shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wanda aka fi sani da hausa novel wanda ni Muhammad abba gana nake rubutawa dan wayar tare da fadakarwa ga mutane a yanayin da muke ciki.

Friday 18 December 2015

KAUNA CE SILA***2***38-39 & 40

kauna-ce-sila.jpg

[12/1, 2:51 PM] Ábbä~Gåñā KAUNA CE SILA 38






MUHD-ABBA~GANA





TO IDAN MA YARINYAR AKA BANI ME YASA RANKI ZAI BACI BS KE TA FARA TAMBAYAR MEYE ALAKAR MU BA KIKA CE BABU KUMA DUK DA IRIN QUALITIES DIN DA TACE MIKI INA DA SHI.turrkashi ina ganin wannan sakon na ce shi kenan abin da nake tunani ya faru shi kenan idan ma ina tunanin ina da da gurbi a zuciyar yaya yanzu bbu ko kuma ya raba mama mu da yawa a take na yankewa kaina hukunci ni dai gara na hakura dan ba zan iya ja da su ba tunda su masu kudi ne ko bbu komai gidan su sannenne haka nayi ta tunani har na lallashi zuciyata na bar maganar kawai a wannan kwanakin na zama wani iri domin ko walwala na rage haka bana masa text shima baya min idan kuwa na ganshi sai na dauke kai dama bamu fiya hada ido ba dan kwarjini yake min watarana na fito ina yin amshi a gurin mu na gama amshi zan karasa sai naji wayata tana kara alamar ana kira kuma wayar da muke amfani da ita tare da shi ina dubawa ashe kuma shine na daga babu alamar fara,a fuskata yace min kizo ki min amshi ko ba zaki yi bane nace bara na zo sai kawai na kashe wayata a waddannan kwanaki babu wani shiri a tsakaninmu dan ko sakonshi nake gani bana bashi amsa mai dadi in da da mun fara zamu gama saboda yanxu ni ban jin dadin sakonshi nake ba domin a zuciyata ina ganin ba sona yake ba gara na daina yaudarar kaina muna cikin wannan yanayin ne wani al,amari ya faru na tashin hankali wanda ba zan taba mantawa ba da misalin biyu saura na rana na fito zan tafi daga vocal naji wayata tana kara ina dubawa sai naga ashe wani mawakine tijjani shima yafi zama a gurin su yaya ina dagawa naji yace kin san abin da ya faru nace a,a meye sai yace maryan ya rasu yanzu






www.abbagana.pun.bz
[12/1, 3:07 PM] Ábbä~Gåñā: KAUNA CE SILA39






MUHD-ABBA~GANA






NACE ME domin gaskiya ban gane me yake nufi ba sai yace yanzu na Allah ya karbi ran marwan yayi hatsari a titin gaba damu kadan a take nayi kasa na tsunguna dan idan ba haka ba faduwa zanyi nace innalillahi na shiga uku sai ya kashe wayar sa ni kuma kasa fita nayi gurin zama na nema na zaro wayata nayi wa yaya text yana karantawa sai ya kirani yace wai ya abun ya faru? nace hatsari sukayi shi da wani mai mashin yace to Allah ya gafarta masa yasa ya huta nace ameen yace ni gani ina kaduna kuma yanzu za a kai shi nace E haka Allah yaso muka yi sallama abin ne yake tayi min yawo a kaina dan jiya da shekaranjiya muna tare da shi yau dinma yace na kira shi zai zo nace to lallai rai ba a bakin komai yake ba kafin yamma zancen mutuwar marwan ta baza ko ina musamman a cikin masana'antar mu yayin da wasu ketayi min waya dan ta,aziya dan sanin irin alakarmu dashi ban bari lokacin tafiya ta yayi ba na tafi domin su manajan mu suna dawowa yace min an kaishi naji wani kuka yazo min nace shikenan yanzu? yace min addu,a zaki masa dan wallahi a gurin ma anayi masa wanka ana zancen ki dan kowa yace jiya ya ganki tare dashi nace hakane mun dade muna magana baka ji abinda ya fada min ba ashe wasiya ce na ce masa bara na tafi gida sai da safe yace to Allah ya kaimu sai hakuri haka na tafi gida bbu kuzari lokacin dana isa gida kasa yin komai nayi bayan nayi sallar isha,i na kwanta amma ba batun bacci dan yanxu duk maganganun da mukayi dashi jiya da shekaranjiya ne suke ta dawo min ina ta kallon lokacin da yanda muka rabu dashi sai kuma na tsinci kaina da cewa a fili yanxu marwan ya rasu Allah mai iko Allah mai iko





www.abbagana.pun.bz
[12/1, 4:45 PM] Ábbä~Gåñā: KAUNA CE SILA 40






MUHD-ABBA~GANA







ANA saura kwana biyu ya rasu muka hadu da yamma a wajen su yaya sai yace haba mamaa kwana biyu nace lafiya lau ai kaine ba a ganinka sai yace haba amma da har waya ma kina yi sai muka ji muryar asma,u tana tsonar mu to fa yanxu zaku fara turancin nan naku da anga marwan da mamaa to sai turanci muka yi dariya a tare yace rabu da ita asma,u ai ta yarda dani nace ni din wa? bara naje aiki zan dora yace nima CD dan karba to sai an jima sai mun hadu wani ikon Allah washegari ana gobe zai mutu kenan kamar wannan lokacin muka sake haduwa sai kawai naji ya riko jakata yace mama abin nan da kike yi bbu kyau wai meye duniya nan ne ma nace masa wai me kuma nayi yace kema kin sani sai tace to marwan yaya ne dama to ba zan iya ba kai yammata suna kawo maka abubuwa saboda shi niko me nake dashi? na hakura na barka dasu yita maka waya suna baka cin hanci sai yace haba mamaa ba haka bane dan Allah ki daina fadan haka ki daina yawan fushi babu komai a cikin duniyar nan nace masa to bara na tafi gidan suna zamu tafi ga hauwa can tana jirana yace muje na kaiku titi har muka kai titi irin maganganun da yake min kenan amma ban kawo komai ba duk da bai taba yi min irin wa,yannan maganganun ba lokacin da muka kai titi ya ce to sai kun dawo dan Allah yau ki kirani zan fada miki wani abu kinji.






www.abbagana.pun.bz
Share:

0 comments:

Post a Comment

pls drop down your comment......
dan Allah ku ajiye comment.

Tallata Kayanka

Guide Tricks Blog

Be With Me Technology

Popular Posts

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Blog Archive