shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wanda aka fi sani da hausa novel wanda ni Muhammad abba gana nake rubutawa dan wayar tare da fadakarwa ga mutane a yanayin da muke ciki.

Saturday 30 April 2016

WAYE SANADI?? 2

waye-sanadi.jpg

WAYE SANADI?

2

MUH'D*ABBA*GANA
09039016969

www.abbagana.pun.bz


in ka ganta cikin farin ciki to tana tare da mijinta ko kuma ta shiga cikin yan uwa kullum tana daki a takura dai dai da mahaifiyarta basa zuwa har tsahon wata bakwai yau ta fito tana faman kwara amai,hajiya saratu tana kicin tana hangenta tayi saurin fitowa tana kwallawa hahiya zuwaira kira tayi saurin fitowa suka tsaya akaina ke baki da lafiya kike kwara amai? suka yi min tambayar cikin tsawa nayi saurin dago kaina ina kwalla shegiya kin zuba mana ido kamar aljana muna tambayarki cikin sarkewar murya nace zuciyata ce take tashi inji dai naci abu sai ya dawo ba kuma bana jin dadin jikina to kin gayawa alhaji? na gigiza kai to bakar munafuka saura ki gaya masa wallahi sai mun yankaki (auxubillahi) ta juya tana kallon hajiya saratu kin san ba muga ta zama ba ki shirya mu fit ko masan mafita wani azababbin rankwashi naji a tsakiyat kaina kaune ki bamu waje makira bayan kwana biyu ina zaune a dakina naji muryar Alhaji yana kwallan kira da sauri na mike na fina yana tsaye sai faman huci yake na tsugun gaban alhaji gani" bai ce kala ba ya hurgun farar takarda jikina ta mace ki tashi ki tafi bana son ganinki takadar sakice,na sake ki saki uku fice min da gani" ina kuka na dago alhaji me ya faru wani abu nayi maka? get out yafada yana huci bana sonki,bana kaunarki bana kaunarki na sake ki bana son ganinki,tashi daga gabana ko nayi ball dake a,a alhaji hayaniyar me kuka wani abu tayi maka? zuwaira bana kaunar yarinyar ban ta bar gidan nan ya juyo yana kallona wallahi na baki mintu biyar in har baki fita ba sai na kira police sun fita dake ya juya ya koma dakinsa,to bakar ashana sai a mike a fita fidan nan yafi karfinki sai a koma tallar nono da fura ta juya ciki tana dariya ina kuka na koma dakina na hada kayan sawata da yan kudina na fito ina share idona nayi sa,a mai gadin baya nan ya tafi kai hajiya saratu unguwa na fita daga gidan ina fita daga layin na samu adai-daita sahu ban tsaya wani yin ciniki dashi ba na shiga muka tafi har cikin unguwarmu ya kaini na zaro kudi na miki masa hajiya nawa zan dauka? rike kawai nace da shi na shiga wajen mahaifiyata ina zuwa na fada jikinta ina kuka tana ta tambayar lafiya amma nayi shiru sai da nayi kuka na gaji sannan na gaya mata abin da ya faru to me abin kuka in dai kin san babu abinda ki kayi masa wallahi bbu abin da nayi masa to shi kenan"

MUHD*ABBA*GANA



Abbagana hausa novels @ facebook.
Share:

WAYE SANADI 1??

waye-sanadi.jpg

WAYE SANADI?

1


MUH'D*ABBA*GANA
09039016969

www.abbagana.pun.bz

Misalin karfe sha biyu na ranar lahadi mama ta nufi gidan alhaji mukhtar dake unguwar dorayi.Dan Allah malam ina son ganin mai gida hajiya zuwanki wajen nan uku yana kin fitowa ni gaskiya na gaji da zuwa kiranshi dan Allah.dana ka taimaka min wallahi in dai bai fito ba daga yau bazan kara zuwa ba yayi cikin gidan yana shiga can ya dawo kinyi sa'a yana zuwa to na gode nafi minti goma kan ya fito har nayi tunanin tafiya na hango fitowarsa yana cikin yana batsuwa ya karaso wajen.yau kuma da me kika zo? bbu abin da naxo maka dashi sai alkairi Alhaji ka dubi girman Allah ka tausayawa rayuwata rakiya kuma ka tuna kaunar da ka kewa rakiya har kai mata mugun sakamako kinfa malama ya isheki ni da kuke so ku cuceni ku batan suna ku zubar min da mutunci sannan ku raina hankali magajiya kar ki dauke ni wanda bai san me yake ba in baki sani ba ki sani in kuma kin manta in tuna miki ni din cikakken likita ne wanda yasan meye ke na riga na saki yarki ba aure a tsakaninmu sannan kizo min da batun tana da ciki har na tsawon wata uku yau duka rabuwarmu wata biyu ya akayi ciki a jikinta har na wata daya ban san dashi ba? to wallahi magaji yau shine maganata dake ta karshe duk ranar da kika kara zuwa nan gidan sai nasa police sun kameki maza ki fice daga nan yar ku taje tayi abin kunya ana so a likan daman can na aura bisa tsatsayi yanzu kuma Allah ya rabamu,kuke neman doran masifa ya juya ciki hajiya kiyi hakuri in har kuna da gaskiya komai daren dadewa zata bayyana na gode ta juya zata tafi ya zaro naira dari ya bata.WANE NE DR MUKHTAR?
Dr mukhtar isah, haifaffen garin kano ne cikin unguwar yakasai su hudu mahaifinsu suka haifa binta da lamratu sai kuma sadiya sannan shi dan auta dukan su sunyi aure har ma sun aurar da ya'yansu sun sami jikoki shi ka daine Allah bai bashi haihuwa ba Allah ya zuba masa son yaya yayi aure aure da dama duk dan ya samu haihuwa amma shiru yana zaune a dorayi da matansa biyu,hajiya zuwaira da hajiya saratu yana yawan karbar yayan yan uwansa ya rike amma rikon baya zuwa ko ina saboda makircin matansa ana cikin haka ya hadu da rakiya bafula ta nace suna zaune a fanshekara,a salinsu yan gongola ne rakiya yarinya kyakkyawa dr mukhtar ya nuna mata ra'ayinsa nasan ya aureta ka ba a sha wata wahala ba, ta amince nan da nan magana ta kankama har takai batun aure sai dai tun shigarta gidan bata taba farin ciki ba koda na minti daya ba,


MUHD*ABBA*GANA


Abbagana hausa novels @ facebook.
Share:

Wednesday 27 April 2016

Abubuwa uku

clean-flower.jpg

ABUBUWA GUDA UKU KADA KA RISKESU HAR SAI
KAYI TAMBAYA AKANSU.

by muhd abba gana

1- IBADA
2- MATA
3- AIKI.
Abubuwa Uku Baka Samun Sakat Har Sai Sun
Rabu Dakai
1- WAS-WASI
2- BASHI
3- MUGUN ABOKI.
Abubuwa Uku Da Baikamata A Jinkirta Su Ba.
1- WALIMA
2- TA'AZIYYA
3- SALLAR MAGARIBA.
Abubuwa Uku Allah Ka Tsaare Mu Dasu.
1- DAN HARAM wato dan cikin (Shege).
2- MAI YANKE ZUMUNTA
3- CIN DUKIYAR MARAYU.
Mutane Uku Karka Kuskura
Kayi Abota Dasu
1- WAWA
2- MAI KARANCIN HIMMA WAJEN IBADA.
3- MAI KARANCIN MUTUNCI.
Mutum Uku Kada Ka Saurari
Maganar Su.
1- MAKARYACI
2- MAGULMACI
3-MAI BAYAR DA SHAIDAR ZURR.
Mutum Uku Kar Kayi Abota Dasu
1- MAI HASSADA
2- MAI SA'IDO
3- MAI FUSHI DA MAHAIFANSA.
ALLAH YASA MU DACE KA DATAR DAMU GA
RAHAMARKA.
Wanda yakeda nasa abubuwa 3 shima zai iya
rubutawa saboda tunatar da yan uwa.

www.hanyantsira.mywapblog.com
Share:

SIRRIN ZAMA DA MIJI 9B

sirrin-zama-da-miji.jpg

SIRRIN ZAMA DA MIJI

{KASHINA 9}

(IYA MAGANA 2)


BY

MUHD*ABBA*GANA
09039016969

manzon Allah yana cewa mafi alherin aure shine auren da aka samu sauki a cikinsa koba komai dukkan iyayen da suke bukatar nemawa yayansu girma a idon mazajensu to sai ku kyautatawa mijinta tare da nuna mishi ai shima dansune don haka dole ne su kyautata masa. to amma abin haushi kuma abin takaici sai ya zama mafi mafi akasarin hankalin iyaye ya tafi a cikin sai an yiwa yayansh abinda zasuyi alfahari da shi kuma su burge koda kuma shi mijin zai shiga halin damuwa da takaici, wanda idan muka dubi koyarwar manzon Allah ya nuna cewa koda a cikin harkar saye da sayarwa Allah yana yin rahama da jin kai a gurin dan kasuwar da yake saukaka kayan siyarwarsa to ballantana ma a cikin sha,anin aure wanda yake duk wanda yace yana son yarka tofa baka da kamarsa a cikin masoyanka don haka shine mafi cancanta da a taimaka masa tare da yin agaji da tausayi a gare shi to amma abin mamaki sai yazo a halin da muke ciki yanzu babu abinda ake jira face sai wanda za,a dorawa nauyi. to jama a ya kamata mu riki koyarwar manzon Allah da kuma abinda zai janyo mana farin ciki da zaman lafiya da sukuni a tsakanin junanmu wannan shine zai taimaka izuwa dorewar zamantakewar aure. kuma ya kamata mu sani cewa shifa auren nan ibada ne bai dace ba a ce muna shigar da son zuciyarmu a cikin abin da Allah ne ya tsara ga yanda yake so aiwatar dashi. in da ace tsadar aure ko kuma tsadar tsadaki wani abin alherine ko kuma wata daraja ce a gurin Allah madaukakin sarki to da mafi cancantar wadanda ya kamata suyi hakan, to amma saiya zama a tsakaninsu bbu tsanantawa sai fa jin kai da tausayi da rahama a tsakaninsu. don haka idan har ba za mu iya yin yanda sukayi ba to sai mu kamanta domin mu samu kadan daga darajojin da suka samu. muna rokon Allah ya hadamu da mata ba gari wadanda zasu taimake mu domin cikar addinin mu ya Allah kayi a gaji ga dukkan matan da suke yin biyayya a gurin mazajensu da kuma wadanda suke taimakon mazajensu kafin na kammala wannan littafi ina sanar da dukkan madmsu sha'awar karanta littafina cewa ina masu albishir da fitowar sabon littafina mai suna "UWA TA GARI" muna rokn Aah yayi mana ludufi da kuma mafita a cikin dukkan al,amuranmu 'amin. NI MARUBUCIN WANNAN LITTAFI INA DADA YIWA ALLAH GODIYA DAYA BANI IKON KAMMALA WANNAN LITTAFI WANDA YA TATTARO MUHIMMAN DARUSA DA SUKA SHAFI RAYUWAR MA,AURATA MUSAMMAN YANDA YA KAMATA AMARYA TAYI MU'AMMALA DA MIJINTA A MUSULUNCI INA ROKON ALLAH YAYI MANA JAGORANCI A CIKIN DUKKAN AL,AMURANMU'AMEEN SUMMA AMEEN DAN UWANKU MUHD ABBA GANA
09039016969
Share:

SIRRIN ZAMA DA MIJI 9

sirrin-zama-da-miji.jpg

SIRRIN ZAMA DA MIJI

{KASHINA 9}

(IYA MAGANA)


BY

MUHD*ABBA*GANA
09039016969

yana daga cikin ladubban zamantakewa wadanda yake amta mace ta kiyaye shine ta iya magana a lokacin da take hira da mijinta ma'ana ya kamata tun farkon ta sani cewa ita fa macece kuma Allah madaukakin sarki ya san ya nutsuwarta a wajen mijinta don haka yana da kyau maganarta ta zama mai farantawa maigidanta. yana da kyau mace ta zama mai tausasa muryarta a lokacin da take hira da mijinta wato ta zama kamar wata karamar yarinya mai nuna shagwaba wannan shi zai dada sa mijinta ya yarda da ita kuma harta kallo idan zaki kalli mijinki to ya kasance kallone na girmamawa da mutuntawa kuma ya zama kallone da zai tabbatarwa mijin cewa kina kaunarsa kuma kin yarda dashi har a cikin zuciyarki, kuma yana da kyau ko a fagen tafiya kada mace ta zama kamar namiji musamman idan tana a gaban mijinta don haka ya kamata tafiyarta ta zama a bisa tsari da kuma nutsuwa amma idan tafiyarta ta zama ta hauka wato irin ta masu jin karfi to wannan zai iya rage kimarta a cikin zuciyar mijinta. haka kuma yana da kyau a musulunce mace tayi shagwaba a gurin mijinta domin nana aisha (RTA) ta kasance yar lelen manzon Allah (SAW) hasalima an samu lokacin data cewa manzon Allah (SAW) sai ya dauketa haka kuma yazo a cikin wani hadisi cewa manzon Allah (SAW) yana yin tseren gudu shida matarsa wato sayyidatu Aysha (RTA) don haka wannan yana nuna mana muhimmancin kyautata mu'amalla a tsakanin mace da mijinta domin a samu jin dadi nutsuwa da kwanciyar hankali sabanin yanda harkar aure take gudana a tsakanin al'ummar wannan zamani wanda zaka mafi akasarin jama'a wato ma'auratan sun saki ka'idojin zamantakewa shi yasa ake ta fuskantar matsaloli a tsakaninsu wannan yasa saika ga hartakai suga rabuwa wanda shine mafi zama abin ki a gurin Allah (SWT) a cikin harkar aure.mafi akasarin abinda ya sa ma aurata suke samun matsaloli a cikin harkar aure shine son zuciya da suke sa a gabansu wato ya zama an daina binciken abinda Allah yace ko abinda manzon Allah (SAW) yace sai ya zama su kuma mata sun maida aure kamar wata hanyar neman wadata da kuma arziki wato kamar kasuwanci tun a farkon neman auren ba a tausassawa mai neman sai a dinga dora masa abubuwa daban daban tun yana ganin kimar matar har ma ya daina ganin girmanta dana iyayenta, kuma sai a zo ayi auren shi kuma idan ya kalli wahalar daya sha kafin ayi auren shi yasa ba zai ji tausayin matar ba. kuma a karshe dai ita ma sai tace mijin ba zai juyata ba to haka dai lamarin zai ci gaba da kasancewa a tsakaninsu a karshe sai kaga an rabu domin kuma tun daga farkon auren an sabawa koyarwan manzon Allah. zan cigaba gobe insha Allah.
Share:

SAUYIN RAYUWA 71 (KARSHE)

sauyin-rayuwa.jpg

SAUYIN RAYUWA. page 71 na BABY ZAHRA HAIFA,ARIF, nd AFREEN, sun tashi cikin gata da jin dadin rayuwa, iyayen su suna mugun son su, ba a gwada musu ban banci kullum suna tare suna wasa, a hakan muktar yasake gina musu wata gidar babba falat uku ne acikin gidan nashi da na nasreen dana kaisa, rayuwa sukeyi cikin jin dadi, idan nasreen zataje hutu ta kan kwashe yaran ne dukka ta tafi da su, haka itama kaisan.
Viser yayi musu dukkan su, sukatafi London daga nan suka biya Egypt, sai da suka kama yawon shakatawar sune sannan suka tsaya a makka sukayi aikin hajji sannan suka juyo ta gida, dukkan su kowa ta dawo da nata tsarabar da muktar yabasu na wata bibbiyu, suna dawowa suka cigaba da rainon cikin su...........bayan wata bakwai ne kowa ta haifo danta, inda kaisa ta haifi Hajara mai sunan fulani, nasreen kuma ta haifi mai sunan mai martaba.....muktar yabude musu manya manyan shaguna na sayar da atamfofi da lesuna, ga kuma na jakkuna da takalmi, ko wacce da nata......zaman lafiya da jin dadi ga kwanciyar hankali ba irin wanda basayi agidan su sun sami SAUYIN RAYUWA bana kadan ba.......to ni kuma bari in huta anan, sai dai ince muku TAMMAT BI HAMDILLAH

Sai mun hadu a sabuwar littafina mai suna WATA RAYUWA insha Allahu.

Nice naku akullum FATIMA ZAHRA YAKUB wanda akafi sani da BABY ZAHRA

SADAKARWA
Na sa daukar da wannan littafin ma group ina
DUNIYAR LITTATTAFAN HAUSA
DA KUMA
GAREKU MATAN KASAITA
Ina mika gaisuwata ga dukkan mutanen group in
GODIYA TA MUSAMMAN
Ga duk masoya na masu karanta littafina

INA MIKA GAISUWA TA
Ga dukkan online writer's, Allah yakara mana basira gaba daya Amin thumma amin
ALHAMDULILLAH.
Share:

SAUYIN RAYUWA 66____70

sauyin-rayuwa.jpg

SAUYIN RAYUWA. page 66 na BABY ZAHRA
Da sallama tashigo, tasame su jigum jigum, muktar na kujera, kaisa na kasa, da sauri suka dago don ganin wake sallama, kallon junan su sukayi cikin makaki, murmushin karfin hali tayi, sannan tace nabaku makaki ko, inda kaisa take gun tanufa tazauna kusa da ita, sannan tace sister kiyi hakuri da abinda yafaru dazu nasan nayi kuskure, wlhy sharrin shaidan ne, da kuma mugun kishi dayake damuna, san......rufe mata baki kaisa tayi tace bakomai aunty nasreen komai ya wuce, ni fatana shine mu zauna lafiya a tsakanin mu, insha Allahu nasreen tace, tashi sukayi suka nufi inda mijin su yake, tsugunnawa sukayi akasa sannan suka bashi hakuri, rugumesu yayi dukkan su, sannan yasaka musu albarka....addu'o'i sukayi sannan suka shafa, suka roki Allah daya basu zaman lafiya a tsakanin su.
Wunin ranan kaf nasreen a gidan kaisa tayi shi, sukayi abinci tare suka citare, bata koma gidan taba har saida sukayi abincin dare sukaci, bayan tayi sallahr ishshane tayi musu sallama, muktar ne yarakata har gida, suna fita kaisa ta fada wanka, sama sama tadan shafa mai, ta murza powdar a fuskarta, sannan ta dakko sleeping dress brown colour iya cinyarta ya tsaya, tafeshe jikinta da turaruka masu kamshi, sannan tafito parlour a parlourn tasameshi, cikin kissa tace mai babyluv harka dawo, harara yasake mata sannan yace tun dazu nadawo har naje nayi wanka amma ke baki fito ba, kinshanyani inata zaman jiranki, ae na dauka yau inma rufe min kofar za ayi, murmushi tayi cikin kunya tace mai na isa.
BABY ZAHRA
[9:12PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 67 na BABY ZAHRA
Tace mai na isa, yau fa kai angone ko kataba ganin inda aka rufewa ango kofa, murmushin jindadi yayi, yace nasani ko za a fara akaina, zuwa tayi inda yake zaune, ta zauna akasa, da sauri yarikota sannan yace kintaba ganin inda amarya ta zauna a kasa, tace masa sosae ma kuwa, yace a'a kam ba dai amarya ta ba don haka zoki zauna akusa da angonki, rufe fuskarta tayi da tafin hannun ta, shida kanshi yadagota ta hau kujeran yajawota jikin shi, yace yanzu kinsan me zamuyi, kai kawai ta girgiza mai, yace tashi muje muyi sallah ko, too tace mai, sannan suka tashi suka shige cikin dakinta,
Bayan sun idar da sallahr ne yafito mata da ledar kaza cikin mamaki tace kai harda wani kaza sai kace wata amarya, cikin sauri yace mata to ae gashi kinfadi sunan da bakinki, murmushi kawai tayi, sannan yabude musu ledar ya yanko namar yasaka mata abaki takarba, itama ta yanko tasakamai yakarba, a hakan suka ciyar da junan su har suka koshi, bayan sun koshine suka koma falo suka saka film suna kallo, tana kwance ajikin sa, sai wasa sukeyi, tanata dan koke koke na shagwaba, cen dai misalin karfe 11:00pm, yatashi yakashe komai yakulle ko ina, cakk ya dauketa saboda jikinta duk ya mutu, dakinta suka nufa, yajiyeta akan gado, sannan ya hau aiki, (nidai danaga abin yafi karfin ganina falo nadawo na manna kunnena ajikin kofar kukan kaisa nake jiyowa tanata mai magiya amma ina muktar kam yayi nisa, Allah sarki kaisa taban tausayi bana kadan ba, kamar inshiga inkarbeta amma ina, yana iya masoyane suna son junan su) misalin karfe 4:00am ne yataimaka mata tashiga toilet tayi wanka, shi da kanshi ya gasamata jiki sosae, sannan yadawo da ita ya kwantar nan da nan bacci ya dauketa
BABY ZAHRA
[9:13PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 68 na BABY ZAHRA
Misalin 11:00am ta farka ido biyu sukayi da shi yana zaune ya hada tagumi, yanaga nin ta bude ido yazo da sauri, hannun ta yarike yace bbyluv kin tashi, harara ta galla mai sannan ta fisge hannun ta tajuya mai baya, murmushi yayi yace haba babyna gwiwata a kasa ayimun afuwa, ba donni ba, kuka tasake masa cikin hanzari ya hauro gadon ya rungume ta yanata lalla shinta, dayaga taki tayi shiru ne yace mata to tunda kinki yin shiru bari kawai mukara wani inyaso sai kiyi kukan da tushe, a razane tamike ta hau tattare tattaren kayanta ta nufi ban daki, takama wankan da bata shirya ba, dariyar mugunta yayi sannan yatashi ya hado mata abin karyawa, tana fitowa ta zauna don daman yunwa takeji, abaki yarinka bata harta koshi
A haka dai RAYUWAR su ta SAUYA daga ki zuwa so

Bayan sunyi wata daya ne ranan jumma'a suka shirya don zuwa gaida su momy, a gidan nasreen sukayi girke-girken da za su kaimusu, basket uku sukayi daya na abba daya na momy dayan kuma na aunty rukkaya,
Suna isa zara'u tafito ta rungumi nasreen, amma bata cewa kaisa ko sannu ba, don haka abinda tayin yabatawa nasreen rai, sai tace mata kanwata ga sister na baki mata sannu da zuwa ba ko baki ganta bane, abin yabawa zarah mamaki, sai kawai ta basar tace sannu da zuwa, yauwa kawai kaisa tace mata, dakin momy suka nufa, momy datagan su tare tasha mamaki, gashi sai wasa sukeyi da dariya, wai me yake faruwa ne, nan da nan wata zuciyar tace mata to ke ina ruwan ki, me na damuwa, tunda suma sun hada kai kam meye naki na damuwa, daga kafada tayi alamar ko ajikin ta, don haka ta karbesu hannu bibbiyu, bayan sun gaisa da momy ne suka sake dunguma sukayi dakin aunty rukkaya, nan ma itama tayi murna da ganin su haka, tayi musu addu'ar fatan alkhairi,falon abba suka nufa, bakaramin albarka ya kwararamusu ba, sannan daga bisani suka koma gidan su,
* * * *
Gida mai kyau nagani nafada abban abuja yasayawa abban jajere a cikin garin jalingo,ya kuma danka masa halak malak, don hakane ma aka saka sunan abban jajere ajikin takardun gidan, nan da nan suka tattara suka koma cen, don haka yanzu haka iyayen kaisa sun dade da koma cikin jalingo da zama
* * **
Nasreen na kwance yau kwata kwata bata ganewa jikin taba, tun safe take ta amai komai tasaka abakinta sai ta amayar da shi tarasa meyakeyi mata dadi, gashi taki tagayawa muktar, tana cikin tunanin ne sai gashi yashigo yasameta acikin bargo sai rawar dari takeyi
BABY ZAHRA
[9:13PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 69 na BABY ZAHRA
Subhanallah yace sannan yakaraso gurinta da sauri yadafa kanta yace sweet meyake faruwa kasa magana tayi, sai hawayene kawai ke zuba a idon ta, da sauri ya dakko waya yakira Dr sa yayi mai bayani yace masa gasanan zuwa, Dr na isowane daya dan dudduba jikinta yace tayi fitsari takawo, bayan falmata tariketa takaita bayan gidane, takawowa Dr fitsarin yatafi dashi yace abashi 15mnt yana zuwa......ba yan yadawo ne yake tabbatar wa da muktar cewa nasreen ciki ne da ita amma za asaka mata ruwa, bakaramin murna muktar yayi ba, har da kyauta yabawa likitan, shikenan aka shiga tattalin ciki
Da murnarsa ya zo yaga yawa kaisa cewa nasreen cikine da ita, itama tayi murna banawasa ba, sannan taboye masa nata cikin, saboda kaisa irin mutanen nan ne wanda basa laulayi, sai dai dan abinda baza arasa ba, amma kuma tana da dauriya shiyasa ma bata bari yasani ba
* * * *
Haka dai suka cigaba da renon ciki, muktar da nasreen basu tashi sanin kaisa nada ciki ba sai da ya kai wata 5mnth da sukaga abu yafara fitowa, da suka titsiyeta sai tace itama batasan tana da shiba sai da taga yafara fitowa kafin tasani, a hakan kuma suka yarda
Da watan haihuwar su yakama ne goggo indo tadawo gidan kaisa, nasreen kuwa dama already tanada masu kula da ita amma duk da haka goggo indo na kula dasu dukkan su
BABY ZAHRA
[9:13PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 70 na BABY ZAHRA
Ranan alhamis ne nasreen tatashi da nakuda, goggo indo ce takaita asibiti da muktar, hankalin kaisa duk Ya tashi, bayan 1hr ne sai gasu da santaleliyar yarinya mai kama da uwarta sak, murna agun kaisa kamar zatayi yaya, kwanan ta uku da haihuwa gidan yacika da jama'a, en fada sunzo mota uku,
Ranar suna ne yarinya taci sunan momy wato hafsat ana kiranta da HAIFA anci ansha,
Aranar da akayi sunan ne kuma kaisa a asibiti ta kwana, har sai washe gari tasamu ta haihu, ta haifa santalelen yaron ta mai kama da uban sak, bayan an fito da yaron ne, ana shirin yanka cibine kuma wata sabuwar nakudan ta tasowa kaisa, bakaramin mamaki likitocin sukayi ba don ba wata alama da tagwada en biyu ne acikin kaisa, amma sae me....santaleliyar yarinya ce ta biyo baya da hancinta irin na uwarta sak, da aka fito aka gayawa su goggo indo da muktar basu yarda ba, sun dai ce dai kawai inta haihu agaya musu, likitanne yace abokina da gske nake muna needing wani kayar jariyar da za sakawa dayar, goggo indo ce tafita da gudu bakin asibitin taje tasiya agurin masu sayarwa, ta dawo da gudu ta basu, muktar baitashi yarda ba sai da yagansu da idon sa, sujjada yayi agurin, yana mai godewa Allah daya bashi irin wannan kyautar, kara duba su yayi mace ce da namiji, rungume su yayi sosae, cen saiga kaisa ta fito goggo indo ce ke rike da ita dakyar take iya tafiya, muktar kamar zai hadiyeta yakeji, suka shiga motar sukayi gida
Kowa yasha mamakin haihuwar kaisa, gida ya kacame da murna...
Ranan suna ne yara sukaci sunan abban abuja da kuma innar kaisa, wato usman da amina, usman ana kiransa da aarif, ita kuma amina ana kiranta da aafreen
BABY ZAHRA
Share:

SAUYIN RAYUWA 61___65

sauyin-rayuwa.jpg

[9:12PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 61 na BABY ZAHRA
Yakai kusan 15mnt yana knocking kafin tazo ta bude, tsaya wa tayi abakin kofar tarike kofar tana mai wani irin kallo irin na tsoffin bariki, kusan 5mnt tana haka sannan tace mai antashi lafiya, bata ji ra amsar saba ta juya ciki, yana binta a baya kitchen ta nufa tacigaba da abinda takeyi, cikin tsarguwa da tashin hankali yace mata kaisa don Allah kiyi hakuri da abinda na miki wlhy ba sona bane kuma nasan ban kyauta ba........har ya karaci maganar sa bata ce mai komai ba, indomie take dafawa harta gama ta juyeshi a plate bata amsa masa ba, bata ma juya ba balle tasan meyake fada, tana gamawa fitowa tayi dakinta ta nufa, yazo zai shigo kenan ta bugo kofar tasaka key, ta zauna taci abincin ta cikin kwanciyar hankali, tana gamawa ne, ta kira rukky kobi ta fada mata yanda sukayi, dariya suka sheke da shi rukky kobi tace ki kwantar da hankalin qawata, kar kiyi mai komai a hakan zaki gara shi, kuma karkice zaki ki yimasa magana fa, kina masa amma banda dariya, too qawata karki damu cewar kaisa, bakiga yanda yadamu bama yanzu, rukky kobi tace ae haka ake musu a hukuntasu ta cikin kasa, sake shekewa sukayi da dariya, sannan sukayi sallama, suka kashe wayar
BABY ZAHRA
[9:12PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 62 na BABY ZAHRA
Misalin karfe 12:00pm na rana ne tafito ta daura abincin rana, tana gamawa sai gashi nan yashigo, dakko mai tayi tazo ta ajiye mai agaban sa ta zuzzuba mai, har yana murna ya dauka ta sakko ne, fuskar ta dai ba yabo ba fallasa har tagama mai, tana zaune agurin yana cii yana yimata magana, in magar ehh tace ehh in kuma na a'a tace a'a, shidai har yagama bai gane mata ba, yana gamawa takwashe ta kai kitchen, zata wuce daki yace mata kaisa zonan inason magana da ke, dawowa tayi batare da tace komai ba, ta dawo ta zauna, a kasa, don wannan al'adar kaisa ce, in har yana kujera to ita tana kasa, yace mata a'a tashi ki hau kujera tace mai a'a inajinka daga nan ma ba sai nahau ba, daga kafada yayi alamar bai damu ba, saboda yasaba da irin wa ennan halayen kaisa, yace mata kaisa, shiru tayi bata amsa ba, yasake cewa kaisa, nan ma shirun tayi, sai da yafadi baki uku sannan tace na am ya muktar, ajiyan zuciya yayi sannan yace mata kaisa nasan inna fada miki abinda ke zuciya ta ba zaki yarda ba ko.
BABY ZAHRA
[9:12PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 63 na BABY ZAHRA
Shiru ne yaratsa falon na dan wani lokaci sannan yace da farko dai nasan namiki laifi kaisa, amma don Allah ina mai baki hakuri akan abinda namiki, nan ma shirun tayi sannan yace mata kinyi shiru kuma kaisa, yarrr tayi da manyar idanun ta tawani kadasu sama, sannan tace ni babu abinda kamin balle kabani hakuri, shiru yayi yana kallon ta, sannan yace kikace ba abinda na miki, daga mai kai tayi alamar ehh, sannan tace ni bansan akan me kake bani hakuri ba, cikin jin kunya yace ina baki hakuri ne akan daukar kwanan ki danayi nakaiwa er uwarki, kallon shi tayi cikin mamaki, sannan tace to ai ba laifin ka bane, kasan abinda zuciya bata so koma maye zata iya aikatawa akai, cikin hanzari ya sakko kasa inda take zaune yakamo hannuwar ta yarike su gam acikin nasa, sannan yace wallahi tallahi INA SONKI KAISA, ina SON KI har cikin ZUCIYATA, bantaba sanin me ake kira so ba sai akan ki, sai yanzu na lura ashe shirme mukeyi da nasreen ba soyayya ba, sai akan ki nasan me masoyi yake ji aransa akan masoyoyar sa, kaisa don Allah ki taimaka KI SONI koda kwatan kwacin wanda nake miki ne.......kamar saukar ARADU kaisa taji kalaman muktar, nan da nan zuciyarta ta karyata mata abinda yake fada.
BABY ZAHRA
[9:12PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 64 na BABY ZAHRA
Cikin hanzari tace ya muktar indai don abinda kamin ne kake so kamin karyar kana sona, ni nayafe maka, amma bana son kana karya donni banna ganin mutuncin mutum mai karya, kaga kuma ni ina ganin girman ka, bai kamata ace kamin karya don in yafe maka abinda kamin ba, kum.....hannu yasaka yatoshe bakinta cikin hanzari, yace kaisa me zan miki don kigane ina tsananin sonki, kaisa ke kalli cikin kwayan idona zaki gane da gske nake, kaisa ko sai na dakko al Qur'ani na rantse miki kafin zaki yarda, mikewa yayi cikin hanzari zai dakko Qur'ani, rike hannun shi tayi cikin hanzari tace ya muktar ba sai ka dafa Qur'ani ba na yarda da kai baka karya ya muktar kakan fadi abinda ke ranka ne, kuka ne ya kwubce mata mai tsuma ran masoya tace daman ashe akwai ranan da zaka budi baki kace kana sona, dawowa yayi ya fuskanceta yasaka hannu yashare mata hawayen ta, sannan ya rungume ta yace kiyi shiru matata, na dade da sonki a raina, amma ban yarda ba, saboda inaganin kamar zuciya ta karya take min, sae da naga sonki zai kasheni kafin na yarda ashe da gske sonki nake, yace kitaimaka kice kina sona don Allah, cikin kwanciyar hankali tace ina sonka yayana! yayana ina sonka!! wani dadine yarufe muktar yadada matseta ajikin sa.........ji sukayi ana cewa to maci amana namiji kudan Zuma inbai kasheka ba zai saka ka jinya, ashe akwai randa zakaci amanata muktar ashe duk irin alkawarin da ka dade kana dauka min na karya ne......
BABY ZAHRA
[9:12PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 65 na BABY ZAHRA
Sake junan su sukayi cikin razana, mikewa yayi a fusace yace ke wai wata irin mahaukaciyace, ko kin mance yanda kike matata itama haka take, kuma in daa na dau miki alkawari to yanzu na karya, kuma ki wuce kifita ke ban guri, kuka nasreen tasaka sosae kamar wacce akama rasuwa, tafadi tanata shure shure, a hankali kaisa ta matso inda take takama hannun ta tace haba aunty nasreen don Allah kisakawa zuciyar ki ruwan sanyi, ni ba abokiyar gaban ki bace, kiyi addu'ar Allah yarabaki da mugun kishi, bashi da amfani, ki tsaya kiyi tunani muhada kai mu zauna lafiya....fisge hannun ta tayi tace dalla cen sakeni makira, in banda makirci ba abinda kika iyayi, tsaki taja sannan ta juya takalli muktar tace mai kai kuma ina jiran takardata, don yau zankoma garin mu, sannan ta wuce tatafi gida, tana fita ya dauki waya yakira numbern baba waziri, bayan sun gaisa ne cikin girmamawa sannan yakaranto masa abinda ke tafiya a gidan sa, baba waziri yaji haushin maganar bana kadan ba, sannan daga bisani yabawa muktar in hakuri, akan zai kira nasreen in

Fada sosae baba waziri yayi wa nasreen sannan daga bisani yayi mata wa'azi mai ratsa jiki, bai kyaleta ba har sai da ya fahimci jikinta yayi sanyi, sannan daga karshe ya umurce ta dataje tabawa mijin ta da abokiyar zamanta hakuri...bai kashe wayar ba har saida ta masa alkawarin zataje tabada hakuri sannan kuma tayi alkawarin irin haka bazai kuma faruwa ba, albarka yayi ta sakamata sannan ya yakashe wayar, kukane ya kwubce mata tayi kuka iya isarta, sannan ta yayyafawa zuciyarta ruwan sanyi, tashiga toilet ta wanke fuskarta sannan tafito tashafa mai tadan murza powder har da wetleaps sannan ta yafa gyalenta tafito.
BABY ZAHRA DAN ALLAH IN AN KARAN TA ANA AJIYE COMMMENT
Share:

SAUYIN RAYUWA 56____60

sauyin-rayuwa.jpg

[9:12PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 56 na BABY ZAHRA
Tashi yayi ya nufi dakin, wow yace gsky dakin yayi kyau ga kamshin turaren da ke tashi a dakin ga wani sanyin a/c wanda ya hadu da kamshin turaren sai yabada sanyi mai dadin kanshi, toilet in ya nufa shima nan yayi kusan 5mnt yana kallon bayan gidan daga bisani ya soma abinda yashigo dashi,
Ita kuwa kaisa tana ganin yashige itama ta tashi tayi nata dakin ta sanya key, tayi kwanciyar ta abinta,
Bayan yafito daga wankan ne yasanya kayan bacci, yafito falon sai kuma bai ganta ba amma kuma tv yana kunne , zama yayi ya dauka ko itama tashiga wankan ne har yanzu bata fito ba, zaman jiran ta yakeyi, har tsawon 30mnt amma yaji shiru tashi yayi yanufi kofar dakin tan yadan murda hannun kofar, yajita gamm, tsaki yayi sannan ya nufi nashi dakin, ranshi a bace ya kwanta, yanata juye juye, wata zuciyar ce tace masa to kai naka a wanne daman so kake ku kwana tare kome, ko ka mance baka son tane, tsaki ya kumayi akaro na biyu, yaja bargo ya gyara kwanciyar sa, da kyar bacci ta dauke shi.
BABY ZAHRA
[9:12PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 57 na BABY ZAHRA
Washe gari da safe kafin yatashi ta gama masa komai na abin karyawa, yana fitowa yayi arba da ita cikin wata riga da wando 3Quetta tadan kama kanta da ribon tanata goge gogen su tv, ya fito yayi kusan 10mnt yana tsaye ya harde hannuwar sa yana kallon ta....haka kawai taji ajikin ta kamar ana kallon ta, a hankali ta Juyo... ido biyu sukayi da shi, irin kallon da yake mata ne yasakata taji kunya amma sai ta batsar, har kasa ta tsugunna cikin ladabi tace ina kwana yaya....karkiso kiga bakin muktar har kunne yana amsawa, hummm dariya yabata amma sai taci fuska bata gwada masa ba,(ashe fa gskyr rukky kobi ce, don ita tabata wannan kissan), cikin kisisina tace masa ga abin breakfast inka nan akan dining table, cikin annashuwa yace to bismillah muje, tana gaba tanata girgiza mazaune shikuma yana binta abaya kamar bunsuru duk hankalin sa yatashi, ita ta jawo mai kujera ya zauna, sai da yazauna sannan tafara zubamai abincin, itama kuma ta zauna don ta deba masa kewa, farinciki yagama kama muktar don ganin yau kaisa tasake mai fuska, dibo soyayyiyar dankali yayi, yamika mata a bakinta, ko kunya bata jiba tasa baki ta karba, farinciki yagama kasheshi a zaune
BABY ZAHRA
[9:12PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 58 na BABY ZAHRA
Allah Allah yake yagama cin abincin.... kaisa tagama fuskantar inda ya dosa, cikin nutsuwa da kissa ta tashi tsaye, cikin sauri yace mata ina kuma zaki bayan kuma bamu gama ba, cikin sassanyar murya tace masa, wlhy kaina yake ciwo zan dan kwanta, nan da nan hankalin sa yatashi, yace to kije ki shirya muje asibiti ko, cikin kissa tace masa a'a wlhy ae nasha magani bacci kawai nake bukata, tashige tayi dakinta, danna key tayi sannan tayi dariyar mugunta,tace hummm yafara shiga hannu, kadan kafara gani ae wlhy sai na gara ka.......kwanciyar ta tayi abinta tanajin shi yana murda hannun kofar, amma tayi banza da shi haryagaji yayi gaba, har bacci ya dauketa, misalin karfe 12:00pm ta tashi abincin rana ta daura, tana cikin yanka carrot ne, taji hannaye sun zageye mata kugu, gabanta ne yafadi sosae amma sai ta batse,tayi murmushin karfin hali, tace yaya na harka tashine, cikin jin dadi yace mata ya ciwon kan dai, tace lfyklw na warke, cikin tsokana yace mata wato shine kika kulle min daki ko, hummm tace masa, cikin faduwar gaba tace ae kasan kaina ke ciwo shiyasa, yace to ae yanzu an warke ko, tace ehh, yace to ae baza akulle min da daddare ba ko, humm kawai tace masa cikin kunya, yace mata ya da humm kuma, tace babu, yace to ya baza akulle min ba ko, ce mai tayi Allah ya kaimu, cikin annashuwa yace amin, sunbatar ta(kissing) yayi a kumatu,sannan yasake ta yace bari in je gida abba yana son ganina, har kofar falon ta rakoshi, tamai addu'ar fatan alkhairi
BABY ZAHRA
[9:12PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 59 na BABY ZAHRA
Bai gama da abba ba har sai bayan sallahr ishsha, duk hankalin sa ya gama komawa gurin kaisa, sai da abba yalura da hankalin shi baya gurin ne shine ya sallameshi, yana zuwa gidan nasreen ya dosa, don yayi mata sai da safe.....a falo yatarar da ita daga ita sai dan gajeren wando iya cinya, sai 'yar riga fale fale ya manne ajikin ta gashi shara shara, kuma ko bra babu ajikin ta komai najikin ta ana gani..da sauri tamike taje da gudu ta rungume shi tace sweet wato yau kashare ni ko don kaje gurin amaryar ka, tunda safe fa nake jiran ka, cikin shagwaba tayi maganan, shafa gashin kanta yayi sannan ya yi kissing inta yace yi hakuri sweet wlhy yanzu ma daga gurin daddy nake tun safe ya rike ni sai yanzu...jawo shi tayi dakinta, ta kwanta akansa ta soma romantic insa tun yana ki har yaba da kai........misalin karfe 12:00pm ne na dare ina zaune abakin gado raina idan yakai million to yabaci wato ni muktar zai wulakanta ko, yasa namasa girki amma baizo yaci ba, yau ranar kwana na amma ya kaiwa nasreen, hummm dogon numfashi ta jaa sannan ta kwanta ta jawo bargo, amma dakyar bacci ya dauketa.
BABY ZAHRA
[9:12PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 60 na BABY ZAHRA
Misalin karfe 4:00am na asuba ne ya farka daga nannauyin baccin da yayi, KAISA! abinda zuciyar shi tafara ambato kenan, a firgice yatashi wanda har sai da yasa nasreen itama ta farka a razane, lafiya tace masa, da sauri yace mata kaisa, bai masan lokacin da ya furta mata hakan ba, cikin bacin rai nasreen tace meye kuma wani kaisa, yace mata nasreen yau fa ranar kwanan kaisa ce nazo na kawo miki, haramtacciyar kwanciya fa mukayi, tsaki taja masa tace to sai kuma me don ka kwana agurina ranan kwanan kaisa, sau nawa ana haka, cikin tsawa yace mata baki da hankali ne nasreen, inda kece aka miki hakan yaya zakiji a ranki, cikin kissa tasaka masa kuka mai cin rai,tace ashe har lokaci yayi da zakafara wulakantani akan wata, tsaki yaja, baiyi niyar rarrashinta ba amma dayaga kukan nata dada yawa yakeyi shine yajawota jikin sa ya hau rarrashin ta, a hakan taso su sake komawa gado amma yaki, ranta idan yakai million to yabaci, ta dada tsanan kaisa a ranta, yaushe muktar ya soma son kaisa, da har zai fara nuna mata kulawa irin haka,to wlhy kuwa zanyi maganin su tafadi hakanne aran ta, haka muktar ya karasa kwana a zaune daya fita sallahr asuba ne bai dawo ba ya wuce gidan kaisa, mai gadi ne yabude mai gate ya shigo cikin hanzari yana gaishe shi ma amma bai tsaya amsawa ba kofar falon ta ya nufa
BABY ZAHRA
Share:

SAUYIN RAYUWA 51___55

sauyin-rayuwa.jpg

[9:12PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 51 na BABY ZAHRA
Washe gari da safe ne akayi wuni, da yamma kuma akayi budan kai, ko wacce amarya aka kaita gidan ta, en uwan kuma suka koma gidan su muktar don su kwana zuwa ashe gari,

Abokanan sane suka rakoshi gidan nasreen, suna zazzaune a falo, akayi siyan baki, sannan suka danyi dan barkwanci daga bisani sukayi gaba, sallah ya umurce ta da su tashi suyi, bayan sunyi sallahr ne suka zazzauna a falor suka danyi ciye ciyen su, suka kunna TV suna kallo, tana kwance lamo ajikin sa sai soyayyar su suke sha, yana ta wasa da jikinta,daga bisani kuma suka tashi suka wuce cikin daki ( nidai a falon natsaya daga nan kuma na wuce gidan kaisa don inga halin da take ciki.. )
Aceen kuwa kaisa anakaita ta tashi ta rufe kofar gidan gabaya kasancewar tasan muktar ba zuwa zaiyi ba, duk da tasan ita yakamata yazo yafara kwana wa, saboda ita akafara daurawa aure da shi, amma tasan rashin adalci irin na muktar bazaisa yazo ya kwana mata ba, yabar nasreen acen, daga kafada tayi alamar ko ajikin ta, gyara kwanciyar ta tayi ta dada jan bargo zuwa jikinta, tayi baccin ta

Da asuba kuwa shiya taimaka mata tayi wanka, sannan suka sake komawa suka kwanta, tana kwance ajikin sa farin ciki yau Kamar zai kasheta, yau itace da muktar inta agado daya....
BABY ZAHRA
[9:12PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 52 na BABY ZAHRA
Misalin karfe 11:00am yatashi a firgice KAISA ce ta fado masa a ransa, a hankali yacire nasreen ajikin sa, toilet yashige yadan watsa ruwa, a gurguje ya sanya kayan sa...gidan kaisa ya nufa kasancewar gidajen a manne suke, katangane kawai yarabasu, tun daga bakin kofar falon yaji kamshin turaren wuta yana tashi, da sallama yashiga falon yaji shiru ya lalleka ko ina baiganta ba, uwar dakin yanufa, tana zaune bisa sallaya sallahr walaha tagabatar tana jan carbi tsayawa yayi sai da ya gama kallon ta sannan yayi mata sallama, a hankali ta amsa masa, saboda daman tunda taji motsi a falo da taso taje ta leka sai kuma taji anshigo tasan ba wanda zaiyi hakan inba shiba, bata juyo ba har saida ta gama tasbihinta, abakin gadon ya zauna, tajuyo tace ya muktar ina kwana,shiru yayi yanata kallon ta kusan 5sec kafin yace mata kin tashi lafiya, tashi tayi a inda take zaune, nade sallayar tayi sannan tayi taku daya biyu tace masa kalau nake, binta kawai yayi da kallo, yace ba akawo miki abin karyawa bane, tace mai ankawo fa, yace to zan iya samu indan ci, cikin tsiwa tace masa ae ba anan ka kwana ba, sake binta yayi da kallo tana bashi mamaki batsoro kwata kwata a idon ta take magana, tashi yayi ya nufi inda take
BABY ZAHRA
[9:12PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 53 na BABY ZAHRA
Tashi yayi ya nufi inda take, tana tsaye ajikin wadrop tana gyara kayan ciki, jitayi hannuwar sa sun zagaye kan kugunta, cikin firgici taso juyowa amma ina yayi mata mummunar kamu, gabantane yake mugun faduwa, cikin tashin hankali tace masa ya muktar meye kuma haka, don Allah nikam kasake ni, cewa yayi in ankifa, shiru tayi tanata murkususuwa tana son kwace kanta, amma ina, sai ma ce mata da yayi, kin san Allah in kikayi wasa yanzu zanyi maganin wannan rashin kunyarkin, cikin tsiwa tace masa to to ni me namaka, daukar ta yayi cak ya wurga kan gado, ya hau ruwan cikinta, ihu tasaka masa mai karfi, da sauri ya lalumo bakinta yasaka a nasa, sai murkususu take tana son ture shi amma ina ko motsi bayayi, hankalin kaisa duk yagama tashi, hawaye ne kawai suke gangara ta gefen kumatun ta,
Nan da nan zuciyar shi ta rayamasa cewa kamance da alkawarin da kawa nasreen ne, na bazaka taba kusan tan kaisa ba.....cikin sauri yamike akan kaisan cikin huci ya fito falo, wayar sa ya dauka missed call in nasreen ne yafara arba da shi, 20 missed call yagani, tsaki yajaa sannan ya fito daga gidan
BABY ZAHRA

[9:12PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 54 na BABY ZAHRA
Yana fita da sauri tabiyo bayansa ta kulle kofar gidan gaba daya, kaii gsky yau muktar yayi mugun razata, ko me yatunone yafasa aika aikan da yake shirin mata, ummm koma dai me yatuna nikam dai yataimake ni, Kutt kullum ana ce min maza basu da kunya ban taba yarda ba sai yau, yanzu ashe ya muktar har zai iyayi min haka, to ni yanzu da wani idone ma zan kalle shi, duk yanzu yabi ya daura min kunyarsa a rai, kai Allah dai ya kyauta....ae kuwa tun daga ranan kaisa tafarawa muktar wasan en buye buye, shi kuma duk hakan ya dame shi amma bai gwada mata ba, kullum da safe zai zo su gaisa, har kwana bakwai in nasreen yacika,
Kuka takeyi shar shar tace haba sweet kwana 7 zanyi batare da kaiba, bayan kuma kasabamin da kwanciya ajikin ka, don Allah sweet Kaduba dai kagani, cikin mulki yace mata to ae itama haka tayi hakurin kwana 7 in batare da ni ba, kuma itace karama a gangan ki, haba sweet amma fa kai da kanka fa kamin alkawarin bazaka taba kusan tar taba, cikin nutsuwa yace mata to ae don na kwana agidan ta ba wai shine na kwana akanta ba, tana da dakinta ina da nawa, haka kowa zaina kwana anasa dakin, ko kuma kinaso ne ran lahira intashi da shanyayyar jiki, saboda bana adalci agurin matana,
BABY ZAHRA
[9:12PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 55 na BABY ZAHRA
Dakyar ya shawo kan nasreen tabarshi yatafi, kasancewar tana da masu aiki da aka kawota da su su biyu, falmata ce da rabi, aka hadota da su daga fada, amma duk da haka sai da yakira zahra don tazo ta taya ta kwana,
Misalin karfe 8:00pm na dare ne ya shigo falon kaisa da sallama, a falo ya taddata tana kallo, tana ganin shi taji gaban ta yafadi,bata zaci zaizo ba, zama yayi akan kujera, tajuyo a hankali tace masa ina wuni ya muktar, idon sa yana kallon tv yace mata lfyklw, tashi tayi ta shige kitchen ta hado masa abinci akan tire, ta kawo masa, ita da kanta tazuba masa sannan kuma ta zauna agurin tana zaman jiran shi yagama, a hankali yace mata kizo muci, kai kawai ta kada masa alamar aa , daga kafadun sa shima yayi alamar ko ajikin sa, yacigaba da cin abincin, abincin yayi masa dadi sosae don tuwan semo ne da egusi soap yaci abincin sosae, yana gamawa ya wanke hannun sa, ita kuma ta kwashe tayi kitchen,bayan ta dawo falon ne tashiga dakinsa dama already ta gyara tasaka turarurruka masu dadi, toilet ta nufa ta hada masa ruwan wanka, tasaka turaren wanka aciki, sannan tafito falon tace masa na hadama ruwan wanka, cikin jin dadi yace mata too.
BABY ZAHRA
Share:

SAUYIN RAYUWA 46___50

sauyin-rayuwa.jpg

[9:12PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 46 na BABY ZAHRA
Misalin karfe 11:00am dai dai aka daura auren MUKTAR USMAN SHEHU JAJERE, da amaryar sa NASREEN MUHAMMAD LAMIDO, ran asabar wanda yakama 03/01/2051 akan sadaki naira #500k, yau dai burin nasreen dai ya cika,tanata rawar kai a cikin gidan yau za akaita gidan angonta,masoyin ta,abin alfaharin ta,rungumar filo tayi da sauri ta kwanta rigin gine ,idon ta yana kallon silin, muktar shi da kanshi ya koma jajere don dakko kaisa, tunda suka dakko hanya ba wanda yacewa kowa ci kanka, sai tsula gudu kawai yakeyi akan hanya, ceeen dai yadan saci kallon ta ta gefen ido, tasha kwalliya tayi kyau kuwa sosai sai wasa takeyi da en yatsunta da suka sha kunshi mai kyau, tayi kyau fa yafadi hakan a ransa, suka cigaba da gudu har suka iso, wani gida suka dosa sai da suka iso yace mata fito, a hankali ta fito tabi bayan sa knocking yayi abakin kofar dakin, wata mata ce ta bude kofar suka shiga, tace a'a muktar kar dai wannan ce dayan amaryar tamu, murmushi yayi yace eh itace, ta kamoni tace sannun ki da zuwa fa, murmushi nayi bance mata komai ba sannan na nemi guri na zauna, daki ta shiga sai gata da mijin ta, yace ya abokina har kun iso, ehh kawai muktar yace masa, sannan yace bari in dakko nasreen ko ina zuwa, yace masa too,
Ceen kamar bayan 30mnt saiga shi ya dawo ce min yayi tashi muje, cikin nutsuwa na tashi, nabi bayan sa,har kofar gidan matar ta rakomu, bayan na bude nashiga, sannan itama ta tashi daga gaban ta dawo baya, muktar ne ya shiga gurin zaman ta while abokin sa kuma ya shiga mazaunin direba, yaja muka tafi, a hankali nace mata ina wuni, sai da ta kalleni sosae sannan ta iya budan baki cikin yatsina tace min kalau
BABY ZAHRA
[9:12PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 47 na BABY ZAHRA
Har muka isa airport ba wanda yakuma ma wani magana, kaina yana kan waya ta ina game in candy crush, muna zaune muna jira a kira mu, a tsakiya muka saka shi sai tadin su sukeyi shi da nasreen, tana kwance a kan kafadar sa, ni kuwa sai game ina nake tayi, duk a tsarge ma nake sakamakon kallon da wani a ake ta mun gsky na tsargu da yawa,duk na bi na matsu ma muyi mu tashi, ceen kuwa sai aka fara kiran mu... Munjeru cikin layi muna shiga jirgin, kowa kan numbern site insa ya nufa, nasreen da muktar tare suka zauna while ni kuma site ina yana ta gefen nasu muna facing in juna, ji nayi ana cemin barka dai hajiya, najuya gefena wa zan gani wannan matashin ne da ya isheni da kallon nan, bance masa komai ba yanata min magana amma nayi shiru, hankalia duk yabi yatashi duk da A/C da ke cikin jirgin amma ni zufa nake hadawa sakamakon wani mugun kallon danaga muktar yana min, magana nasreen ta ke masa amma ina hankalin sa yayi nisa gurin kallon mu nida mutumin nan, shiru nayi tayi har Allah yasa jirgin mu tasauka lafiya, nan da nan jikina yakama bari sakamakon bina danaga mutumin nayi, sae da muka isa dai dai gurin motar dazamu shiga ne, muktar yatare mutumin da cewa malam lafiya kam ko, murmushi matashin yayi ya mika masa hannu da sunan suyi musabaha amma ina kememe muktar yaki yabada hannun sa, sae ma ce masa da yayi cikin tsawa kai tambayar ka fa nake lafiya, cikin nutsuwa yace wlhy lafiya kalau sai alkhairi, wlhy naga kanwar kace kuma ina so, wlhy in za aban ita ina so kuma da aure, amma tun dazu nake mata magana taki kulani, wani mummunar harara muktar yasake masa, sannan yace ce maka akayi tallar ta akeyi ne ko meye, to mata nane ita ko da magana ne, cikin sauri saurayin nan yace a'a ba magana, amma in kana son ka hanani ita ba sai ka dangan ta ta da matar ka bama in kace min baka sona ba shikenan ba.
BABY ZAHRA
[9:12PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 48 na BABY ZAHRA
Ya wuce yayi tafiyar sa abinsa, ran muktar in yayi millions to duk ya bace, da karfi yabude gabar motar ya buga ta da karfi, drivern sune yace Allah ya huci zuciyar ka yallabai ko uhumm baice masa ba, haka zalika ran nasreen ma ya baci sosae akan meye muktar zai gwada kishin sa akan yarinyar da yace baya so, kodai muktar karya yayi min dai, dukka motar kowa ranshi a bace haka suka iso gidan, hannu bibbiyu aka tarbesu nasreen tayi dakin momy kaisa kuma tayi dakin aunty rukky, sai misalin karfe 4:30 kafin sauran suka iso a gajiye, en uwan nasreen aka sauke su a masaukin su, en uwan kaisa ma aka sauke su anasu masaukin
[9:12PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 49 na BABY ZAHRA
Misalin karfe 8:00pm kowa ya shirya don zuwa gurin DEENA, har an fara tafiya da wasu ma gurin, masu kwalliya aka dibowa amaren, muktar ne ya kawo kayan da zasu saka, kasancewar shi ya hada dinar, fess sukayi kamar basu ba, sai da kowa yagama tafiya kafin aka umurci amaren da su fito su tafi, amota suka hadu, shine a tsakiyar su, suka tafi, suna isa bakin hall in motar ta tsaya, suka fito daya bayan daya, nasreen bata tashi ankaran ashe kaya iri daya suka saka da kaisa ba sai da hasken wutan filin ya haska su, tana gani taji kamar tayi hauka don kishi mai muktar yake nufi dayakama yayi musu kaya iri daya da wannan bakauyiyar yarinyar, haushi ne ya rufe ta, amma ba yanda ta iya haka nan dai suka jera zuwa ciki, kujeru uku aka saka musu shi yasha kayan ado, a tsaki ya suka sakashi, bakaramin kyau sukayi ba, anci ansha sannan aka cashe, misalin karfe 1:00am sannan suka gama aka kwashi kowa aka mai da shi gida, sannan amare da angon su suma suka tafi, suna isa kaisa ce tafara bude motar don ganin yanda nasreen take shishshi gewa jikin muktar duk sai kunya takama kaisa shiyasa ma tayi ta Allah Allah su samu su iso gida don ita bata taba ganin irin wannan al'amarin ba.
BABY ZAHRA
[9:12PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 50 na BABY ZAHRA
Agajiye ta shige dakin su saboda tagaji ba kadan ba, kwanciya tayi da niyar yin bacci amma sai mee?, abinda yafaru tsakanin nasreen da muktar ne yafado mata nan da nan taji bacin rai yakamata tarasa meyeke mata dadi a wannan daren, ceen kuma sai wata zuciyar tace mata to ke bacin ranki akan me, bayan ba sonshi kikeyi ba, in ma sunyi ba masoya bane su ke kuma naki a wanne, tsaki tayi da karfi wanda har sai dayajawo hankalin mutanen dakin kowa yajuyo yana kallanta, rakiya ce tace kawata lafiya kuwa, kada manyan idanuwarta tayi, tayi wani yarrr da su, tadan yatsina fuska tace wlhy kaina ke ciwo, daya daga cikin en dakin ne tace bari in baki panadol, cewa tayi a'a kibarshi kawai ban son shan magani bacci kawai nake bukata, tadan gyara kwanciyar ta, amma ina bacci yaki zuwa mata tunanin muktar ne kawai yake zuwa mata, sai tsaki takeyi acikin ranta

Juyi yakeyi kawai agado amma bacci yaki zuwa masa, yarasa meyasa yanzu daga zaran yasaka kansa akan filo da sunan bacci amma sai ya gagara, in banda tunanin kaisa ba abinda yakeyi, yarasa dalilin wannan abu ga wacce yakamata yayi tunanin ta amma bayayi saina kaisa, tsaki yayi yadan gyara kwanciya, ko zai dan samu bacci yazo masa amma sai mee? tunanin ta yacigaba tun bayajin dadin tunanin har yafara ji, nan da nan yaji ransa tana son ganin ta, wayar sa ya dakko ya dialing numbern ta, ceen kuma kome ya tuna sai kuma ya fasa yayi tsaki yayi cilli da wayar gefe.......haka dai tsakanin kaisa da muktar bawanda ya rintsa har saida akayi kiran sallar farko kafin shaidan yazo yarufe su da babbar bargo, bacci mai dadi ya dauke su.
BABY ZAHRA
Share:

Friday 22 April 2016

WAI ME YASA???

peopleimagessm7.jpg

KISHIYA ABOKIYAR ZAMA CE. BA ABOKIYAR GAABA BA: * Idan wani abu ya sameki (Nakuda, rashin lafiya, ko wani abun) kafin 'Yan uwanki su zo, ita zata fara kulawa dake. * Zata yiwa yaranki wanka da wanki, ko kina nan ko ba kya nan. * Ita zata yiwa Mijinku da 'ya'yanku girki ta kula dasu alokacin da kike da lafiya, ko kike jinya. * Ranar da baki da lafiya (haidha), ita zata debe ma Mijinku kewa. * Ita ce babbar Qawarki, abokiyar zamanki, abokiyar shawararki, kuma babbar Makwabciyarki. DON ALLAH KU 'MATAN ZAMANI wai me yasa kuke QIN KISHIYA NE???

Share:

SAUYIN RAYUWA 41___45

sauyin-rayuwa.jpg

[9:11PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 41 na BABY ZAHRA Cikin sauri goggo indo tace to wawiya wannan kudin ne yayi yawa, bari in kirga inga nawa ne, kirgawa goggo indo tayi tsaff 300k ne cif cif , cikin sauri kaisa tace 300k goggo indo ae yayi yawa, harara goggo indo tasake mata tace wai kin mance ne bamu bayar fa da kudin dilkan ki bafa gasu kudin gyaran ma duk ba akarasa bayarwa ba, kuma ae jiya kina ji hajja fatee takirani tace an kawo turarukan wutan ki, too kawai kaisa tace, sannan goggo indo tace kuma ina son zakiyi kamu ma, tace ammafa nace masa walima kawai zanyi, goggo indo tace banni da shi zan gaya masa tace mata too ta tashi taje ta jona wayar ta a charge... Washe gari har gurin motar suka raka shi sannan yatafi su kuma suka juya gida, gidan su nasreen ya nufa, bayan sun gaisa ne take tambayar sa yasu abban jajere, kasancewar bata san yana cikin gari ba tun tuni, amsa mata yayi da suna nan cikin koshin lafiya, cen bayan sun dan taba hira ne, ya mike yace zai wuce saboda jirgin su ya kusan tashi, cikin shagwaba tace sweet baka kara min kudin ba, yace gsky nasreen kiyi hakuri saboda yanzu banda kudi, kinsan kaisa ma zatayi event so itama naje nabata nata kudin, cikin fushi tace ohhh wato kaje ka kwashe kudin ka bata kenan ni kuma ko oho ko, cikin mulki yace mata yanda na baki haka itama nabata so bana son mita pls, yayi gaba yabarta agun har ya isa mota baiganta ba, yacewa drivern ya jaa kawai sutafi, wato saboda ya hanata kudi shine yau baisami rakiyar da tasaba masa ba, kai nasreen kenan Allah dai ya shirya BABY ZAHRA [9:11PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 42 na BABY ZAHRA Acen abuja kuwa komai ya kan kama na zancen biki, abba shi da kansa ya raba amaren ko wacce in aka kawota ga gun wanda zata sauka, kasancewar abba yasan momy bawai tana son kaisa bane yasa yabata nasreen, yace in aka kawo nasreen komai na hidimar ta ita da kawayenta da en uwanta suna kan momy, ita kuma kaisa yabada ta wa er uwar ta aunty rukkaya, komai na hidimar ta yana hannun aunty rukkaya ne, so komai na bikin yana tafiya dai dai ba tare da ansami wata matsala ba...., za a daura auren kaisa ran Friday while ita kuma nasreen ran Saturday, don haka komai ke tafiya dai dai

Tun ranan talata ne akafara event in nasreen, mothers day sukayi anci ansha sannan kuma an chashe, sai dai ango bai sami hallartar event in ba cewa yayi shi sai ran alhamis zaizo,washe gari ranan laraba ne akayi family nd frnds day, shima dai kamar na jiya anci ansha kuma ancashe, amarya tayi rawa sosae, Ranan alhamis ne kaisa zatayi kamun ta wanda tayi shi a cikin garin jalingo, kamu yayi kyau amarya tafito sasoe gashi kuma ango ma da abokanan sa sun hallaci bikin,bai wani zauna sosae ba a filin yatashi yayi gaba. sakamakon kiran da nasreen take ta mai saboda itama ranan take kamun ta BABY ZAHRA [9:12PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 43 na BABY ZAHRA Bayan antashi daga kamun ne, suka koma gida dakin su suka shiga suka kwakwkwanta suna hutawa saboda gajiyar da sukayi....rukkaya kobi kawar kaisa ce da sukayi makaranta anan jalingo ita er Bauchi ce amma itama tana aure ne a abuja, ta zauna ne a gurin yayar ta anan jalingon kuma unguwar su daya dasu goggo indo, don haka mijin ta yasan su tare shiyasa ma bai hanata zuwa bikin kaisa ba, juyowa tayi tace qawata gsky kinyi sa an miji fa, wannan san talelen saurayi haka, gsky naji miki haushi da akace ku biyu zai aura naso ace ke kadai ce wlhy, amma duk da hakan dai ba wata matsala zan daura ki akan network ae, gashi ma Allah yasa gari daya zamu zauna, wacce unguwa ce ma zaki zauna, murmushi kaisa taya tace kai ke kam qawa Allah ya shirye ki wato haryanzu dai bakin nan tana nan ko, na so ace ae kamal yayi min maganin bakin nan, dariya suka yi dukkan su, rakiya ce tace ae sai an dan taimaka an dauraki akan network saboda ke innan da sauran ki anbarki a baya ae, sake shekewa da dariya sukayi, rukky kobi tace ke da Allah nikam gaya min a wacce unguwa zaki zauna, kaisa tace inaga a saraha estate ne, ihu rukky kobi tayi tace qawata ke dai kawai sai mun hadu, bari intashi inshiga gidan maman shazia kafin tafara nemana, tashi nayi narakata har kofar gida, najuyo kenan zan shige karo muka ci da shi sosae har sai da kirjina ya hadu da jikin sa, kasancewar ban kaishi tsayi ba, da sauri nace yi hakuri ya muktar wlhy bansan kana gurin ba, poster yayi don ko iya motsi baiyi ba, na ja jikina a hankali na barshi a tsaye a gurin, daki na shige nafada kan gado ruf da ciki kakkaurar ajiyar zuciya nayi, ni kaina naji awani abu, balle kuma shi, ae dolene ma yayi poster agun, tafadi hakan a ranta, bansan me ta tuna ba kuma sai naga tayi murmushi ta tashi ta zauna, rakiya ce tace mata ke kuma amarya lafiya nagan ki kina murmushi, ko dai kin tuna gobe yiwar haka kina gidan angon kine, gaban kaisa ne yayi mummunar faduwa, kuma hakane fa a she, innalillahi wa inna alaihirraji un ta furta shi a ranta ta dafa kirjin ta yana bugawa da karfi da karfi, ihu su rakiya suka sake, sai a lokacin ta tuna metayi, nan kuwa basu san mai yake damun taba tsaki tasake sannan tace lalle kukam baku da matsala wlhy, mameey yahya ce tace kema ae matsalar ki ta kare tunda gobe za akaiki gidan angon ki, tashi kaisa tayi tabar musu dakin abinta. BABY ZAHRA [9:12PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 44 na BABY ZAHRA Washe gari da sassafe ne muktar ya turo mota aka dauki su kaisa aka wuce da su jajere dukkan su, harda goggo indo da tawagar ta duk aka dunguma zuwa jajere,

Karfe 3:00pm dai dai na ranar jumma'a ranar da takama 02/01/2015, ne aka daura auren MUKTAR USMAN SHEHU JAJERE, da amaryar sa KAISA AHEAD MALAMI SHEHU JAJERE, akan sadaki naira #100k dubu dari, tunda aka daura auren ne ango da abokanan sa suke ta daukar hotuna, shi dai muktar baisan me yakeyi ba murna yakeyi ko bakin ciki shidai yasan ya tsinci kanshi cikin annashuwa, abokan sa sai tsokanar sa suke wai mai mata biyu, dariya kawai yake musu Misalin karfe 4:30pm amare suka shirya don zuwa gurin walimar da suka hada shi anan jajere, anci ansha sannan kuma an wa'azantu sosae domin kuwa malama juwairiyya ce tazo tun daga Bauchi domin bikin kasancewar ta kawar goggo indo ce, so tayi wa'azi mai ratsa jikin kowacce mace, bayan amare sun dawo ne sukayi sallah suka ci abinci, wayar ta ce ta hau ringing, ya muktar tagani baro baro akan screen in gaban tane yafadi tunda yabata wayar nan bai taba kiranta ba sai yau, a hankali ta danna received sallama tamasa ceen kusan 5sec kafin ya amsa yace ya gida tace lfyklw, yace to daman ba wani abu bane BABY ZAHRA [9:12PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 45 na BABY ZAHRA Daman kice wa duk wacce zataje abuja to gobe zasu wuce da sassafe misalin karfe 6:00am saboda su samu su isa da wuri don akwai DINA partyn da za ayi goben acen, amma banda ke,ke zamubi jirgin karfe 2:00pm insha Allahu, su dai ki gaya musu saboda su fara gaba, too kawai tace masa, bai kara ko 1sec ba ya kashe wayar sa bata tsamma nin ma ko yaji too inda tace in, cikin gida ta shige, gurin goggo indo taje tasanar mata da sakon ya muktar in, too fa goggo indo tace za ayi ta kenan saboda kowa zatace zataje amma bari inje in sami innarki sai muyi shawarar wa enda zasu, too nace mata sannan na koma dakin da muke nida kawaye na, sanar musu nayi da zancen tafiyar nan da nan suka fara shiri ba wasa, Washe gari kuwa Kamar yanda ya fadi 6 nayi sai ga motoci sun bai yana, ta window naji shi shida goggo indo suna magana, akan suyi sauri tafiyar basu kadai bane harda en gidan su nasreen ma, tun tuni ya tura musu mota don haka mu suke jira zasu tafi tare, amma banda kaisan don na yanka mana ticket uku ne ni da ita da nasreen, guda goggo indo tasake har sai da tasashi jin kunya tace wato mune 'ya'ya baabaa shine aka turamu amota zaka dauki matan ka kasaka su ajirgi kuyi gaba ko, sosa keya yayi yabar gun da sauri sai da ya isa bakin zaure sannan yace goggo don Allah muna jiran ku yanzu. Bakwai saura motar su ta tashi suka tafi ni daya ta aka bari a gidan, dakin inna ta na wuce nasame ta da sauran en uwa wa enda basu watse ba anan na zauna suka sakani a gaba da nasiya.. BABY ZAHRA

Share:

SAUYIN RAYUWA 36__40

sauyin-rayuwa.jpg

[9:11PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 36 na BABY ZAHRA Daga cen nesa ya hangota ta nufo inda ya ke hijab ne ajikin ta har kasa rungume da al Qur'ani a da wasu littafai a hannun ta da alamu dai daga makaran ta take, sai da tazo daf da shi har zata wuce sai kuma yaga alamar bata ganshi ba, cikin mulki da kasaita yace ke daga ina kike, Gaban tane yayi mummunar faduwa arazane tajuya don ganin mai wannan muryar, Allah Allah take Allah yasa ba wanda take zato bane.....ya ilahi ta furta acikin zuciyar ta, wannan kuma meya kawo shi nan kuma..... ya katse mata tunanin ta da cewa bada ke nakeyi bane, cikin bacin rai fuska ba wal wala tace daga makaranta, yace wacce makaranta kuma, tace islamiyya, gyaran murya yayi sannan yace zo ki dauki kaya a both, a hankali ta juya tare da shi suka jera zuwa gurin both in, yana nuna mata wa enda zata dauka, a hankali yace bakiji dadin ganina ba ko, shiru tayi bata ce mai komai ba, sannan yace to ai ni inma inda nasan zan zo insameki a nan da banzo ba, cikin tsiwa kaisa tace to ai yanzu ma bai baci ba zaka iya tafiya, a hankali yace to ae ba gurin ki nazo ba ko, kibari duk randa kikayi gidan kanki in kika ganni a gidan sai ki koreni amma yanzu nazo gurin uwata ce, har falon suka shiga suna gayawa juna magana, goggo indo ce tace ke kaisa ke da waye, lekowar da zatayi sukayi ido biyu da muktar tace ahhh lalle fa yaron abba Kaine a gidan nan BABY ZAHRA [9:11PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 37 na BABY ZAHRA Murmushi yayi yace eh wlhy goggo nine yau a gidan ki, goggo indo tace wato don kaji matar ka tana nan shine ka kwaso kafa kazo ko, yaushe rabon ka da gidan nan, cikin kunya muktar yace laaa goggo ba haka bane, hasalima niban san tana nan ba, a kofar gida muka hadu shine ta hada fuska tafara gaya min magana wai bata so zuwa na ba, goggo indo ce tace lallai agaishe ki kaisa, to gwanda ma kina sakawa kanki cewa mijin kine shi yanzu, kaisa ce tace wlhy goggo indo ba haka mukayi da shi ba.... cikin masifa yace dalla kiyiwa mutane shiru manya suna magana zaki sa baki, goggo indo ma ta biye wa muktar sukawa kaisa caaa aka, goggo indo ce tace maza tazo har gaban sa tabasa hakuri, baki zunbure ta taso tazo gaban sa ta tsugunna tace don Allah ya muktar kayi hakuri da abin da na maka.....sai wani shan kamshi yakeyi yana wani daga kai sama nan da nan mulkin ta motsa, da kyar ya iya cewa karki damu, tashi tayi ta shige cikin daki tayi kwanciyar ta BABY ZAHRA [9:11PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 38 na BABY ZAHRA Gsky zuwan ya muktar ba karamin takurawa kaisa yayi ba, yana zaune komai sai an masa, gashi goggo indo sai goya mai baya takeyi yana mata abinda ran shi yake so, Allah Allah take yasamu ya koma... Sallama akayi akofar dakin kafin suka shigo, da gudu ta tashi taje ta rungume su kawayen tane na skul suka zo mameey yahya da ruwaeda, bakin gado suka samu suka zauna, bayan sun gama gaisawa ne da dan tade taden da suka saba na skul, sannan suka mika mata kudin ashoben su daman abinda ya kawo su kenan, mikewa tayi tsam don taje ta dakko musu ashoben a dakin goggo indo, kicibiss sukayi da shi abakin kofar dakin ta, har sai da jikin su suka gogu da juna,hakan bakaramin fadar mata da gaba yayi ba, nan da nan ta hade rai, takama neman hanya ta gefen shi zata wuce, tare hanyar yayi shima ransa abace, yace ke wai bakisan yakamata bane da bazaki kawo min abinci naba, kanta akasa tace ae bansan ka dawo bane, yace tayaya za ayi kisan na dawo tunda kin sami wa enda suka fini kin bude musu baki kunata shashanci, ko kallon shi batayi ba balle tace mai wani abu gefen shi ta goga sannan ta wuce abinta, shekeke ya tsaya yana kallon ta, aaa lalle fa wannan yarinyar ta girma wato har tasan ta gogi jikin sa sannan ta wuce tabb lalle yarinyar nan zata sani, bari ta shiga hannuna zatayi bayani, ita kuwa kicin ta nufa ta har hada mai abincin nasa akan babban plat don haka goggo indo tace tana masa, wai tafara koya tun yanzu, a palour tasame shi shame shame Kamar wani mai jiran mai aikinsa takawo mai abinci, ajiyewa tayi a kan table inda yake gaban sa sannan tajuya zata tafi yace mata ke zonan BABY ZAHRA [9:11PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 39 na BABY ZAHRA Juyowa tayi batare da tadawo ba tace ya ne, yace zoki zuba min, nan take tace mai ina da abinyi yanzu, bata ko tsaya taji mai zai ce mata ba tayi gaba, bakaramin tashi hankalin muktar yayi ba wato har yakai stage inda kaisa zata fara masa rashin kunya, to insha Allahu yayi ma kansa alkawarin ba zai sake kulata ba koda abincin ne ya gwammace yana shiga kitchen shi da kansa yana dakko wa, insha Allahu yayi makansa wannan alkawarin,

Kwana daya biyu uku kaisa taga muktar baya ko kallon inda take, daga farko tayi farin cikin abun don ganin yanzu baya takura mata, amma daga baya kuma sai abin yadame ta gashi gobe wai zai koma abuja, kai wai menayiwa yaya muktar ne yayi irin wannan mummunar fushin da ni, tunowa tayi tayi metamasa na karshe, nan da nan gabanta yafadi sakanakon tuno da rashin kunyar da tamasa na karshe, kai gsky ban kyauta ba yakamata insa meshi in ba shi hakuri, to taya ya ma zan fara mutumin da ko murmushin shi na daina gani yanzu, yanzu ya koma asalin muktar usman jajeren shi, tana cikin tunanin nema sai taji sallamar sa yashigo falon da sauri tace sannu da dawowa ya muktar, bai ko kalli inda take ba balle ya amsa HANNU yadaga mata alamar ya amsa, nan da nan gaban ta ya fadi tace tabb ya muktar an koma DA kenan, kai tsaye kitchen ya wuce yakama zubama kansa abinci da sauri tazo tasame shi tace yaya kawo in saka maka, kai kawai ya girgiza mata, bakaramin tashi hankinta yayi ba fatan ta daya shine kar goggo indo tazo tasame shi a kitchen shi da kansa yana debawa kansa abinci, ai bakaramin tashin hankali yajawo mata ba. BABY ZAHRA [9:11PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 40 na BABY ZAHRA Binshi takeyi a baya kamar jela suka sake komawa falon, yana zama itama ta zauna shiru shiru ba wanda yacewa kowa kala har sai da yagama sannan yayi gyaran murya yace meye da meye zakiyi na event in bikin ne, a hankali tace walima zanyi, yace to ga wannan 300k yaba ta kamar yarda yabawa nasreen,arazane ta kar bi kudin wannan uban kudin me zatayi da shi, cikin sauri ta dan zari kadan aciki tace masa ga wannan karike, wannan ma ya isa, bambarakwai yaji abin abinda baisaba ji agurin nasreen ba, amma sai yaci fuska bai gwada mata kamar yaji mamaki ba, ko kallon ta baiyi ba balle yasan me take fada, yaci gaba da bude ledar da ke gaban sa, waya ya ciro a kwalinta ya mika mata tasaka hannu ta karba cikin murna da farin ciki tace nagode YAYA NA! Wani yarrr yaji ajikin sa da sauri ya kalleta yaga ita bata Masan ta furta wannan kalmar abakin taba, har cikin ransa yaji dadin kalmar, sai kuma wata zuciya tace mai to meye nawani jin dadi don yarinyar da baka SO takira ka da yayanta ga nasreen inka nan tana kiran ka da sweeet ma ba wani yayan ta ba, tsaki yayi acikin ransa ya mike yafita, bude wayar tayi TECNO PANTOM ce da gudunta ta shige dakin goggo indo ta dira akanta tana ihu da sauri goggo indo ta tashi tace ke lafiya, kefa baki da hankali wataran mika mata wayar tayi da sauri tace ya muktar yasai mun waya, eyye goggo indo tace a'a gsky waya kam yayi kyau ina shi muktar in yake tace yafita yanzu, sake miko mata kudin daya bata tayi tace gashi wai yaban inyi event da shi, ni inaganin kamar kudin yayi yawa ko

Share:

SAUYIN RAYUWA 31__35

sauyin-rayuwa.jpg

[9:11PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 31 na BABY ZAHRA Cikin murna da zumudi ta tashi ta zauna sosae Dr Adam ne da falmata suka shigo da sauri nasreen ta fincike karin ruwan ta tashi da gudu taje ta rungume falmata tace mata nagode falmata da shawarar da kika ban gashi har mai Martaba ya amince da bukata na, nagode sosae sosae, ta juya takalli Dr adam tace mai nagode kaima Dr naji dadin abinda kamin, tajuya ta kalli falmata tace kibude site drawer zakiga kudi kibawa Dr, da sauri falmata tace to, ta dakko mai kudi mai tarin yawa, wanda ita kanta nasreen in batasan nawa bane a gun, aka mika mai, godiya yayi sosae Kamar zai yi mata sujjada don murna, ta sallame shi yayi tafiyar sa....haka nan dai fulani tayi hakuri da zancen auren nasreen da muktar ta dangana abin a matsayin kaddara don haka aka ci gaba da shirye shirye Tsakanin gidajen uku ko ina shirye shirye akeyi ba kakkautawa, kasancewar dukka 'ya'yan fari za a aurar..... Akwana atashi har biki saura sati biyu don haka shirye shirye sai ci gaba takeyi........ Haka kawai yau yatashi yaji yana dan kewar kaisa ko meyasa haka oho, dan zaman da yayi a jajere yasa yadan saba da ita amma ba sosae ba don ma dai kullum fada ne ke hada su, to amma bari dai yagani ko zai iya shiga jalingo yau, wayar sa ya dauka yakira ahmad abokinsa ne dake aiki a airport bayan sun gaisa ne yake tambayar sa ko zan samu ticket in jirgin da zanje jalingo da safen nan, acen bangaren Ahmad ne yace mai kar ka damu abokina zaka sami na karfe goma 10:00am, farincike ne yakama muktar yace to shikenan bari in shirya ina zuwa, sannan yakashe wayar yashige wanka. BABY ZAHRA [9:11PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 32 na BABY ZAHRA Tsaff ya shirya bai ko gayawa kowa zaiyi tafiya ba sai da yagama shirin sa ya dakko kayan sa sannan ya sakko kasa su abba yagani dukka su suna zaune ya gaggaishe su bayan sungaisa ne, ya dubi abban shi yace abba yau ina son in je jajere fa, abba yace lafiya zakaje tafiya ba shiri, murmushi muktar yayi yace ina sone inje saboda inji ko kaisa tana da matsala na kudi, kuma bata da waya balle muna communication da ita, shine yau nashirya nace bari dai inje inji, nan da nan abba ya wangale baki yana dariya dadi ya kama shi, nan da nan yakama sakawa muktar albarka yace ubangiji Allah ya kaika lafiya ya kuma dawo da kai lafiya idan kaje ka gaida min da dan uwana sosae sosae, to abba zasuji insha Allahu, nan kuwa idan ran momy yayi dubu to ya bace, me yaron nan yake nufi da zaije duba kaisa, karfa yace min yakamu da son yarinyar nan ne, ko kuma dai maganar abba gsky ne dayace shi yazo yace masa yana son kaisa shiyasa yabashi ita, lalle kuwa zanci masa mutunci, bari yaje ya dawo, abba ne ya katse mata tunaninta da cewa yanzu sai yaushe kenan zaka dawo, yace eto abba inaga dai bazan yi sati ba, saboda nima inzo inkarasa nawa shirye-shiryen anan, toto shikenan ae cewar abba to Allah ya kiyaye hanya ko agaggaishe su, yace amin, yace to momy, aunty nikam natafi!!! ,ba aunty rukkaya ba harta su momy sun sha mamakin yanda akayi yau kuma muktar yayiwa aunty rukayya magana kuma cikin lafazi mai dadi, to Allah ya kiyaye maka hanya muktar agaida mun da su innan kaisa, cewar aunty rukaiya, insha Allahu ya fada cikin nishadi, yakee momy tayi tadan saki fuska tace agaida min da surkata sosae sosae, gashi banda abu yanzu ai dana baka ka kaimata, kai innema da tafiya ba shiri, ko dai ita tayi kiran ka ne, kowa afalon sai da yayi dariya, sannan tace to Allah ya kiyaye hanya ko agaggaishe su sosae, to insha Allahu yace mata sannan suka rakashi har bakin motar ya shiga driver yaja suka tafi BABY ZAHRA [9:11PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 33 na BABY ZAHRA Misalin karfe 11:00am yana zaune a falon karbar baki na gidan su nasreen, soyayyar su suke ci sosae, sai zuba masa shagwaba take, tana narke a jikin sa, abinda yasa muktar yake kara son nasreen kenan saboda yana son mace mai shagwaba gashi nasreen inshi ta iya sosae, shiyasa yake Allah Allah sati biyun nan yayi saboda yasamu ya mallaketa har abada..... agaban sane yayi mummunar faduwa sakamakon tunowa da kaisa da yayi, baisan me yasa ba kwana biyun nan idan har yatuno ta sai yaji bagan sa ya fadi, cikin sauri ya janye jikinsa daga na nasreen, a hankali tace masa lafiya kuwa yace a'a lafiya kalau, kawai na tunone da aikan da abba ya ban, ya kamata in wuce jajere ne yanzu, cikin shagwaba tace haba mana sweet kabari sai da yamma, cikin kasaita yace wlhy nima naso hakan amma bazai yuyu ba, yanzu abinda za ayi kisa afitomin da motar ki da ita zan wuce, too kawai tace mai tayi waya tasa aka fito da motar, dubu dari biyu 200,000 yabata yace ga wannan kifara rage abubuwa da shi ina ce kince event hudu zakiyi tace ehh yace to ga wannan, tasa hannu ta karba tace sweet nawa ne a nan yace 200k ne tace gsky sweet ba zai wani isa ba event hudu fa, ya saka hannu a aljihunsa ya karo mata 100k yace to ga kari, ta karba tace to za dai afara managed insa amma shi inma ba isa zaiyi ba, ajiyar zuciya yayi abinda yake hada shi da nasreen kenan tun ba yauba ita a rayuwar ta bata iya godiya ba sai ma raina ko, sannan yace mata to shikenan ni kuma yanzu banda wani kudi a hannu na, sai naje bank don haka yanzu kam sai na tashi dawowa, too kawai ta ce mai ta tashi taraka shi har bakin motar sannan yatafi BABY ZAHRA [9:11PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 34 na BABY ZAHRA Karfe 2:00pm dai dai acikin garin jajere yayi mai, kasancewar bai sanar da kowa da zancen zuwan san ba, kai tsaye ya shige cikin gidan sallama ya kwada da gudu su nana sukazo suka rungume shi suna ga yaya muktar ga yaya muktar inna ce tafito tace aaaa lale marhaban da ba kon abuja, bismillah shigo ciki ko, da sallama ya shiga dakin ya nai mi guri a kasa ya zauna ya mika mata gaisuwar sa baisan meyasa ba yanzu kwata kwata kunyar inna yakeji, bai saniba ko don ta kusan ta dawo surukar sace oho, abinci inna ta kawo mai ta ajiye masa sannan ta juya tafice waje ta zauna saboda inna akwai kunyar nan tamu ta fulani balle kuma yanzu da take mai kallon surukin ta, sai sa ido yakeyi don yaga ta ina kaisa zata bullo amma yaji shiru ba ita ba labrin ta, cen dai ya dan rage murya yace nana ina auntyn ki take, tace ai aunty kaisa ta dade da tafiya jalingo gurin goggo indo, goggo indo ce tace wai za ayi mata wasu en gyararraki kafin ayi mata aure,yaya muktar inace zaka zo auren aunty kaisa ko, da sauri ya to she mata baki ganin tana maganar da karfi kar inna ta jiyo ta,saboda nana irin yaran nan ne masu shegen magana fadi ba atambaye kaba duk ta iya shi, kuma kwata kwata shekarunta hudu ne a duniya,da sauri yace ehh zan zo mana nana, wai gyara akaje ayi mata a jalingon, da sauri nana tace ehh wai gyaran biki za amata, wani munafurtacciyar murmushi muktar yayi wanda ni kaina na gagara gane me wannan murmushin ke nufi BABY ZAHRA [9:11PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 35 na BABY ZAHRA A gaggauce yaci abincin shima yacine don baya wuce tayin inna saboda dadin abincin ta, a hankali yafito daga dakin, inna ce tace bari insaka agyara maka cen dakin ko, da sauri yace a'a ai inna daman nashigo ingaishe kune, amma yanzu zan wuce, abban baya nan ne, inna tace ai abba ya tafi yola yau amma gobe zai dawo, da ka tsaya kajirashi ya dawo ae, amma kace wai zaka wuce, yace ehh wlhy inna akwai aikan da abbana ya bayar in kaiwa goggo indo ne, to ina ganin idan naje ta gidan tan zan kwana zuwa washe gari sai in wuce, inna tace ohh to ae shikenan, inkaje cen ma kwa hadu da kaisan acen don itama ta dade da zuwa cen in, fuska yaci sannan yace owk to shikenan, nidai zan wuce, inna tace to Allah ya kiyaye hanya, yaciro kudi mai tarin yawa yabawa nana yace babyna gashi kije kisayi alawa ko, yabata ne saboda yasan inya bawa inna bazata karba ba, har bakin mota su nana suka rako sa, yashiga yaja yatafi sai garin jalingo, bai shigo garin ba sai misalin karfe biyar na yamma 5:00pm sannan yashigo garin kai tsaye gidan goggo indo ya nufa, sai da ya isa dai dai kofar gate in gidan sannan ya tsaya, yakama tunani to wai meyasa ma na biyo yarinyar nan ne, wai me nake nufi da hakan, kaii karfa yarinyar nan ta raina ni fa taga kamar ita na biyo, kwana yayi da kan motar sa da niyar zai koma, sai kuma me.....zuciyar ce ta gagara tafiya don bazata iya tafiya batare da taga fuskar kaisa ba, kan starring motar ya buga da karfi, gsky bansan me yake damuna ba kwana biyun nan akan wannan kucakar yarinyar BABY ZAHRA

Share:

SAUYIN RAYUWA 26___30

sauyin-rayuwa.jpg

[9:11PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 26 na BABY ZAHRA Sallamar ta ne ya katse mai tunanin sa, a hankali ta ajiye mai kular abincin a gaban sa, har ta juya zata fita yace mata zonan cikin nutsuwa ta dawo ta zauna, ya ce mata kaisa ni sa'an ki ne? A'a kawai tace masa, yace to amma meyasa kika rai nani ko don kinji ance miki ni zan aure ki shiyasa kika bi kika raina ni, cikin nutsuwa da fahimtar juna yake mata maganar, bata ce masa komai ba har sai da tabari yagama maganarsa sannan tace haba ya muktar yanzu don kawai ance min kai zaka aure ni sai kawai in raina ka ae yanzu ne ma yakamata in girma maka ta yanda baka zato, indon ban kawo maka abinci da kaina bane yabata maka rai to don Allah kayi hakuri, insha Allahu irin haka bazai kuma faruwa ba, shiru kawai yayi yana mata wani mugun kallo wannan yarinyar ko duk yanda ka kai da bacin rai tasan ta yanda zata shawo kanka da kalamai masu dadi nan da nan kaji zuciyar ka ta kariya, sai yace mata to ina son kimin wata alkawari guda daya, cikin sauri tace ya muktar inajinka indai har baisabawa addini ba ni kuma namaka alkawarin koma meyene zan maka shi matukar zai faranta maka rai, yaji dadin kalaman ta ba na wasa ba, sannan yace ina son kimin alkawarin baza ki sake tsayuwa da wannan saurayin naki ba, saboda kinga abban ki baya son kina tsayuwa da shi don haka sai ki kiyaye bacin ran abban ki, BABY ZAHRA [9:11PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 27 na BABY ZAHRA Ni kinga gobe in Allah ya kaimu zan koma abuja kuma jirgin karfe 9:00am zan bi, don haka zan bar nan da safe, cikin nutsuwa tace insha Allahu na maka alkawarin bazan kuma tsayuwa da shi ba amatsayin saurayi da budurwa, sannan kuma Allah ya kiyaye maka hanya, inka isa ka gaidamin da su zahra, yace to zasuji, tashi kije.... A hankali ta tashi tayi fucewar ta, binta kawai yayi da kallo yace a ransa wannan yarinyar inda namiji ce ita bakaramin yaudara zatayi ba saboda kalaman bakinta masu dadi, gsky kalaman ta sunyi gashi kuma.........yayi sauri ya kawar da tunanin ta daga ransa... Washe gari da sanyin safiya yatashi ya kammala komansa yashiga cikin gidan yasamu abba ya sallame shi ya sallami inna ya dakko kudi mai yawa yabawa inna taki karba shi kuma ya ajiye mata akasa adakinta yayi fucewar sa waje, kicibuss sukayi da kaisa a dai dai zauren gidan, ina kuma kikaje da safen nan ta sunkuyar da kanta kasa sannan tace mai naje sayo kosai ne, yace meyasa baki aiki su nana ba bana son yawan yawo fa, ooh su muktar akwai son iko da mutum, a hankali tace mai lokacin basu tashi a bacci bane, kuma nayi saurin zuwa ne saboda in kawo maka kasamu kaci kafin kafita ashe ma har ka fito, yaji dadi sosae saboda kaisa tana bala'in kula da cikin sa ta yanda baya zato ko shi bai kula da cikin sa Kamar yanda ita take kulamasa da cikin sa, dan murmushi yayi yashafa gen fuskarta yace karki damu inna je gidan su nasreen zanyi breakfast, wani yarrrr taji tundaga kanta har zuwa tafin kafanta, sakamakon shafa fuskarta da muktar yayi BABY ZAHRA [9:11PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 28 na BABY ZAHRA Wucewar sa yayi baima san yayi ba, tana tsaye a inda yabar ta har saida abban ta yazo wucewa ne kafin hankalin ta yadawo jikin ta, da sauri ta fice kofar gida tasamu harya saka kayansa a bayan both suka iso inda motar yake ita da su abba suka mai sallama ya shiga motar suka dagawa juna hannu yayi kwana da kan motar yatafi sannan suka shige cikin gida... Zaune yake akan kujera 2 setars nasreen ce kwance akan kafadar sa sai zuba masa shagwaba takeyi yana ta faman lallashin ta, da kyar ya kwaci jikinsa anata saboda karyayi missing flight ganin har 8:30am ya wuce, da kyar suka rabu sai a hakan ma sai da yayi mata alkawarin next month zai zo, harda ita a en rakiya har airport suka rakashi sai da sukaga tashin jirgin su kafin suka koma gida... * A cen abuja kuwa shirye shirye ake tayi bana wasa ba ana wancen ana wancen duk na shirye shiryen bikin muktar, gida abba ya gina masa manya guda biyu a hade gidan suke gate zaka gani guda biyu irin daya komai na gidan iri daya ne, daya na kaisa daya kuma na nasree , su momy ba shiga ba fita ta gama gayawa kawayen ta matan manya kaf akwai auren shalelen ta, bakincikin ta daya ashine auren nan harda kaisa BABY ZAHRA [9:11PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 29 na BABY ZAHRA Duk farincikin da takeyi daga zaran ta tuna auren nan har da kaisa aciki sai taji ranta yayi mummunar baci tsaki taja sannan tanemi gu ta kwanta...momy kenan Tunda sakon auren kaisa yasami goggo indo, take ta shirye-shirye ba kakkautawa, tayi murna sosae dajin cewa kaisa muktar zata aura, tunda taji su biyu za a hada su sannan taji wancen in er sarki ce, shikenan kuwa goggo indo ba zama, duk wani kaya datasan anawa yarinya er gata to sun hada karfi da karfe ita da abban abuja sun ma kaisa ko su momy basu san iya kudin da abba yabayar don ayiwa kaisa kayan daki ba, kasancewar dakunan ta guda uku ne to haka aka cika mata su da kaya tamm gado uku aka mata kuma dukka royal bed ne, parloun ta kuwa wasu luntsuma luntsuman kujeru aka saka mata,ga TV nan plasma LG, anythings dai da ake sakawa a palour to sun saka mata, dayake auren nagida ne, ana siyan kayan direct gidan ake kaiwa ko muktar in bai sani ba balle su momy, abba ne da goggo indo suketa kaiwa da komowar su, don haka ko su kaisa ma basu san abinda ke tafiya ba abban jajere ne kawai yake sane da abinda ke tafiya, kayan kitchens kuwa ba irin wanda goggo indo bata siya mata ba matukar muna amfani da shi a gida Nigeria, saboda kitchen in nata babba ne sosai, shiyasa sukaji dadin cika kaya aciki, gida yayi kyau nagani nafada, mata kawai yake jira....Allah dai yakaimu lokacin auren nan BABY ZAHRA [9:11PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 30 na BABY ZAHRA Kwance take shame shame har da karin ruwa na karya da ake saka mata, mai martaba ne da fulani da waziri da Dr adam akan ta, Dr adam ne ke musu bayani, gsky ranka shi dade yarinyar nan tana cikin hatsari fa, ya juya ya kalli fulani yace ranki shi dade shin ko akwai abinda yake damun gimbiya ne, shiru fulani tayi, Dr adam yaci gaba da bayani gsky to zuciyarta yana gabb da harbuwa, sakamakon yawan tunani da takeyi, inda hali yakamata a kwantar mata da hankali don samun kwanciyar hankalin zuciyar ta, ko zai daina harbawa da sauri da sauri, maimartaba ne ya juya ya kalle fulani yace mata ko kinsan abinda ke damun 'yata, a hankali momy tace masa a'a yace to abamu guri da ita zamu gana, kowa da kowa ya fita yabasu guri zama yayi abakin gadon yakamo hannun nasreen yace babyn daddy me yake damun ki, hawaye ne ya gangaro ta gefen idanun ta, maimartaba yace a'a banna son kuka kawai kigaya min meke damun ki, a hankali ta budi baki cikin murya irin na marasa lafiya tace daddy fulani ce tace wai bazan auri muktar ba ni kuma shi nake so, cikin shagwaba ta furta maganar, daddy yace bangane bazaki aure shi ba saboda me, nasreen tace wai don saboda anmishi alkawari da wata er uwar sa, shine akace mai sai dai ya aure mu tare, da nima ban yarda ba to amma daya min bayani shine na yarda naso in fahimtar da fulani amma taki sai fada take min wai tun kafin inshiga gidan shi wai harya min kishiya, murmushi maimartaba yayi sannan yace ki kwantar da hankalin ki bbyn daddy auren ki da muktar kamar anyi angama ki watstsatsake ki fara shirye shiryen bikin ki nan da sati shidda 6weeks in Allah ya kaimu,cikin jin dadin abinda daddy yafada nasreen ta hau dariya tana godiya wa daddyn ta har ta mance da zancen wani ciwo, girgiza kai kawai daddy yayi yatashi yafito BABY ZAHRA

Share:

SAUYIN RAYUWA 20___25

sauyin-rayuwa.jpgsauyin-rayuwa.jpg

[9:10PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA page 20 na BABY ZAHRA Dawowa tayi cikin nutsuwa, tasamu guri ta zauna, yana cin abincin sa yace kaisa tace na am yace kinsan me nake so da ke tace a'a yace inace kina son saurayin ki iron nan ko, cikin sauri tace mai eh, yace to nima ina da wata wanda nake so kuma ita nake son aura, kinsan me nake so da ke, tace a'a kisami abban ki kice masa ke bakya sona kina da wanda kike so, idan yaki ki masa kuka sosae kice masa ke bakya sona, saboda ke kinsan ni ba tsarar auranki bane, idan kikayimin haka to ni namiki alkawarin zan samawa iron kin aiki a jalingo inace kince yayi diploma tace ehh ya ce to zan Samar masa aiki a cen inyaso sai kuje cen ku zauna, tunda yafara maganar sa batace mai komai ba sae da tabari yakaraci zancen sa kafin tace mai, naji abinda kace ya muktar, amma kasani ni ina da tarbiyya kuma ina da biyayya don haka bazan iya samun abbana ba, ae Kaine babba don haka Kai kasami abban ka kagaya masa cewa baka sona, inyaki sai kamasa kuka kadaga masa hankali inyaso sai yace yafasa,da kake zancen soo kuma kai shaida ne ni bana son kamar yanda kaima baka sona, biyayya nayi nakarbe ka amatsayin kaddara, sannan kuma bakayi karya ba da kace ni ba tsarar auren ka bace saboda ni miji mai addini nake nema nagari wanda yasan mutuncin 'ya mace da kimarta, wanda yake biyayya wa iyayen sa,don haka ni ban damu da namiji dan boko ko wayayye ba, da kake zancen zaka samawa iro aiki ce maka akayi baya aiki ko mai, a hakan da ka ganshi yana da arzikin da zai ciyar dani ya tufatar da ni, alhamdulillah a hakan nake son shi kuma inza abarni zan aure shi, amma ni banna son kyalkyal banza, kuma ni inda zaka je kasami su abba da maganar nan da ka taimake ni ba kadan ba, domin nima banna son ka biyayya zanyi, kaga tafiya ta BABY ZAHRA [9:10PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA page 21 na BABY ZAHRA Poster kawai yayi yasake baki yana kallon kaisa, wai wannan yarinyar dama tana da baki ashe har zata iya duban tsabaragen idon sa tace zata gaya mai irin wa ennan magan ganun lalle agaishe da ita, ko da shike ba laifin ta bane laifi nane da nasake mata hartake gayamin irin wa ennan magan ganun, daga yau na daina sake mata fuska, wata kakkaurar ajiyar zuciya yayi yadan kishingide akan gadon, wayar sa ce ta hau ruri da baiso dagawa ba, sai ya duba yagani ashe momy ce da sauri yadaga ,tace mai kai muktar kar kayiwa kaisa maganar nan, ashe abban ka yaji abinda nagaya naka har yayi mummunar fushi da ni, da sauri yace ae nikam harna gaya mata ma ae momy, cikin daga murya momy tace shikenan ka kashe ni, me tace maka yace bata yarda ba tace bazata fada ba, zagina ma tayi, tayi gaba abinta, momy tace to alhamdulillah, gwanda da tamaka hakan, da sauri yace gwanda da tamin haka kuma momy, momy tace iyyi gwanda ta maka hakan, ina ce ba marinka tayi ba, yace ehh tace to ai zagi baya tabo, yace momy nifa ban gane me kike nufi ba, momy tace bazaka gane ba kuwa kabari sai kadawo zamuyi magana, nidai abinda nake son ingaya maka dai yanzu kasan yanda za ayi ka lallaba kaisan kurabu lafiya, yace in lallabata fa kika ce mom, momy tace eh ka lalla bata, muktar yace gsky momy bazan iya ba, cikin fada momy tace sannu muktar wato har kayi girman da ina fada kana fada ko, to bari ingaya maka wata abinda baka sani ba, shine aure na yana shirin mutuwa akan auren ka da kaisa, in anyi in zauna in ba ayi ba inyi garin mu!!! BABY ZAHRA [9:11PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA page 22 na BABY ZAHRA Gaban sane yayi mummunar faduwa yace momy bangane ba, tace eh haka dai ubanka yace, salati yasake yace momy ki kwantar da hankalinki insha Allahu za ayi auren nan, ae wannan ma abu ne mai sauki don dai aure kawai, momy tace to in akayi ka ceci aure na in kuwa ba a yi ba kai kayi sanadiyar aure na, noo momy baza ayi hakabama insha Allahu, kashe wayar ta tayi domin kwana biyun nan hankalinta baya jikin ta, bakaramin tashi hankalin muktar yayi ba da jin wannan maganar, yanzu ashe abin haryakai haka da har abba zai furta irin wannan mummunar kalmar akan momyn su zazzafar ajiyar zuciya yayi, ya mai da kansa kan filo ya kishin gide ya shiga kogin tunani kala kala. Kuka takeyi sharshar da hawayen ta, tadaga manyan idanuwar ta tace fulani gsky ni bazan iya rabuwa da muktar ba yaza ayi don kawai yace zai aure mu mu biyu shikenan kuma sai kice ae baya sona ne, wlhy ni ina da yakinin muktar yana sona yanda bakya zato, shima dai abin yafi karfin shine babu yanda ya iya shiyasa ya karbi yarinyar a matsayin kaddara, dalla rufemin baki! cikin tsawa fulani ta ke maganan daya ke bakisan mutuncin kanki ba shiyasa kike furta irin wanna kalaman daga bakin ki BABY ZAHRA [9:11PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 23 na BABAY ZAHRA Kuka nasreen tasake sosae kamar ranta zai fita, fulani ce cikin tsawa tace tashi ki fitamin adaki ko in ci ubanki! da sauri nasreen ta tashi tafita gefen ta ta wuce cikin sauri, kan gado tafada ruf da ciki tana ta kuka mai tsuma rai, kuyan gunta ne suka tsaya tsuru tsuru suna kallon junan su anrasa wanda zai shiga uwar dakin ta ya rarrashe ta, falmata ne tayi karfin halin shiga dakin kasancewar itace amintacciyar kuyangan ta, a hankali ta karaso inda take tare da cewa ranki shidade gimbiya lafiya kuwa, da sauri nasreen ta tashi tace falmata fulani tana son ta rabani da muktar intarabani da shi bansan inda zan saka rayuwa ta ba wai don kawai zai aure mu mubiyu ni kuma nace ehh na yarda amma wai fulani bata yarda ba cikin kuka take maganar, dasauri falmata ta zauna bakin gadon ta tallafo kafadar nasreen tace ranki shidade insha Allahu baza ayi haka ba, ki kwantar da hankalin ki nasan yanda za ayi hajiya ta yarda, da sauri nasreen tace kamar yaya falmata, kasancewar falmata itace mai bawa nasreen shawara kuma bata taba bin shawarar ta taga ba dai dai ba don haka tana gab dajin tabakin falmata, falmata ce tace hadin kanki kawai zaki ban, domin nan da kwana biyu zanje incewa hajiya baki da lafiya, ke kuma sai ki kira Dr adam ku dai dai ta dashi inyaso sae muyi karyar zaki kamu da ciwon zuciya in har ba abaki wanda kike so ba, nasan hajiya najin hakan zata amince BABY ZAHRA [9:11PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 24 na BABY ZAHRA Daddadar ajiyar zuciya tayi, ta rungume falmata abinda yasa take son ta kenan saboda akwai ta da bawa mutum shawara nan da nan, tace to yanzu abinda za ayi ko bari inkira Dr adam in yanzu sai in tsara masa yanda za ayi, wayar ta falmata ta miko mata tasaka hannu ta karba ta daddan na numbers in shi ringing biyu yayi ya dauka, bayan sun gama gaisawa ne ta karanto masa abinda ke faruwa da kuma wanda take da bukatar yayi mata, baiyi wata wata ba ya amince kasancewar shine family Dr su kuma sunyi da shi akan duk kudin da akabayar na magani yarike an bashi, bakaramin murna yayiba da jin wannan zancen, don haka sun bar abin zuwa jibi... Acen jajere kuwa muktar duk ya zaku gobe yayi saboda a gobene yake son komawa abuja, daga bakin kogi yake yana tafiya a hankali cikin kasaeta da nuna kamar hanyar na gidan sune, daga cen ya hango ta suna ta hira harda da dariya, da saurin sa ya iso inda take cikin tsawa yace mata ke wai bakya jin magana ne, ke wai mara hankalin inane, jikin kaisa ne ya hau rawa tace wlhy yaya inagaya masa ne kar yasake kulani donni yanzu anmin miji, yace dallah rufemin baki shine naga har da dariya, zaki wuce ki ban gurine ko sai na wanka miki mari, da gudun ta ta wuce tayi hanyar gida, juyawa yayi cikin bacin rai yace kai idan nasake ganinka da yarinyar nan sainayi mugun bata maka rai wlhy, IRO baice mai komai ba yayi gaba kawai abinsa, tsaki muktar yayi tare da cewa kazami kawai, sannan yasaka kansa gaba ya nufi hanyar gida BABY ZAHRA [9:11PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA. page 25 na BABY ZAHRA Yana shiga ya tura nana tayi masa kiran ta, da sallamar ta tashigo jiki a sanyaye saboda tasan me ta aikata,tsoronta daya ma shine kar ya gaya wa abban ta, tana shigowa tanemi guri ta zauna tace yaya gani, ko uhumm bai ce mata ba balle har ya kula ta, suna zaune a hakan sai da sukayi kusan 30mnt tun tana zaune akan kafarta harta gaji tanemi guri ta zauna, kaiii cen dai har ranta yafara baci, kuma ba abinda yafi bata mata rai kamar ko ya daga ido ya kalle ta yanata daddana wayar sa, ranta ya kai kololuwa gurin baci, a fusace ta tashi zata fita, da sauri yace inkin fita ki kawomin abinci, kuttt lalle agaishe da ya muktar wato daman bawani abu bane yasa yayi kiranta ya kirata ne don yayi mata rashin mutuncin shi daya saba, shiru tayi ko ta amsa, takama hanya ta fita, ceen dai yaune gobe ne ba kaisa babu dalilin kaisa yana zaune agurin yana zaman jiran dawowar ta amma yaji shiruu, yana zaune agurin tsawon 40mnt kafin sai ga nana takawo masa abincin, ranshi idan yakai million to ya bace, cikin tsawa yace wa nana kee ina kaisan take, da sauri tace tana cikin gida, yace ki mayar mata da abincin kice mata ta kawomin ita da kanta, da sauri nana tajuya ciki, ranshi yagama baci harya kullatawa zuciyarshi cewa tana zuwa sai ya wanka mata mari saboda shi ba sa anta bane, sai kuma wata zuciyar tace kai fa kafara mata hakan inda baka mata ba, da itama bazata maka ba, kan gadon ya buga wai meye yake faruwa da nine nasakewa yarinyar nan dayawa duk wata hanya da zata sa ta rainani nariga da nabi wannan hanyar, kuma ko ya kirata daniyar yi mata fada amma sai ya gagara tana da kwarjini sosae a idon sa..... Sallamar ta ce ya katse mai tunanin sa BABY ZAHRA

Share:

SAUYIN RAYUWA 16__20

sauyin-rayuwa.jpg

[9:10PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA page 16 na BABY ZAHRA Hakince suke a dakin baki,muktar da nasreen bansan wayafi wani iya mulki da sarauta ba, suna zaune sai zubawa junan su mulki sukeyi,kuma ahakan soyayya sukeyi sosae don har wani shagwaba nasreen ke wa muktar, cikin faduwar gaba muktar yace wa nasreen sweet kinsan kuwa da yaya abbana ya yarda yazo yamin tambayar ki, tadan gyara zama tace a'a sai kafada yace in gaya miki da kyar yazo , ko kinsan meyasa tace a'a saboda wai ya bani mata er kanin sa anan jajere, subhanallah cewar nasreen yabaka matafa kace cikin kasaita yace mata eh!!! Nasreen tace yanzu ya akayi kenan yahakura, yace mata waaa ae ba hakura yayi ba, sharadi ya gindaya min kafin yazo, tashi tayi sosae ta zauna daga kishingiden da tayi tace sharadin me kenan, cikin isa da mulki muktar yace cewa yayi sai dai in hadaku ku biyu dukka in aura arana daya!!! Zumburr tamike tsaye tace bangane ba muktar kana nufin tunkafin inshiga gidan ka harkamin kishiya, to kuwa bazai yuyu ba gsky ba zata taba sabuwa ba, er ni innan ace wai har anmin kishiya gsky inaaa, cikin nutsuwa muktar ya mike tsaye yace ashe daman bakya sona nasreen, saboda irin son da nake mikine fa yasa na karbi auren wancen yarinyar da bata dace dani ba, saboda abbana yace in har ban yarda da auren ta ba, to kema insakawa raina munrabu kenan, ko ance miki ni ina son ta ne, kenake so nasreen, nasreen ke nake so, jikin nasreen ne yayi sanyi tajuya ta kalli masoyin ta, tace nima ina sonka muktar amma bazan iya jurar ganin wata tana taraiya da kai ba, cikin muryar kuka ta furta maganar, nan da nan tasaki kukan da ke makoshinta, da sauri muktar yazo ya riketa yace ki kwantar da hankalinki nasreen ni nakine ke kadai, ko an aura min kaisa kisakawa ranki cewa ke kadai ce agurina, namiki alkawarin babu abinda zai shiga tsakanina da ita na aurataiya, wani daddadan sanyi ne ya ziyarci zuciyarta wanda har yasa bata san sanda ta rungumeshi kam ajikinta ba, kusan 15mnt suna haka, muktar ne yayi kokarin janyeta daga jikinsa, gudun karya shiga wani hali BABY ZAHRA [9:10PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUW page 17 na BABY ZAHRA Dakyar suka rabu da juna, sun rabu akan zai sake dawowa, shi da kanshi ya koma da motar akan sai randa zai koma abuja zai dawo da ita, a hanya ne wayar momy ta shigo, a hankali ya dauka sallama yayi mata amma ko amsawa batayi ba ta haushi da fada, gefen titi yasamu yafaka motar don sauraren abinda mahaifiyarshi ke kunshe da shi....... Kana jina ko muktar yanzu ashe mani zaka watsawa kasa a ido karasa wacce zaka aura wai sai kaisa, kuma yaushe kafara neman kaisa a gidan nan ni ban sani ba, da har zakace wai zaka aure su su biyu kana hauka ne, ta inda take shiga ba tanan take fita ba, sai da tamasa tatass yana shiru baice mata komai ba, sai da takai aya sannan yace to ni momy ninace miki ina neman kaisa, abba ne fa yace saina aure ta na dole nima naso inbijire masa shine yace to sai dai incire rai da auren ko wacce mace indai bazan auri kaisa ba, nima fa hakuri nayi na karbi ta, kuma yanzu haka ma daga gidan su nasreen in nafitoni kuma nagaya mata yanda abin yakasance kuma ta yarda za ayi auren haka, salati momy ta sake, atakaice dai kace min kayarda ka karbi auren kaisan kenan, to wlhy baka isa ba, muktar cikin tashin hankali yace to momy in banyar da ba yazanyi kenan kinga yanda ran abba yabaci ne sosae, tsawa momy yasake mai to ni ina ruwa na yabaci mana nidai yanzu kaji abinda zan gaya maka kasami kaisan kace mata tasami abban ta tace masa itafa bata son auren nan tadagawa abban ta hankali in yaso sai yagayawa abban ku sae susan yanda zasuyi, too kawai yace mata, kaaa sai kuma yaji wayar ta katse, yakira yakira bata daga ba, sai kawai ya hau hanya, acen kuwa momy na cikin kitsawa muktar abinda zaiyi sai kawai taga abba akanta harde da hannu da alamu yaji me take kitsawa...... BABY ZAHRA [9:10PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA page 18 na BABY ZAHRA Dan sose sose ta fara na rashin gsky, sae da yakai 5mnt baice mata komai ba sannan daga bisani yace mata bazan hanaki abinda kika kin tsawa danki ba amma sai dai ina son kisani , duk randa akace an fasa auren kaisa da muktar to kisakawa ranki cewa kema zaman ki yakare agidan nan!!! Kamar saukar aradu taji saukar maganar, da sauri ta mike tsaye tace a'a alhj abin bai kai harga haka ba, indai zancen aure ne ko yauma a daura, bai tsaya sauraron ta ba yayi ficewar sa abin sa, zama tayi abakin gadon ta, wata zazzafar ajiyar zuciya momy ta sake, tace cab in alhj ya sakeni ina zan fara zuwa ae sai dai in koma kauyen mu, da sauri ta dakko wayar ta ta danna lambar muktar amma ina tayi tayi ya shiga yaki, tsaki taja tadan kwanta tafada kogin tunani Acen kuwa bayan ya isa yadan kwanta yana tunanin maganar momy shi, saiga nana er autar su kaisa tazo shigewa tagun dakin shi, ya kwalla mata kira ta shigo cikin sallama tace yaya gani yace yauwa goggona auntyn ki tana gida kuwa, ehh tace mai yace to tashi kije ki kiramin ita ko maza kice mata tazo ina neman ta, cikin sauri nana ta mike tana mai cewa too, adakin inna tasame tasuna hira da innar ta tashigo aunty wai kizo inji yaya muktar cewar nana, cikin faduwar gaba tace ni kuma yadawo ne ya muktar in tace mata eh yana dakin sa, inna ce tace tashi kije mana tunda kikaji ance miki kije inji shi kam ai kema kinsan yadawo kenan BABY ZAHRA [9:10PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA page 19 na BABY ZAHRA Da sallama tashiga dakin a hankali ya amsa don itakam bataji mai yace ba ta dai ga bakinsa yayi motsi, tana zama yace ke waike bakisan yakamata bane nadawo tun dazu amma shine baki kawo min abinci ba balle ruwa, a hankali tace laaa ai yaya bansan ka dawo bane amma kayi hakuri bari in dakko maka, da sauri ta mike tashige cikin gida, al halin fa cikin sa a koshe yake kawai dai baya wuce abincin kaisa ne don koba komai yarinyar ta iya girki, yasan dadin dandanon abincin kaisane tun lokacin da take zuwa musu hutu abuja, idan har kaisa na gidan to bayacin abincin kowa inba nata ba, ya zame mata jiki itake mai girki kullum nashi daban ne bayacin na masu aiki, kuma yayi missing in girkinta sosae yayin da ta daina zuwa gidan su, saboda irin musguna mata da sukeyi agidan da shi da kanwar sa zahra da uwarsu momy, agurin hjy rukkaya kawai take hutawa kasan cewar tana mata matsayin goggo ne ita, sallamar tane ya katsemai tunanin da yake yi foodflacks ne na abinci da plat da spoon da ruwa a gora mai sanyi ta kawo masa ta jiye a gaban sa, ta bude jalof in shinkafa ne yaji kifi banda, nan da nan kamshin abincin ya mamaye dakin, har yawun muktar ya kada, tadan zuba mai ta kalleshi tace ya yi haka, kai kawai ya daga mata, Allah Allah yake tagama yasamu yafara cii ta rufe kular tasaka mai cokali ta ajiye mai,ta siyaya mai ruwa a cup ta mika mai domin tasan al'adar sace baya cin abinci sai yadan sha ruwa, yasaka hannu yakarba, yace ashe dai wannan yarinyar haryanzu bata manta halaiyata ba,yafadi hakar azuciyar sa, tana gamawa ta tashi ta juya zata fita, yace zonan ki zauna BABAY ZAHRA [9:10PM, 3/18/2016] baby zahra: SAUYIN RAYUWA page 20 na BABY ZAHRA Dawowa tayi cikin nutsuwa, tasamu guri ta zauna, yana cin abincin sa yace kaisa tace na am yace kinsan me nake so da ke tace a'a yace inace kina son saurayin ki iron nan ko, cikin sauri tace mai eh, yace to nima ina da wata wanda nake so kuma ita nake son aura, kinsan me nake so da ke, tace a'a kisami abban ki kice masa ke bakya sona kina da wanda kike so, idan yaki ki masa kuka sosae kice masa ke bakya sona, saboda ke kinsan ni ba tsarar auranki bane, idan kikayimin haka to ni namiki alkawarin zan samawa iron kin aiki a jalingo inace kince yayi diploma tace ehh ya ce to zan Samar masa aiki a cen inyaso sai kuje cen ku zauna, tunda yafara maganar sa batace mai komai ba sae da tabari yakaraci zancen sa kafin tace mai, naji abinda kace ya muktar, amma kasani ni ina da tarbiyya kuma ina da biyayya don haka bazan iya samun abbana ba, ae Kaine babba don haka Kai kasami abban ka kagaya masa cewa baka sona, inyaki sai kamasa kuka kadaga masa hankali inyaso sai yace yafasa,da kake zancen soo kuma kai shaida ne ni bana son kamar yanda kaima baka sona, biyayya nayi nakarbe ka amatsayin kaddara, sannan kuma bakayi karya ba da kace ni ba tsarar auren ka bace saboda ni miji mai addini nake nema nagari wanda yasan mutuncin 'ya mace da kimarta, wanda yake biyayya wa iyayen sa,don haka ni ban damu da namiji dan boko ko wayayye ba, da kake zancen zaka samawa iro aiki ce maka akayi baya aiki ko mai, a hakan da ka ganshi yana da arzikin da zai ciyar dani ya tufatar da ni, alhamdulillah a hakan nake son shi kuma inza abarni zan aure shi, amma ni banna son kyalkyal banza, kuma ni inda zaka je kasami su abba da maganar nan da ka taimake ni ba kadan ba, domin nima banna son ka biyayya zanyi, kaga tafiya ta BABY ZAHRA

Share:

Tallata Kayanka

Guide Tricks Blog

Be With Me Technology

Popular Posts

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).