shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wanda aka fi sani da hausa novel wanda ni Muhammad abba gana nake rubutawa dan wayar tare da fadakarwa ga mutane a yanayin da muke ciki.

Friday 25 January 2019

NASIHA ZUWA GA MATAN AURE - SIFFOFIN UWA TAGARI 9

NASIHA ZUWA GA MATAN AURE - SIFFOFIN UWA TAGARI 9


NASIHA ZUWA GA MATAN AURE
Ki kasance mai yi wa Allah biyayya a bayyane da boye, shi zai hana miki cutar da wadanda kike tare da su, mutane ne ko dabbobi, ki sanya wadannan sunaye hudu na Allah a tare dake koda yaushe, su ne kamar haka: “Assamii’u – Albasiiru – Al’aliimu – Alqadiiru”. Idan ki ka sa wadannan sunaye a gaba gare ki, to zaki rabauta a duniya da lahira, domin zaki bauta ma Allah kamar kina ganinsa.
Ki kasance mai gudun duniya kada ki qwallafa wa kanki wannan duniyar, domin ida ki ka lura da ita, za ki ga cewa masu wadatar cikinta mafiya yawa ba su samun wadatar sai bayan shekara ar’abin ko makamancin haka, sai mutuwa ta dinfare su. Wadanda kuma suka same ta a lokacin quruciya sai ka ga nan da nan mutuwa ta zo masu. Amma idan ki ka guji duniya, ki ka fuskanci lahira, sai ki ga kwanakinki sun zo maki a cikin sauqi.
Ki kasance mai qanqan da kai ba mai alfahari ba, domin ki sani duk inda ki ka kai wajen wadata ko mulki akwai wacce ta fi ki, domin mafiya yawan mata akwai su da ji – ji da kai da taqama, kuma wannan ba dabi’a ba ce mai kyau.
Ki nisanci kwalliya da sanya turare yayin fita, ba ina nufin kada ki yi tsafta yayin fita ba, a’a, a yau mafi yawancin mata idan za su fita unguwa ko asibiti ko gidan suna su ci kwalliya suna bayyana adonsu, koda ko sun sanya hijabi har qasa sun sanya niqabi. Za ki gan su sun bayyana adonsu ta wurare da dama; ta wajen idanunwansu, da daurin niqabansu, da hannayensu, da qafafuwansu, tare da cewa sun kulle jikinsu duka, saboda haka ki kasance mai tsafta koda yaushe, amma ki nisanci bayyana ado yayin fita, domin wannan shi ne zama lafiya gareki.
Ki yi amfani da lokacinki wajen abin da zai amfane ki duniya da lahira, ta hanyar karatun alqur’ani, zuwa makaranta, sannan ki nisanci gulma, hirar banza, yawan surutu da dai sauran su, domin wadannan abubuwan baza su Haifa maki da mai ido ba. Kiyi amfani da lokacin ki wajen abin da zai amfane ki ya kusantar dake zuwa ga Allah.
Ki zamanto mai qarancin Magana ba mai yawan surutu ba, ki zamanto babu wata kalma da za ta fita daga bakinki sai alheri, kada a ji maganganun banza a bakin ki.
Share:

0 comments:

Post a Comment

pls drop down your comment......
dan Allah ku ajiye comment.

Tallata Kayanka

Guide Tricks Blog

Be With Me Technology

Popular Posts

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).