Wednesday, 30 December 2015
Tuesday, 29 December 2015
NA DAINA SO!! 6 & 7
NA DAINA SO!! 5
NA DAINA SO!! 4
Monday, 28 December 2015
NA DAINA SO!! 1-2 & 3
Sha'awar 6oye.
HAUWA-JIDDA***36 & 37 (KARSHE)
HAUWA-JIDDA***31-32-33-34 & 35
HAUWA-JIDDA***26-27-28-29 & 30
HAUWA-JIDDA***16-17-18-19-20-21-22-23-24 & 25
HAUWA-JIDDA***11-12-13-14 & 15
Sunday, 27 December 2015
HAUWA-JIDDA***10
HAUWA-JIDDA***9
HAUWA-JIDDA***8
HAUWA-JIDDA***6-7
Thursday, 24 December 2015
HAUWA-JIDDA***3-4 & 5
HAUWA-JIDDA***1 & 2
Friday, 18 December 2015
BAYANI AKAN WASA
BAYANI AKAN WASA
Malam yace:
ﻭﺍﻟﻌﺒﺚ
WAL ABATHU
««fassara»»
Dayin wasa
SHARHI
-------
Asalin wasa haramunne, don haka bai halatta ga
duk wani balagagge musulmi mai hankali yariqi
wasa abin yiba.
Domin UBANGIJI (S.W.T) yafada acikin
SURATUL MU'UMINUN
SHIN KUNA ZATON CEWA MUN HALICCE KUNE
DOMIN WASA ???
KO KUMA KUNA ZATON CEWA BAZAKU DAWO
IZUWA WAJEN MUBA ???
TO KUSANI ALLAH (S.W.T) SARKIN GASKIYA
YAFI KARFIN YA RIQEKU ABABEN WASA, DOMIN
SHI ALLAH NE NA GASKIYA WANDA BABU WANI
ALLAH SAIDAI SHI KADAI, SHINE KUMA
UBANGIJIN AL'ARSHI MAI GIRMA.
Saidai duk da haka malamai sunce shi wasa
yakasu kashi biyu:
Kamar yadda aka rawaito hadisi daga KHALID BN
ZAID (R.A) yadda yake cewa:
Babu wani wasa daya halatta sai wasanni guda
uku sune kamar haka:
1- Wasan da mutum zaiyi da iyalinsa.
2- Wasan da mutum zaiyi domin ya horar da
dokinsa.
3- Harbe-harbe ko guje-guje (tsere) domin koyar
yaqi.
Imam Ahmad da tirmizy da Nasa'I da Hakim suka
rawaito.
Darasi mai zuwa zanci gaba.
Insha Allah.
Allah yabamu ikon yin aiki da abinda muke
karantawa.
KAUNA CE SILA**2***57 (KARSHE)
KAUNA CE SILA
57
MUHD-ABBA~GANA
A zaune nake ina ta yan danne danne waya ina kuma sauraron shigowar sakonnin mutane muna ta hira cikin nishadi kawayena can sai naga an min gausuwa wata sabuwar namba sai na dauko karanta waya ina ta duba lambar sai naga ashe zakiyyar yaya ce ai kuwa na mayar mata bayan mun gaisa sai nace mata ta bani pin dinta nafi yin BBM tace min to ta turo min bayan na tura shikenan muka zama kowa yana da kowa a cikin mutane n tsakanin da ita kenan bayan kwana kamar biyu sai yaya yayi min text ina dubawa ga abin da yake cewa I NEED YOUR PIN,
ALHAMDULILLAHI
muhadu a littafina kashi na uku 3 (karshe)
koh kuma na kan hanya mai suna
"NA DAINA SO!!"
naku har kullum har abada jikan marububuta: muhd Abba Gana(sharifin~Zamani)! For
correction and advice call me/ whatsapp me @ (09039016969)
Sadaukarwa: My sweet abunan (HAFSAT BALARABE)
wish you long life and prosperity,
GODIYA:godiya ta tabbata ga Allah madaukakin sarki da ya bani damar rubuta wannan littafi mai suna KAUNA CE SILA tsira da aminci su tabbata ga shugaban mu annabi muhammadu (SAW) da wa'ayanda suka bashi gaskiyar har izuwa ranar alkiyama
GAISUWA GA dukkan yan uwa musulmai maza da mata Allah ya hadu a aljanna LOVE YOU ALL
Jinjina gareku
members na::
-Duniyar marubuta
-novels!
-home of hausa novels
-best of hausa novels
-hausawan arewa
-rayuwan kwaraii
-sirrin zama da mace
-soyayya jigon rayuwa
-sirrinmu
-zumunchi
-takaicin rayuwa
-hausa literature
-hausa novels
-hausa novel books
da de wanda ban samu ikon lissafowa ba love u oll!
Ban manta daku ba members na groups dina
house of hausa novels (1, 2 & 3)
A karshe Allah yajikan
yan uwa musulmi
dasuka rigamu gidan gaskia! Love You all my well
wishers.
KAUNA CE SILA***2***56
KAUNA CE SILA
56
MUHD-ABBA~GANA
TO ni me zan ce maka sweet heart kake sona ce kome ina tura masa na tayar da sallar shafa'i da wutiri ina cikin yi kuwa sakon shi ya shigo ban duba ba har sai da na gama nayi shirin kwanciya nayi addu'oi na sai na fara karantawa: SUNANA AHMAD BA WANI SWEET HEART TUNDA AIKIN SAN HAKA AKA SAKA MIN bayan na karanta sai nace masa idan kuma ba zan ce ahmad din ba fa sai yace min sai na fadi abin da nake fada dana ce masa naji to dai a wannan dare munyi wa juna sakonni da yawa kamar bamu yi tsawon lokaci ba ma magana ba matsala ta shine son da nake yiwa yaya yayi min illa ba karama ba tunda kome yayi min in har zai kula ni to zam saka jiki da shimuyi yanda muka saba duk da abin yana raina amma yana min sako zan masa idan ma tambaya ta wani abu yayi to kuwa zan bashi amsa daidai da abin da ya tambaya na karbi sabuwar watar da nace a saida min BB ta zamani Allah ya sani makasudin yin wayar shine dan na dinga hira da kawaye na wa,ayanda mukayi garko tare da sauran su dai duk yawancinsu suna yi wasunsu kuma sunyi aure gaskiya a lokacin dasu kawai nake chatting tunda dama yaya ne ya sabar min hira ta waya to yanxu kuma ina sona dan ja baya tunda auren shi zaib yi saboda haka dole ne na koyawa kaina zama ba tare da shi ba kuma juriyar hakuri da rashinsa ranar wata juma,a ina zaune a gurin su yaya muna zaune ana ta hira sai ya shigo yayi sallama aka amsa bai zauna ba ya fita can ya dawo lokacin ina ta danna wayata ya shigo ya dauki abinda zai dauka ya fita ban kuma jin duniyar shi ba har na tafi gida ina alwalar magariba kawai ina shigowa naga yayi min text ina karantawa sai naga yana tambayata meye ya hadani da waya BB sai na ce masa ina chatting ne amma da kawaye na na makaranta nace masa ko babu kyau na daina sai yace a ,a ki daina nima dana taba yi na daina saboda bana so yin hira da sababbin mutane amma zan dawo dayi nima nace masa to nagode mukayi sallama.
www.abbagana.pun.bz
KAUNA CE SILA***2**51-52-53-54 & 55
[12/8, 8:13 AM] Ábbä~GåñāKAUNA CE SILA 51
MUHD-ABBA~GANA
Ai kuwa ina fitowa ban tsaya a wajen mu ba sai gurin su asma'u bayan mun gaisa na shiga bata labarin abubuwan da suka faru na kuma fada mata ni nace kar ya kara kulani sai kuwa ta rike kai sai kuma ta shiga tafa hannu haba mamaa me yasa kikayi haka kin san fa yana sonki kin san halin shi wani irin miskilin mutum ne kuma kowa ya san yanda yake wa yan mata wulakanci wallahi da baya kaunarki da tuni kema kin gane gashi kin san kaf mawakan nan namu mata bbu wadda yake mutuntawa irin ki kuma kema kin yi kuskure meye na cewa ya baki lambar wata bayan kin san zakiji haushi ai ni tunda nasan kana sona bbu ruwa na da wata na katse ta nace asma'u kin gama? tace na gama ai gaskiya nake fada miki na fara magana asma'u abin da yasa na nemi lambar ta saboda ya dameni da zancenta kuma ina so na tabbatar dan yana min wasa da hankali abu na biyu kuma ban so naci gaba da yaudarar kaina ne dan me zan ta batawa kaina lokaci da bata dare bayan kuma ga wata can ya ajiye zai aura ni bance dama ni budurwarsa bace amma me yasa yake nuna kulawar sa a kaina irin yadda saurayi ne ya kamata a ce yana wa budurwarsa sai tace ban gane ba nan kuwa na ciro wayata a cikin jaka na ce mata kinga na nuna mata gurin sako ba tare dana buda ba nace mata ai kin san lambar shi a haka zaki iya ganin su ba tare da kin bude ba ai kuwa tana ganin ta razana tace yanzu mamaa da ma wannan wayar shi ce nayi murmushi nace ni dai ki ga abin da nace miki tace lallai dole ki gigice irin wannan sakonnin haka ai zasu kai dubu nayi dariya nace mata dan Allah asma'u wanda yake min wannan ya ba zan so shi ba? ya ba zan dauka yana sona ba? ya ba zan dauka nafi kowa matsayi a gurinshi ba"
www.abbagana.pun.bz
[12/9, 7:50 AM] Ábbä~Gåñā: KAUNA CE SILA 52
MUHD-ABBA~GANA
TACE gaskiya kam nace ki dauka ma zagina yake a sakon nan ai kudin shine ko bare ma ba haka bane wataran dauka na yake kamar aminiyarsa to fi sabillilahi meye amfanin ci gaba da batawa kaina lokaci tace kin yi gaskiya amma ni bazan baki shawarar ki rabu da shi ba dan idan nice sai na dage na same shi tunda bbu laifi a ciki dan kayi yakin neman abin sonka nace ban gane ba me zanyi da ya wuce wanda nake yi tace addu'a in kina yiki kara dagewa na kalleta nace ban ga amfanin yin addu'ar samun shi ba bayan nasan ba sona yake yi ba zuciyarshi tana gurin wata can sai tace waye ya fada miki haka bayan duk alamomi sun nuna yana sonki kina bani mamaki kamar baki san halin shi ba nayi shiru kawai nace mata ba zan gane ba amma na gode da shawararki tashi ki rakani yau ba zan iya wuni anan ba dan ko ganin fuskarshi bana sonyi tace lallai abin naki babbane muka fito muna fitowa shi kuma yana gyara tsayuwar motarsa na hada rai na kawar da kai muka wuce gurin mu na karasa na nemi wani a kasan mu nace masa wayata zan siyar yace meyasa ga wayar ki mai kyau ga karko nace wata zan canja ai kana da blackberry ko yace eh wacce kike so nace voltouch yace kenan ciko zakiyi nace masa E ya nuna min wata fara mai kyau nace ya bari na gama zan kawo maka yace to ina hawa sama na fara goge sakonni shi ko karantawa bana yi sai da na goge dari takwas da wani abu nayi ajiyar zuciya nace gara na goge dan barin ku ma anan tashin hankaline,
www.abbagana.pun.bz
[12/9, 8:03 AM] ?Ábbä~Gåñā?: KAUNA CE SILA
53
MUHD-ABBA~GANA
NI kuma bana son abin da zai tuno min da shi lokaci da zan tafi gida na bashi wayar tawa nace masa ka ajiye wani sati in Allah ya yarda zan baka cikon yace Allah ya nuna mana nace amin na wuce ina zuwa gida na cire sim na jefa a can kasan akwatina na karshe na ajiye shi anan haka naci gaba da bawa kaina hakuri ina kuma addu'ar Allah ya bani dangana na kuma goge lambar amaryar tashi kamar yanda ya umarta ban kuma tunanin nemansa ba bare nace ina sakarai da sakonsa bayan kamar kwana biyu da misalin takwas da mintina na dare ina zaune sai naga wata lamba tana kirana bayan na daga sai aka cemin ina gajiya maryam ce nace oh ya garin tace lafiya ban ce komai ba sai tace ga ahmad dama ce miki zanyi gashi ku gaisa sai nace to na danyi shiru sai naji maganarsa kamar yana waya sai tace bara dan Allah ya gama waya yakeyi nace mata ki barshi kawai yace na daina kula shi idan ya tafi mayi magana tace mai yasake kuwa bata karasa ba na kashe wayata sai da na fuskanci kamar ya tafi dan sai dana bari goma ta dan gota kadan tana dauka tace min Dan Allah me yasa kika ki yarda kuyi magana dashi sai nace mata bbu komai ka bana so sai tace kin san meye nace mata a,a tace min kin sam ni fa kin taba yiwa sister ta wakar aure kawai ba zan tuna miki bane nace to meye dalili tace nima kawai nace mata to shikenan sai kuma tace min ina so mu hada kai dake mu kula da ahmad tunda nasan kina sonsa,
.
www.abbagana.pun.bz
[12/9, 8:20 AM] Ábbä~Gåñā: KAUNA CE SILA
54
MUHD-ABBA~GANA
A take naji wani takaici nace mata shi ne ya fada miki ni ke sonshi shi baya sona? sai tace a,a to ai da baya kulaki ya za ayi ki samu lamba ta kawai dai bana so naga mace tana son namiji sosai kuma bata sameshi ba sai nace mata ke ba kya sonshi kenan sai tace a,a ina sonshi amma ba zan bar miki shi ba sai dai ya hada mu nayi saurin tattarar numfashina nace to ni bana sonshi idan ma kina ganin da ina sonshi to yanzu a a sai tace ina da wayanda na sani haka suka yi tayi ni gaskiya ma saboda bacin ran da maryam ta jefa ni bana gane me take cewa sai da tace min kina tare kuwa da ni nace mata E ina jinki sai tace ahmad har fada mukayi yace wai bana kishinsa nace masa ba haka bane abin da dai na sani ahmad yana sona nace mata haka ne Allah ya tabbatar da alkairi tace amin na gode muna gamawa naji wani kuka yazo min tare da haushin shi mai tsanani wato ni ina nan ina kishinshi shi kuma yana can yana son wata in Allah ya yarda ko da zan kwanta ciwone tona hakura dashi in Allah ya yarda saboda takaicin da nake ciki washegari dana fita kawai sai na karbi kudin wayata yace min wadda kika ce kina so fa nace zanzo na siya kamar nan da sati biyu yayi dariya yace Allah ya nuna mana na fita na barshi a nan ranar haka na wuni kamar mara lafiya ina kuma taci gaba da jin haushin shi da muka hadu da asma,u na bata labari ita ma tace min kai kema dan Allah ki daina kiranta nace mata wallahi ita ta kirani da har na goge lambarta amma bbu abinda zai kara hada mu da ita bara na kirata a wayannan kwanaki na bawa kaina hakuri nayi juriya na kuma fuskanci rayuwa duk da bana jin dadin yanayin da muke ciki amma idan ka ganni ba zakace ina cikin damuwa ba,
www.abbagana.pun.bz
[12/10, 7:24 AM] ?Ábbä~Gåñā KAUNA CE SILA?
55
?MUHD-ABBA~GANA?
MUNA yawan haduwa ina yawan zuwa gurin su amma ko da na ganshi ko gaisuwa bata hadamu idan na ganshi sai dai na dauke kai mun kusa kai wata a haka dan munyi kamar kwana ashirin da bakwai wata rana da yamma nayi shirin tafiya gida asma,u ta tashi dan rakani muna fitowa sai muka hango shi zaune a inda suke zama amma yau shi kadaine a zaune sai asma,u ta ce min dan Allah ke kuwa kizo ki gaishe shi ko dazu sai da ya tambaye nikr haba ke kuwa nace mata ba zan jeba gaskiya tace dan Allah fana ce miki nace to muje muna zwa sai asma,u tace masa "farin doki sannu da hutawa sai ya kalle ta yace yawwa nima na san ana ce masa farin doki to amma ban taba kiran shi da haka ba ni kuwa jin ta fadi haka kuma dama dole tayi min nazo na gaida shi sai nima nace farin doki ina wuni sai ya kallleni a razane bai amsa ba naga yana girgiza kai kenan mamakin jin hakan yake daga bakina ganin bashi da niyyar amsawa sai naja hannun asma,u muka tafi muna tafiya muna dariyar abin da yayi ni kuwa ko kadan banji haushin kin amsawar saba duk kuma abin da nayi masa ina gida ina shirin shiga wanka zan kwanta sai naji an yi min text ban kawo komai ba tun da wayata ce ta amfanina da kowa yake kirana ina budewa sai naga lambar yaya nace kai to ya akayi yasan bana amfani da layin dana ware masa sai nace bari dai naga me yace min wai nan na fara karantawa kamar haka: BA SUNANA FARIN DOKI BA KARKI KARA KIRANA DA HAKA KI KIRANANI DA SUNAN DA BABANA YA RADA MIN ,dariya sosai nayi bayan da na gama karantawa na ajiye waya ta na wuce wanka ina tunanin me ya kamata na fada masa ne dana dawo sai na fara rubuta masa.
www.abbagana.pun.bz
KAUNA CE SILA**2**46-47-48-49 & 50
[12/5, 9:46 PM] Ábbä~Gåñā KAUNA CE SILA46
MUHD-ABBA~GANA
JIN haka sai nayi saurin barin gurin dan bana san ganinshi yau nayi tafiya ta sai da yamma naji ta kirani ina dagawa sai kuwa ta ce ke wallahi dariya kawai yake wai da gaske kinyi kuka nace eh sai yace Allah sarki kanwata kyale ta kawai karki damu nace mata umnm asma'u ba zaki gane ba nifa nasan da gaske yake amma shi kenan na gode mukayi sallama na kashe wayata wayar da muke tin text na kashe har washegari ina shirin fita sai wani ya kirani naxo na masa amshi amma a tukuntawa ina zuwa na fara kenan sai naji wayata tana kara ina dubawa sai naga lambar yaya naji gabana ya fadi kawai na daure nq daga ina dagawa naji yace kizo ki mana amshi ko ba zaki zo ba nace gani nan kawai na karasa na suri jakata na tafi ina zuwa na ganshi a waje suna magana da wasu ban masa magana ba nayi ciki sai na ciki yace bara na bude miki ki dan masa amshi ne da baiti biyu nace to bai shigo ba har na gama da yasan idan ya shigo ba lallai na iya ba ina gamawa sai asma'u tace bara na zo na baki labari nace ta taho ina jiranki tace ai dazu muna tare ya kiraki cewa yayi wai kina dagawa zai saka kuka yace mamaa niba zan iya rabuwa da ke ba nace to me yasa bai fada din ba sai tace to ba ke bace kina jin shi kawai kika kashe nace asma'u baza ki gane ba amma ba komai Allah ya zaba abinda yafi alkairi tace ameen nan dai muka yi ta yin hira har lokacin tafiyata gida yayi na tafi kawai sai na kunna wayar da muke yi sako to banga amfanin fushin da nake yi ba tunda bai ma san ina yi ba shi mara wayo ma ya maidani dan gashi ko a fuskarshi baya nuna komai gashi banji ana maganar bikin shi ba.
www.abbagana.pun.bz
[12/6, 8:51 AM] Ábbä~Gåñā: KAUNA CE SILA47
MUHD-ABBA~GANA
RANAR alhamis ne tun a gurin aiki naji wani zazzabi haka dai na karasa na tafi ina zuwa gida kuwa ya rufeni da daddare asma,u ta kirani tace yau baki zo ba nace eh a gurinmu na zauna zazzabi ne ya rufeni yanzu haka ma a cikin bargo nake tace Allah sarki Allah ya baki lafiya nace amin sai da safe washegari sai na tashi jikina babu dadi babu zazzabi amma idan na tashi zanji kamar zan fadi sai ina dafa bango sai na ba zan iya fita ba da yamma har nayi wanka dan na fara jin karfin jikina sai fa kiran asma,u tace min ya jikin nace da sauki tace ga ibrahim nayi dariya nace bashi shima duk a gurin su asma,u yake nayi musu godiya mukayi sallana bayan anyi sallar magariba ina kan sallaya naji shigowar sako nayi murmushi dan nasan ko dai yaya na ne ko kamfani dan bani da wanda yasan layuin ina budewa ai kuwa yaya ne ;: SALAM NAJI ANCE BAKI DA LAFIYA IDAN AURE NANE ZAI KWANTAR DA KE HAR KIYI CUTA TO KI TASHI NA FASA , ina gama karantawa nayi dariya nace yaya kenan kawai sai na fara rubuta masa sako kamar haka: DAMA JIYA NE NAJI SOSAI YAU DA SAUKI AMMA BAN IYA FITA BA BUT YAUNZU ALHAMDULLILAH NAJI SAUKI SOSAI NA GODE, A AI kuwa yana gani ya kara turo min wani kamar haka: AU SHIKENAN DAMA NA ZATA NINE NAJA MIKI RASHIN LAFIYA TUNDA BANI BANE ALLAH YA BAKI LAFIYA YA TASHI KAFADU sai nayi murmushi nace hmmmm! kamar yaya so ne yace shine silar cutata ko to ko da gaske zai iya fasawa saboda ni kawai sai na hau rubuta masa wani sakon
www.abbagana.pun.bz
[12/6, 9:58 AM] Ábbä~Gåñā: KAUNA CE SILA 48
MUHD-ABBA~GANA
GASKIYA ba kai bane amma ka yi contributing sosai dan kusan abin daya kwantar dani kenan sai yace min ai na riga naji kince bani bane saboda haka Allah ya baki lafiya yasa kaffara ce na ce masa ameen bayan kwana biyu na dawo daidai na ci gaba da fita sana,a ta ina kuma yin nishadi na kamar yanda na saba amma fa ina tuno zancen yaya zanji wata mummunar faduwar gaba kuma ina jin tsoron yi masa sako ranar nan na bar gurin aiki ina gida sai ga sakon shi GA BIKI FA YANA TA KARATOWA AMMA BANGA GUDUNMAWARKI KI BA LOKACI YA KUSA banji ji dadi ganin sakon sa ba amma ban isa na nuna ba sai na bashi amsa yaya wai dan Allah da gaske kake auren nan zakayi to maman junior ta amince? sai yace min shi da gaske yake mana kuma matar shi ai ba ita ce mijin ba shine saboda haka zan yi nace masa to Allah ya sanya alkairi ya zabi duk abinda yake so zan masa sai yace waka ma ta isa nace to shikenan bayan mun yi sallama haka na karasa wannan daren dauke da tunane tunane, babu abin da yafi damuna sai yanda mutane zasu yi ta min dariya gashi dai ni ba cewa nake yi soyyaya muke yi ba amma mutane da yawa suna cewa ai ina bala'in sonsa wasu ma cewa suke yi ina sonshi amma bai san ina yi ba to yanzu idan suka ji yayi aure ai wasu a gabana zasu fada a zuci nake wannan zancen a fili nace innalillahi Allah ka yaya min son wannan bawan naka kaji tausayina washegari haka na fita na ganshi ai kuwa muna hada ido na dauke kai na shige ciki ban kuma fitowa ba har sai da lokacin tafiya ta yayi na tafi haka dai a kwanakin muka dinga yin wasan buya dan bana bari ya ganni saboda ina ganin shi zan ji wani sabon sanshi kuma ina ganinshi zan ji hawaye mun kai kamar sati daya a haka watarana sai ya yo min sakon cewa biki nan ya kusa nace masa Allah ya kaimu sai kuma nace bara dai na kira mutumin nan naji wai shin da gaske yake ko dai zolayata yake yine? ban san lokacin dana fara neman layinsa ba ai kuwa ya daga nace dan Allah da gaske kake aure zakayi?
www.abbagana.pun.bz
[12/7, 5:09 PM] Ábbä~Gåñā KAUNA CE SILA 49
MUHD-ABBA~GANA
sai yace au kin dauka wasa ne? to da gaske nake ai ranan ma na hada su da asma,u ta waya sun gaisa hatana ce min wai asma'u tana da hankali nace dan dai waya ne daga nan ban kuma jin meye yake cewa ba dan duk na rikice nayi masa sallama na kashe wayata sai na kira asma'u na fara mata masifa wato har da gaisawa da amaryar yaya koni bance kinyi laifi ba da sai ki fada min ai tace wallahi bi ban san anyi ba wasa yake ni bai hada ni da kowa ta waya ba nace mata shi kenan sai mun hadu tace to nan mukayi sallama muka rabu ina hanya duk hakan ya faru har na karasa gida ina tunanin wannan abin mamakin da haushin ina gida har na kwanta duk da dai ban kwanta da shirin sai da safe ba amma na fara bacci sai naji shigowar sako waya ta na bude dan na karanta DA GASKE HAR YANZU KINA SO NA BAKI LAMBAR AMARYAR TAWA KO KIN FASA? ni ko ina karantawa nace masa ya turo min ina so nan take ya turo min naji wata muguwar fargaba nan nayi sauri na rubuta amarya sai ya ce min kuma wai na kira yanzu sai nace masa sai dai da safe dan har na fara bacci yanzu ma sakon sane ya tasheni ai kuwa sai yace to idan ba zan kira yanzu ba na barshi dan yace mata zan kira ta bance masa komai ba kawai sai na fara neman layin da ya turo min ban taba razana irin haka ba dan muryar mace naji kuma ban taba jin mai kama da muryar ba bare nace nasan mai muryar banji me ta fara cewa ba dan na tafi duniyar tunani sai naji tace ina gajiya ina jinki sai nace mata mamaa ce ban san me ya haddasa min rawar murya ba sai ji nayi tace a ina kika samu lambata.
www.abbagana.pun.bz
[12/7, 5:33 PM] Ábbä~Gåñā: KAUNA CE SILA50
MUHD-ABBA~GANA
sai nace mata dazun ne a studio naji yaya ahmad yana cewa zai kara aure sai na ce ya bani lambar amaryar na gaida ta sai naji tayi dariya tace Allah sarki na gode kece mai waka mu koh nace mata Eh tace ai nima zaki mana koh dan an kusa wata shekara wata na uku nace mata Allah ya nuna mana nace mata a ina kike ne tace a abuja nake zone 6 nace to na gode tace nima haka muna gamawa wani kuka ya zo min mai karfi nace na shiga uku innallilahi wa inna ilahi rajiun a take na dinga ganin wani duhu kai ni dai ina tunanin kiran sunan Allah da nayi shine ya takaita min abin da nake ji haka ban daina tsiyayar da zazzafen hawaye ba waya ta tana hannuna na fara rubuta masa sako da a yanxu bana sha yin komai ina DAN ALLAH DAN ANNABI DAGA YAU KAR KA KARA SHIGA HARKATA DAN ALLAH ko minti biyu bai yi ba dan yana gani ya turo min sako cikin dimauta ME YA FARU? dan haushin dana karanta ce masa nayi bbu komai kawai bana so kuma da gaske nake ganin haka shi ma sai ya ce min:NAJI IN ALLAH YA YARDA BA ZAN KUMA BA YANZU ZAN GOGE KOMAI DAYA SHAFEKI SANNAN KEMA KAR KI KARA KIRA MIN MATAFA, wani kunci ne naji yaxo min ba bacin raina da yace shima ya rabu da ni ba haushin na kalmar daya fada ta karshe matarsa yace gashi har da bani umarni ko gargadi nayi tsaki kawai na kashe wayata gaba daya washegari na tashi da wata shawara kamar wanda aka bani ita ina cikin bacci dan ina tashi na yanke shawarar na canja layukana gaba daya sai kuma wata zuciyar tace saboda mutum daya zaki daina mu'amala da mutanan arziki wani cewa ta zaiyi a bashi lambar ki kuma kowa ai ita yake da ita nayi ajiyar zuciya nace nasan abin da zanyi shi layin da muke turawa juna sakonni shi zan rufe sannan na siyar da wayar dan ko ganinta bana son yi,
www.abbagana.pun.bz
Popular Posts
-
Assalamu Alaikum barkanmu da warhaka barkanmu da sake saduwa daku a cikin sabon shirin namu wadda yake zuwa muku kai tsaye daga shafin “Abba...
-
TANA TARE DA NI... PAGE 76 BY MIEMIEBEE Hannunsu ta had’a tana murzawa a hankali, “I’m ready Habeebi.” Har yanzu ya kasa yarda, “Flower are...
-
TANA TARE DA NI... TANA TARE DA NI... PAGE 56 BY MIEMIEBEE Wani irin tausayin daya jima be mata irinsa ba ya soma jimata yau, azabarcaccen k...
-
[9:09PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA page 1 na BABY ZAHRA Kayatatciyar daki ne mai dauke da ko mai na more rayuwa, alarm ce ke bu...
-
TANA TARE DA NI... PAGE 89 BY MIEMIEBEE Daidai tashiwan Anas daga bacci kenan, da k’yar ya iya ya raba jikin Fannah da nasa dan wani s...
-
TANA TARE DA NI... PAGE 68 BY MIEMIEBEE Kasa koda amsashi tayi wani kunya taji ya rufeta, she can’t believe abinda ta aikata sede kuma ...
-
TANA TARE DA NI... PAGE 74 BY MIEMIEBEE D’ayan hannunsa ya aza a hab’arta tare da d’ago fuskartata. “Flower you don’t have to be sorry baki...
-
TANA TARE DA NI... TANA TARE DA NI... PAGE 61 BY MIEMIEBEE ★‡★‡★‡ PRISON HOUSE MAIDUGURI, BORNO STATE. K’aramin gate ne ya bud’u...
-
TANA TARE DA NI... PAGE 75 BY MIEMIEBEE Sede still bayason miyan kukan yafison ire-iren abincin daya saba ci a London su burger, pizza, buf...
-
TANA TARE DA NI... PAGE 01 BY MIEMIEBEE ANAS K’auyen Bama dake jihar Maiduguri, Borno. Da yammacin ranan Asab...
About Me
- Muhammad Abba Gana
- Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).
Blog Archive
-
▼
2015
(528)
-
▼
December
(41)
- NA DAINA SO!!***8 & 9
- NA DAINA SO!! 6 & 7
- NA DAINA SO!! 5
- NA DAINA SO!! 4
- NA DAINA SO!! 1-2 & 3
- Sha'awar 6oye.
- HAUWA-JIDDA***36 & 37 (KARSHE)
- HAUWA-JIDDA***31-32-33-34 & 35
- HAUWA-JIDDA***26-27-28-29 & 30
- HAUWA-JIDDA***16-17-18-19-20-21-22-23-24 & 25
- HAUWA-JIDDA***11-12-13-14 & 15
- HAUWA-JIDDA***10
- HAUWA-JIDDA***9
- HAUWA-JIDDA***8
- HAUWA-JIDDA***6-7
- HAUWA-JIDDA***3-4 & 5
- HAUWA-JIDDA***1 & 2
- BAYANI AKAN WASA
- KAUNA CE SILA**2***57 (KARSHE)
- KAUNA CE SILA***2***56
- KAUNA CE SILA***2**51-52-53-54 & 55
- KAUNA CE SILA**2**46-47-48-49 & 50
- KAUNA CE SILA***2***41-42-43-44 & 45
- KAUNA CE SILA***2***38-39 & 40
- KAUNA CE SILA***2***36 & 37
- KAUNA CE SILA****2***31-32-33-34 & 35
- KAUNA CE SILA**2**26-27-28-29 & 30
- KAUNA CE SILA***2****21-22-23-24 & 25
- KAUNA CE SILA****2***18-19 & 20
- KAUNA CE SILA***10----17
- KAUNA CE SILA***2****5-6-7-8 & 9
- CIKIN BAYANI AKAN HASSADA.
- ABUBUWAN DA AKA HARAMTA GA MAI JININ HAILA (2)
- ABUBUWAN DA AKA HARAMTA GA MAI JININ HAILA (1)
- KAUNA CE SILA***2****1-2-3 & 4
- KAUNA CE SILA***59 & 60 {karshe}
- KAUNA CE SILA***58
- KAUNA CE SILA***57
- KAUNA CE SILA***56
- KAUNA CE SILA***51__55
- KAUNA CE SILA*** 46__50
-
▼
December
(41)
Sassa
- AMINAN JUNA
- BANA KAUNARKA HAUSA NOVEL
- DAN ALHAJI HAUSA NOVEL
- DILKA & HALWA
- DOMIN KE DA MIJINKI
- GUZIRI MAFI KYAWU
- HAUSA NOVELS
- INSIYA
- KAUNA CE SILA HAUSA NOVEL
- KUKAN KURCIYA
- MU DAUKI DARASI
- mu koyi sana'a
- MY kitchen
- NA DAINA SO HAUSA NOVEL
- RAYUWAN NIHILA
- rayuwar fauziya hausa novel
- SASHIN YAN UWA MATA
- siffofin uwa
- TSORATARWA.
- WAYE SANADI