shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wanda aka fi sani da hausa novel wanda ni Muhammad abba gana nake rubutawa dan wayar tare da fadakarwa ga mutane a yanayin da muke ciki.

Wednesday 9 December 2015

KAUNA CE SILA***2****5-6-7-8 & 9

kauna-ce-sila.jpg

[7:56PM, 12/8/2015] Bana: KAUNA CE SILA 2***5




MUHD-ABBA~GANA






wayar na tabbatar min da saok na naje sai na kashe wayata na juya dan na kwanta amma bacci yaki zuwa wani irin dadi nake ji da ban taba jin irinshi ba ga wani sanyi da nake ji yana shigata wani tubnani nakeyi mai xurfi amma ta shi nake gani kona rufe idona bude a haka bacci ya saceni wannan text da yaya ya min sai ya zama kamar karatu ko yaushe zaka ganni da waya ina dubawa wani ikon Allah ko marwan ban ji zuciyata ta aminta dana fada masa ba a wa yannan kwanakin duk wanda ya ganni yasan ina cikin farin ciki ban kuma damuna ganshi ba text din ma yana sani nishadi wani lokaci ina zaune zan masa text nace masa I LOVE YOU idan ya gani sai yace min thank you duk da haka ina jin dadi wani lokacin kuma sai nace masa dan Allah yayi min text sai yace wani iri sai nace ko wanne sai kawai ya turo min addu'a koh hadisin annabi, haka abubuwa suka dinga faruwa rayuwa taba tafiya har wannan lokacin salisu bai fara fitowa ba amma yaji sauki hannun sane dai har yanxu bai daidai taba wani sabon al'amarine ya sameni duk hauka da tsalle tsallen da kai zance dana sabawa yiwa yaya yanzu ko na ganshi bana iya yi a wata shakkarsa ce ta shigen ga wata irin faduwar gaba da nake ji duk lokacin da na ganshi idan yana gurin bana iya sakewa kai ko aiki bana iya yi don yana zaune idan kuwa aikin shine sai dai wani ya dauke ni idan kuwa nayi ma duk wanda ya saurara zai fahimci tsoro ko rashin kwarewa a murya ta amma fa idan wakar wasu ce daidai zaka ji nayi tun text yanzu kuwa ya fara zama min kamar aiki don kusan kullum sai na tura masa koh bayan kwana biyu dan ko waya bana iya yi masa yanzu shima a yanzu yana yi min text don kusan duk juma a sai ya turo min text ko na addu a ko na fadakarwa ni irin nawa duk na soyayya ne da nuna kulawa ko addua nima duk da haka bai taba ce min ina sonki ta text ba,



MUHD-ABBA~GANA




www.abbagana.pun.bz
[8:01PM, 12/8/2015] Bana: KAUNA CE SILA 2**6



MUHD-ABBA~GANA



NIMA hakan nake yi wannan abu da yake faruwa tsakaninmu sai ya fara canja min tunani a wannan lokacun na kara fahimtar ashe haka yaya yake da ilimin addini gana boko kawai sai na fara ganin ai duk duniya ba wanda ya iya kwalliya gaskiya matar yaya tayi dace ai tuni manta da batun salisu ni yanzu kiran nashi ma na daina idan kuwa wani yayi min text ko na sanshi ko ban sanshi ba ko da text din yaya bukatar amsa bana iya turawa sai naga ai nayi laifi don ni yanzu text dina ns yaya ne kawai har gara in kira mutum dana tura sako a gaskiya ina matukar jin dadin text din yaya gashi bana taba bari a gani kai ba na ma taba ba wani wayata ba zan kuma ka taba ji na bawa wa wani ko wata labarin wai yana min text ba dani da marwan mutuncinmu ya kara karfi dan duk wani abu da nake so jita wajenshi nake ji hatta irin matan dake son yaya shi yake fadamin da kuma wanda shi yakeso a irin hirar da muka fiya yiya fi bani labarin wata zakiyya yafi nuna min cewa ita yaya yafi so don da ita zai aura kuma har yanzu suna tare na kan ji kishinta amma ban taba gigin tunkarar yaya da zancen taba amma ko a bakin direban yaya ina jin labarinta kuma wai makarantarmu daya amma nafi tunanin nafi ta aji da daya kenan su ne a bayanmu bama a guri daya muke lectures ba su a dayan suke sai ma ka fita daga gate din tamu nayi kudurin in har ina makarantar nan kafin na bar ta sai na nemo taba dan komai ba sai don na gano me yasa yake sonta kuma ya take ni shin ta fini kyau kuma ma dai ina so na santa kawai irin wadannan tunani su nafi yi kullum akan ta ni kuwa da yaya text yaci gaba da gudana yanzu na fara sabawa da irin rubutun shi da kuma kalamansa wani abin dadi a kwanan nan waya muke yi kuma yawanci da daddare amma gaskiya amfi yawanci shi yake fara kirana kuma muna kwashe mintina da yawa muna hira,



MUHD-ABBA~GANA



www.abbagana.pun.bz



KAUNA CE SILA 2**7






MUHD-ABBA~GANA




hirar bata wuce a kan rayuwa don ba mu fiya hirar soyayya ba matar mai gida muce ta haifu yau saura kwana daya suna ina dawowa daga makaranta zan hau sama kenan sai wani yaro yace min mamaa salisu yana kiranki nace aina ne aka ce min yana nan wani studio kasan mu lokaci dana shiga a zaune na same shi na jawo kujera dan nesa da shi kadan na zauna sai naji yace Dan Allah me nayi miki nace babu komai mai ka gani yace gaba daya kin canja nace haka dai kake gani ya kuma cewa gobe suna nace eh yace Allah ya kaimu nace amin yace muga wayarki nace a'a bara naje nayi sallah yace shikenan to nayi tafiyata na barshi a nan ranar suna naje makaranta da safe sai na kira layin yaya bayan ya daga mun gaisa sai kuma na kasa cewa komai shi kuma shirun yayi kuma yaki kashe wayar can dai na kashe da kaina nayi masa text kamar haka: KO WANE LOKACI SAI NAJI INA SO NA MAKA WAYA AMMA INA JIN MURYARKA SAI NA KASA YIN MAGANA NIMA BAN SAN DALILI BA KILA DON INA SONKA NE,bayan na tura masa naci gaba da harkokina na makaranta lokacin da muka tashi sai kawai na wuce gida tunda suna za muje zainab da hauwa suka min waya suka ce zasu biyo gidanmu mu wuce tare hadu saura suka shigo gidanmu shadda na saka army green dinkin riga da skirt ne yayi kyau na yafa mayafi kalar kayan takalmi da jaka baka dan kunne na ma kallar takalmi da jaka bakake dan kunnena malar shadda ne amma bai kai kayan turuwa ba ni kaina na yaba da kyan danayi haka muka isa gurin wanda kafin muje tuni an fara shagali gurin ya cika ga kida yana ta tashi muna shiga filin gurin muka ji mic yana gabatar da mu,



MUHD-ABBA~GANA





www.abbagana.pun.bz
[8:09PM, 12/8/2015] Bana: KAUNA CE SILA

2***8






MUHD-ABBA~GANA




bamu dade da zama ba muka dan tashi muka dan taba rawa ina fitowa naga miss call din marwan na kirashi yace gamu nan zuwa gurin sunan ku nace Dan Allah ku taho yace wallahi yayanki yace baza mu zo ba nace shikenan to muna ji a fara kirayen sallar magariba mutane sun fara wastewa sai daidaikun ina tsaye sai naji salisu a baya na ya min magana na juyi nace mekace yace me kikeyi anan nace babu hauwa na rako ta tafi yace bani wayarki na gani nace gaskiya ba zan bayar ba ka manta waya ce take hada mu fada to don Allah ka bar zancen nan abu kamar wasa sai naga ya fusata yana rantsuwa sai na bashi nayi masa banza sai naga yana kokarin kwacewa kawai sai na mika masa ban san me ya gani ba amma nafi tunani idan nake tura sako nan ya duba dai text din da na turawa yaya da safe shi ya nuna min nace ai ba wani abu bane dan ajinmu ne nayi hakan ne don naga alamar bai gane wa na turawa ba saboda na canja masa sunwma (1kai much) wannan ne yasa bai gane wana turawa ba kawai sai ya miko min wayar ya fara wasu irin maganganu kamar tababbe abin da yake fada ne ya tsoratani wallahi sai na tozartaki sai na wulakantaka rayuwarki yanda kika wukakanta tawa rayuwar jin irin abin da yake fada ne ya sa hankulan mutane aka tsaya ana kallonmu wasu kuma na bashi hakuri iya bacin rai naji shi ranar har naji me ma ya kawo ni gurinan ina tsaye zainab ta matso kusa da ni tace Dan Allah ki goge duk text din da ke wayarki na kalleta nace wallahi ba zan goge ba".




MUHD-ABBA~GANA




www.abbagana.pun.bz
[8:44PM, 12/8/2015] Bana: KAUNA CE SILA2***9




MUHD-ABBA~GANA




SAI gashi ya kara zuwa inda nake maganganun dai da yake yi irin na dazun ne a hankali sai na ga mutane darewa ya rage daga ni sai shi na juya nima zan tafi sai naji muryar shi ta fara rawa da alamun kuka ai kuwa ina juyowa kukan yake nan da nan naji jikina yayi sanyi amma ko kadan ban ji tausayinsa ba hasalima naji na tsane shi a yanzu,
ganin yana kokarin shiga wata irin yanayi yasa na na kara matsawa kusa da shi na fara bashi hakuri kayi hakuri" sau naga ya kara rikicewa ga hawaye na ta zuba na lura kowa ya tafi daga ni sai shi sai wasu dake gefe suna hada kayan kida nace masa tafiya zan yi kayi hakuri amma a zuciyata tunani nake an ya salisu bai samu tabin hankali a hatsarin nan da yayi ba to ko dai yana da aljannu ne saboda yanzu kuma ya koma rarrashina yana cewa dan Allah kar na barshi yana sona,nace to wai dan ma fa salisu bai gane wana yiwa text din ba kuwa bai duba wayar da aka min ba lallai Allah ya taimakeni ina wanan tunani muryashi naji yace muje na rakaki kawai binshi nake yi da idanu tare muka je har titi na ma yana tare za mu tafi nace masa gida fah zani yace eh na sani a daidaita sahu muka hau tare muna hawa hauwa ta kirani tace har taje gida bayan na kashe kawai sai na maida wayar silent kawai nayi ta gumi ina tunani yanzu yau naga ikon Allah wacce irin masifa ce wannan shi ma tunani yake dan ya kwantar da kanshi a kujera kuma idonsa a rufe suke muna shigowa titi unguwarmu muke sai na lura wayata tana wuta alamar an kira ni ina dubawa sai naga ashe text ne wani abin mamaki yaya ne kawai na fara karantawa.YA GAJIYA KUN SHA RAWA KAM




MUHD-ABBA~GANA




www.abbagana.pun.bz
Share:

0 comments:

Post a Comment

pls drop down your comment......
dan Allah ku ajiye comment.

Tallata Kayanka

Guide Tricks Blog

Be With Me Technology

Popular Posts

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Blog Archive