shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wanda aka fi sani da hausa novel wanda ni Muhammad abba gana nake rubutawa dan wayar tare da fadakarwa ga mutane a yanayin da muke ciki.

Monday 10 August 2015

sireenah*******5,6,7

samp906c78071de1d454.jpg

Sireenah2*5




*********NA**********


muhd-Abba~Gana

www.abbagana.pun.bz




Motarsu suhail ya lalace saman hanya, daidai
gwargwado sun iya bakin kokarinsu motar yatashi
amma motar kamar batasan sunayi ba gashi basu
san meye matsalarba a karshe dai they decided
to call mai gyara(mechanic) cikin kankanin lokaci
mechanic din yagyara motar.
**********
Haba manager kashanyamu haka kamar kayan
wanki? munyi takira anace mana number busy.
Hajiya sorry kinsan yanayin garin namu sai a
hankali hold up yatsaidani, kutashi yanxu muje
office, Sai da suka zauna manager harda dauko
masu drink a fridge bayan sun shane yasoma
bayani kamar haka: ina sireena Sadam Saraki
take, gani nice.. ,lokacin yakai dubansa ga
sireenah tabbas itace pretty tacikin passport
saidai ta dan kara girma sannan tafi kyau a fili,
wow hajiya itama wannan yarki ce? eh manager
yatace. Gaskia tafi sauran kyau ko zaki bani ita?
wani kololon bakin ciki yatasowa mommy tee
batasan sanda tace anrigaka don tana da mijinta
aurenta cikin satin nan za ayi auren. Sireenah
idanuwa tabude saboda mamakin wannan karya
da mommy tee tashirga duk da manager baiyi
mata ba amma taji haushin hakan. No wonder
hajia naga tasa hijabi dogo da alamu mijinta zaiyi
kishi, koda yake banga laifinsa macce irin wannan
dole ayi kishinta, Allah yatabbatar da alkhairi.
Okay manager back to our business, Alright hajia,
bayan fitarku jiya nakara bincike sosai gameda
account din. A binciken danayi nasamu wata
takarda wanda Alhaji ya aiko da wata takarda
wanda yayi bayani kamar haka:- "Ni Alhaji
saddam Saraki dukkan tarin dukiyar dake account
dina mallakin 'yatace sireenah bayan rasuwata ita
kadai zata tayi operating account din ko matata
hajia fati ban amince tayi amfani dashi ba!
Akarshe bazata fara amfani da account din sai
lokacin da mallakin hankali kanta which is after
tayi aure!
Wani gumi yatasowa mommy tee, manager ban
fahimta kana nufin ni hajia fati banida right ga
account din mijina? tabbas haka yake hajia,
kenan sireenah sai bayan aurenta zata fara
amfani dashi? kwarai hajia haka mahaifinta
yace... Sireenah tayi farin cikin hakan sosai
tagodewa Allah daya sama mata mafita atleast
basu samu biyan bukatarsu, suka tashi jiki
sanyaye, motarsu yana gab da barin harabar
banki sai ga nasu suhail yashigo kamar ance
masa yadaga idanuwansa yayi tozali dana
safnarsa yazata ko gizo take yimasa but daya
rufe idanuwansa yabude yaga tabbas itace bashiri
yace Nazir ga funny girl can cikin mota don Allah
yi parking naje nasamesu kafin su wuce. Suhail
for God sake calm down mana bawai muje
musameta ba why not mubisu a baya muga gidan
da zasu shiga kaga yafi. Is better musan
gidansu.. Okay toh muje nazir kada su kubuce
mana, sun yanke shawarar binsu abaya, sireenah
bata gansu ba dayake motarsu suhail tinted ce.
Suna biye dasu har suka isa unguwar sa'ar su
daya ba hold up. Saida suka tabbatar nan ne
gidansu safnar saboda tambayar dasukayi kafin
suka bar unguwar zuwa inda aka aikesu, zasu
dawo zuwa anjima daddare he want to suprised
her............by muhd Abba Gana



www.abbagana.pun.bz



Sireenah 2*6




********NA***********


muhd-Abba~Gana



Azeema naga wautarki kina abu kamar bajina ba
irin wannan bai kamata kitsaya jamasa ajiba, ke
kanki kinsan bazan hana 'yata abinda takeso ba
daman ni can bawani son aurenki nake da suhail
don dai naga baki samu wanda yafishine amma
yanzu tunda kinsamu dole ayi da wannan, aini
abin farin ciki nane 'yata tazama sarauniyar wani
country bama gida nigeria, dagani akwaishi da
sakin hannu, kinga irin kyautar dayayi a tashin
farko. Daddy daman abinda yasa nace sai nayi
tunani shine baikon suhail dake kaina kada nazo
dashi kace bakasan da zancen, Suhail din banza
da wofi mena taba ci nasa dazanyi amansa, daga
yau na soke baikon dake tsakaninki dashi. Idan
kinada numbersa(shureim) kirashi kice masa kin
amince kinsanfa hausawa sunce abari yahuce
shike kawo rabon wani. Daddy banida numbersa
yace dai zai kirani dakansa. Toh shikenan kada
kibari ya kubuce maki. Zulfa'u kina ina ne wai?
gani tafe daddyn azeema, kinji abin farinki daya
samu yarki ko? wane abin farin ciki kake magana
daddyn azeema? badai yaudarar da kuke shirin yi
bane abin farin ciki? inajin duk zancen dakuke
banason saka kaina ne don ba'asa dani ba, wato
ku butulu kunje wurin mai martaba da kokon
bararku ya amince da auren suhail dana azeema
wato yanzu don kunga wanda yafi suhail din
shine zaku ci amanarsu? Dakata ke! cikin tsawa
yayi maganar, ni na kiraki shiyasa kike son ci
mani mutunci. Daddyn azeema kayi hakuri amma
wannan ba zancen cin mutunci bane gaskiace! Ki
rike gaskiarki bama so, nakula zulfa'u kema kina
cikin mahassada, wato kina bakin cikin hanyar
karuwana toh kisani daki amince da karki amince
sai azeema ta auri shureim. Yi hakuri daddyn
azeema bahaka bane Allah yahuci zuciarka yasa
kagane gaskia yakuma bada sa'a. Yanzu naji
abinda nake son ji ko kefa ai addua kadai
yakamata kiyi, idan baikon suhail yasa kike tada
jiyoyin wuya haka anfasa nasan yadda zanyi da
mai martaba yanada saukin kai. Nidai yar kalloce
baruwana daddyn azeema..
*******************
Lale maraba da Nazir ashe tare kuke da
mutuminka, saukar yaushe? hajia barka da
hutawa jiya nadawo. Madalla natayaka murna
suhail yace mani kungama karatu yanzu sai aure
ko sai ka tsaya ruwan ido irin na abokinka? Eh
hajia mungama, ai aure lokacine kidai tayamu da
addua samun macce tagari matan yanzu sai
ahankali, shima suhail ba ruwan ido yatsaya ba
lokacinsa ne baiyi ba amma ai nasamu labarin an
kusa aurensa shima da azeema. Eh hakane wurin
ruwan idonsa aka hadasu Allah dai yatabbatar da
alkhairi.. Ameen hajia, Yauwa nazir meka bawa
abokinka nagansa yau sai wani farin ciki yakeyi?
Hajia komai ban bashi ba watakila Allah yaakusa
amsar adduarsa ne. Toh Allah yasa. Ameen
hajiyarmu. Zan tafi suhail zanzo rikaya zuwa
gidansu safnar around evening time. Ina gaida
mami please... Bayan suhail yadawo wurin
rikayar nazir, take yawuce sashensa wurin zaba
tufafin dazai saka don burge sahibarsa zuwa
anjima but unfounately mai martaba dakansa yaje
sashen suhail. Alhaji barka da warhaka. Yauwa
suhail kashirya yanzu zuwa london akwai meeting
dinda za ayi cikin gaggawa na companing mu
wanda kai nakeso ka wakilceni flight dinku zai
tashi in the next 20mnt. Toh alhaji suhail bai
tsaya bata lokaci ba yasihrya cikin kankanin
lokaci mai martaba yana cikin mutanenda zasu yi
masa rakiya zuwa airport... A ranar suhail yabar
nigeria gashi baisamu damar zuwa gidansu
safnarsa. Ko nazir bai tarar dashi koda yadawo
daddare kamar yadda suka shirya
****************
Malama....malama... salamun Alaikum bayan
sallamar data amsa bata kara furta masa komai
sauri take ta isa gida shikuma mutumin yakafe
yaki tafia sai famar biyarta yake, gudu-gudu hadi
sauri kamar zata fadi kasa tasamu tashige cikin
gida, shigarta cikin gidan yayi daidai da isowarsu
yan biyu, cikin zafi nama Hussaina tafito daga
motar tana mai tambayarsa bawan Allah lafia?
metayi maka daka biyo wadda tashiga cikin gida
yanzu? Eh toh hajia lafiar takawo haka yarinyar
data shiga gidan yanzu nagani nake so kuma ni
da aure nake sonta amma taki saurarena..
Yasunanka? Sunana Salau hajia ina tsayar da
shayi a karshen layinnan. Okay malam salau
kadawo zuwa anjima zata saurareka kada kaji
komai. Salau yashiga washe korayen hakoransa
yana mai godia, ga wani uban silifas dake
kafafuwansa wanda yasha liki da leda,silifas din
yasade da kodaddar rigarsa ga dukkan alamu
fama yake dakansa bakine sosai bayada jiki
amma akwai tsawon wuya kamar marakin lema
inshort salau baya da kyan yau balle nagobe.
Yatafi da maganar zai dawo anjima, Hussaina
meye haka kin wani shanyani cikin mota nazata
gate zaki bude amma kin wani tsaya kina zance
daa wancan banzan almajiri.. Dadina dake
hassana saurin fushi ai kya saurari uzurina tukun,
baki kula lokacin da sireenah tashiga ciki bane?
taya zan kula bayan my attention yanaga driving.
Ok wannan dakike gani wurinta yazo nan ta
sanarda hassana yadda sukayi da sallau. Kai
hussaina gaskia naji dadin wannan lamari shine
don bakin ciki irin nata taki saurarensa bayan
tasan munyi kwanaki muna nema mata wanda
zai aureta bamu samu ba saboda bakin jini irin
nata, don bakin ciki shine zata koresa wallahi tayi
kadan.. muje ciki mommy tee tasan me ake
ciki.......toh fah!!!




muhd~Abba~Gana


www.abbagana.pun.bz
Share:

2 comments:

pls drop down your comment......
dan Allah ku ajiye comment.

Tallata Kayanka

Guide Tricks Blog

Be With Me Technology

Popular Posts

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Blog Archive