shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wanda aka fi sani da hausa novel wanda ni Muhammad abba gana nake rubutawa dan wayar tare da fadakarwa ga mutane a yanayin da muke ciki.

Friday 25 January 2019

SAKO ZUWA GAREKU MATAN AURE - SIFFOFIN UWA TAGARI 8

SAKO ZUWA GAREKU MATAN AURE - SIFFOFIN UWA TAGARI 8

Aure dai sunna ne na manzon Allah S.A.W, don haka a kowace sunna akwai lada matukar dai an yi ta kamar yadda manzon Allah S.A.W ya koyar. Don haka shi ma aure yana da nashi ladan idan aka yi shi kamar yadda Manzon Allah S.A.W ya koyar. Manzon Allah S.A.W ya yi bayanin irin ladan da ya kamata mace ta samu wajen biyayyan ta ga mijinta. Duk matar da take kyautata ma mijinta, tana faranta masa rai, tana kwantar masa da hankali, tana taya shi farin ciki a lokacin farin ciki, ta kuma taya shi bakin ciki a lokacin bakin ciki. To babu shakka itama xata ga farin ciki a duniya da lahira, Allah ya sa mu dace, amin.
Ya zo a cikin hadisin AbdurRahman Bn Auf, Allah ya kara masa yarda inda yake cewa Manzon Allah SAW ya ce "idan mace ta yi sallar ta guda biyar, kuma ta azimci azimin watan Ramadana, kuma ta kama kanta daga zina, kuma ta yi wa mijinta biyayya. A ranar lahira za a ce mata ki shiga aljanna ta kofar da kike so. Imamu Ahmad ya ruwaito wannan hadisi, kuma Albani ya inganta shi acikin SAHIHUT-TARGIB. Don haka ya kamata matan aure su kula da yin biyayya ga mazajensu. Akwai wata mata da mijinta ke bada labari: yace wata rana ya bar Abuja inda yake aiki zuwa Kaduna inda iyalinsa suke, koda ya zo sai ya kunna fanka don ya sha iska, har bacci ya dauke shi, sai aka dauke wuta, matarsa na ganin haka sai kawai ta dauko kujera da mafici ta zauna kusa da mijin tana masa fifita har sai da gari ya waye.


Da aka kira sallah sai ta tashe shi domin ya yi sallah, da ya ganta a zaune sai ya tambaye ta me ya faru take zaune kusa da shi? Sai ta ce masa ai yana kwanciya sai aka dauke wuta, don haka ita kuma tunda a wajen nemo masu abinci ne ya gaji, kuma gashi yana so ya yi barci amma zafi ya hana shi, to bari ita ta bar nata barcin don shi ya samu ya yi barci. Allah ya yi ma wannan mata albarka, Allah ya baku ikon yin koyi da ita. Dan duk matar da mijinta ya shede ta akan wani abin kirki, to lallai Allah ma zai yabe ta. Allah kasa ku kasance cikin mataye nagari. Amin.
Share:

0 comments:

Post a Comment

pls drop down your comment......
dan Allah ku ajiye comment.

Tallata Kayanka

Guide Tricks Blog

Be With Me Technology

Popular Posts

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).