ya kalleta zata farantamasa rai.
3. Itace idan mijinta yayi rantsuwa akanta zata barrantar dashi.
4. Itace idan mijinta yayi tafiya zata kiyaye kanta da dukiyarsa
1. MACE TAGARI ITACE WACCE IDAN MIJINTA YAYI MATA UMURNI ZATA YI MASA BIYAYYA: Yake yar’uwata ki sani duk irin umurnin da mijinki yayi miki to wajibine kiyi masa biyayya matukar bai sabawa Allah ba. Kuma acikin kowani hali kika samu kanki ba tare da yamutsa fuska ba. Balle jan aji, kuma yar’uwa ki sani jan aji haramunne idan mijinki yayi miki umurni, wajibine ki zamo mai bin umurninsa. Allah ya baku ikon bin umurninsa Ameen.
2. MACE TAGARI ITACE IDAN MIJINTA YA KALLETA ZATA FARANTA MASA RAI: Ya yar’uwata mijinki ba zai taba kallonki har ki faranta masa rai ba, face kin dauwama a siffarki ta ya mace.
GA WASU DAGA CIKIN SIFFOFIN KAMAR HAKA KWALLIYA DA GAYE: Yar’uwata ki sani yana daga cikin asalin hallitar mace akai shine kwalliya, don haka ba’a son mace cikin sahun mata idan batayin kwalliya, anan wajibine ki kasance zinariya a gidan mijinki ko wani lokaci da irin salon kwalliyan da zaki yiwa mijinki acikin lokuta guda hudu kamar haka:
i- LOKACIN SAFIYA: Yar’uwata bayan kinyi Sallah wajibine kiyi wanka kiyi kwalliya irin kwalliyar Amarci.
ii- BAYAN BREAK FAST: Idan kin gama wanke kwanukan da aka ci abinci kinyi shara sai kiyi wanka kiyi kwalliya, yar’uwata kar ki yarda mijinki ya dawo ya sameki a hargitse, kamar yadda wasu mata sukeyi, abin kunya wai suna da zanin zaman gida kuma suna da zanin fita anguwa, wallahi wannan mummunar dabiane a dena.
iii- BAYAN ABINCIN DARE: Yake yar’uwata anan ma ya zama dole ne kiyi masa kwalliya irinta zamani wadda zaki kayatar dashi.
iv- LOKACIN BARCI: Yar’uwata anan kuma wajibine zaki yiwa mijin ki kwalliya da shara sharan kaya wadda zasu rikita mijinki.
do you want to learn how to blog and also make money online check this site
do you want to learn how to blog and also make money online check this site
Saturday, 11 November 2017
SIFFOFIN UWA TAGARI 3
MACE TAGARI
Mace ta gari za a same ta da:
1.
KAMEWA:
Daga duk wani abu da zai sosa wa maigidan ta rai, a kanta ne ko gidansa ko
abincinsa da sauransu.
2.
GASKIYA: In za ta yi magana ba ta qarya, domin
samun riqe gidan gaba daya.
3.
AMINCEWA:
Duk abin da yake so ta yi ta amince, don yarda da cewa ba zai halakar da ita
ba, tana qaunarsa.
4.
TAWALU'U:
Ta qanqar da kai gare shi koda kuwa tana da ilimi, arziqi da shekaru sama da
shi, kamar dai Khadeejah R.A da Annabi (S.A.W)
5.
NATSUWA: Kar ta riqa tuno abubuwan da suka
gabata, kuma ta dena tsoron masu zuwa.
6.
KUNYA: Ta riqa jin kunya, wannan ado ne gare
ta, masamman in tana tare da mijinta a cikin jama'a, wannan zai qara masa kaunarta.
7.
KWANCIYAR HANKALI: Mantawa da matsalolin
rayuwa da qoqarin tura farin ciki ga mai gida koda suna cikin matsala.
8.
GODIYA: Duk abin da ya zo da shi a nuna masa
jin dadin zuwa da shi komai girmansa komai qanqantarsa.
9.
HAQURI: A
kan duk abin da zai bayyana daga miji (wannan ne kawai muka dauka alhali suna
da yawa)
10.
TSAYUWA
QYAM: A wajen bauta da qarfafa mijin da 'yayan su.
11.
AMANA: Ta
zama mai amana, kar ta yarda maigidan ta ya ga ha'incinta koda kuwa sau Daya
ne, ta riqa gaya masa abin da za ta yi domin maganin shedan.
Wadannan abubuwa guda 11 su suke nuna mace
nagari, dan uwana kada ka riqa binciken qyalqyal banza, ke ma yar uwa ki dai na
kallon kudi ki duba rayuwarki idan kin shiga gidansa, komai kudinsa in ba
kwanciyar hankali ba za ki ji dadinsu ba. Biyayya ga miji ba mai iya wa sai
mace ta tagari, da yawa mata suna so a ce su ne wadan da Annabi (S.A.W) ya
sifanta dinnan da (Nagari) sai dai biyayyar ce ta yi qaranci, ko za’a yi sai
dai a gabansa in ya matsa an watsar kenan.
Mace ta gari takan yi qoqarin ta zama wa mijinta aljannarsa ce, ba ta
son ta ga gazawarta a idanunsa, don haka takan yi farin ciki in taga
murmushinsa, takan damu matuqa in ta ga fushinsa ko da ba da ita yake ba, ba ta
jinkiri a wajen abinci, kuma ta iya dafawa ba tare da almubazzaranci ba, ita ce
amin taccen abokin shawararsa, mai iya riqe masa sirri, ba ta yarda wani ya
sani ko waye kuwa, sannan ga taimako.
do you want to learn how to blog and also make money online check this site
do you want to learn how to blog and also make money online check this site
Popular Posts
-
‘Hips’ 'Girmam Kugu' Girman kugun mace yana daya daga cikin abubuwan dake janyo sha'awa tare da tayar da hankalin maigida idan y...
-
Wallahi da ina karanta wannan labarin saura kiris hawaye su zubo mini wasu iyalaine talakawa a wani kauye cikin pakistan sunada 'Da nami...
-
TANA TARE DA NI... PAGE 76 BY MIEMIEBEE Hannunsu ta had’a tana murzawa a hankali, “I’m ready Habeebi.” Har yanzu ya kasa yarda, “Flower are...
-
TANA TARE DA NI... TANA TARE DA NI... PAGE 61 BY MIEMIEBEE ★‡★‡★‡ PRISON HOUSE MAIDUGURI, BORNO STATE. K’aramin gate ne ya bud’u...
-
SIFFOFIN MACE TA GARI Yar uwa mai karatu ga kadan daga cikin siffofin mace ta gari, idan kuwa baki da wadannan siffofin, to s...
-
______________ Sukumbiya Danye Me Kyau 1 Tattasai 2 Attaruhu 3 Cabbage Albasa 1 Curry Maggi Mai : Zaki Wanke Kifinki Da Lemon Tsami ...
-
TANA TARE DA NI... TANA TARE DA NI... PAGE 66 BY MIEMIEBEE Mutuwan zaune Fannah tayi bata tab’a tsammanin jin wad’annan dad’ad’d’...
-
[12/27/2016, 10:03 PM] ๐รbbรฅ-Gรฃรฑรข๐: ๐WAYE SANADI?๐ 9⃣1⃣ & 9⃣2⃣ ๐๐๐ ๐๐๐ ๐๐๐ ๐๐๐...
-
Assalamu Alaikum barkanmu da warhaka barkanmu da sake saduwa daku a cikin sabon shirin namu wadda yake zuwa muku kai tsaye daga shafin “Abba...
-
TANA TARE DA NI... TANA TARE DA NI... PAGE 36 BY MIEMIEBEE Duk ta gama tsorata ta d’au ko farkawa zeyi yako kama ta red handed, se taga kwan...

About Me
- Muhammad Abba Gana
- Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technology, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Sassa
- AMINAN JUNA
- BANA KAUNARKA HAUSA NOVEL
- DAN ALHAJI HAUSA NOVEL
- DILKA & HALWA
- DOMIN KE DA MIJINKI
- GUZIRI MAFI KYAWU
- HAUSA NOVELS
- INSIYA
- KAUNA CE SILA HAUSA NOVEL
- KUKAN KURCIYA
- MU DAUKI DARASI
- mu koyi sana'a
- MY kitchen
- NA DAINA SO HAUSA NOVEL
- RAYUWAN NIHILA
- rayuwar fauziya hausa novel
- SASHIN YAN UWA MATA
- siffofin uwa
- TSORATARWA.
- WAYE SANADI
