shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wanda aka fi sani da hausa novel wanda ni Muhammad abba gana nake rubutawa dan wayar tare da fadakarwa ga mutane a yanayin da muke ciki.

Tuesday 4 October 2016

TANA TARE DA NI... PAGE 91&92

tana-tare-dani.jpg

TANA TARE DA NI... TANA TARE DA NI... PAGE 91 BY MIEMIEBEE Cike da so da qaunan juna suka shirya suka fita chin lunch a restaurant Manhattan kamar yadda Fannah ta buqata, bayan Anas ya kawo musu order’nsu suka soma ci cike da jin dad’i, sosai Fannah ta zage ta gabza abincin se kewaye kewaye take ko zata ga Ummimi daga bisani k’ofar restaurant d’in ya bud’u atare Fannah da Anas suka miyar da kallonsu wajen Ummimi sukaga tsaye wajen tana rik’e da leda da alama shopping tayi sanye take da rigan cleaners, mamaki ne fal kwance kan fuskokinsu musamman ma Anas bade Ummimi aiki take anan as a cleaner ba? ya tambayi kansa disbelievingly. Sun d’au tsawon minti biyu suna kallon juna sannan daga bisani Anas ya kawar da kallonsa daga gareta ganin hawaye sun soma ambaliya mata a fuska. “Flower tashi mutafi.” Dagangan tace, “Habeebi ban gama chi bafa.” “Nasani zanje in siya miki wani lets leave now” yayi maganar tare da miqewa, kafin Fannah ta sake samun daman magana Anas ya d’agata badan tanaso ba tasoma binsa sunzo daidai bakin k’ofan kenan zasu wuce Ummimi tasa hannu ta tare Anas ta hanyan rik’o hannunsa chak! ya tsaya ba tare da ya juya ya kalleta ba. “Anas dan Allah karka min haka nasan banida iko akanka nasan banida daman tambayar yafiyanka amman dan Allah kabani daman baka hak’uri dan Allah Anas” ta k’are maganar cikin sautin kuka. Shiru Anad yayi totally speechless ayayinda zuciyarsa ke raya masa kar ya kuskura yabata wannan dama zuciyan nasa kuwa yabi ya fisge hannunsa daga nata yakama tafiya, dawani erin force Fannah taja kanta baya tare da k’wace hannunta dake a nasa cike da tashin hankali ya juyo yana kallonta. “Flower lets go!” Yayi demanding. “No Habeebi I’m not going anywhere with you se inhar ka tsaya ka saurari Ummimi, haba mana Habeebi wannan fa mahaifiyarka ce ita ta tsuguna ta haife ka bekamata kana wulaqantata kamar kashi ba, Habeebi nasan kanason Ummimi please give her this one chance to explain herself please for Hanan.” Alokaci d’aya Ummimi taji tana son Fannah dan yadda ta burgeta, “nagode ‘yata, Anas dan Allah kaji maganar matarka kabani daman baka hak’uri dan Allah Anas.” Hannunsa Fannah ta rik’o a hankali tana mirzawa “kaji Habeebi? Zaka iya bawa mahaifiyarka daman baka hak’uri, can you? Please...” Kallonsa ya miyar kan Ummimi daba abinda take banda kuka yana ganinta kawai se last incident daya faru tsakaninsu ya soma masa yawo a k’wak’walwa seyaji he can’t give her the chance she is asking for, gabad’aya ya riga ya dawo daga rakiyarta da ace 15years back ta dawo da yayi accepting nata amman banda yanzu. “No I can’t Flower I can’t mutafi nace!” Yayi maganar a tsawace. “Habeebi is okay calm down okay? Calm down” tayi maganar cikin salon dake kwantar masa da hankali. *“INA TARE DA KAI Hanan NA TARE DA KAI*do this for me please just listen to her” badan yanaso ba ya gyad’a mata kai. ** Zaune Anas da Fannah ke kan wani d’an dogon kujera a yayinda Ummimi ke zaune opposite them fuskarta jik’ap da hawaye. Cikin kuka ta soma magana; “Anas nagode daka bani wannan dama nagode sosai Allah maka albarka” ko kallon direction nata baiyi balle yace ameen. “Nasan banida izinin da zan fara rok’ar gafararka saboda abinda na muku, bansan ta ina zan fara baka hak’uri ba wallahi barin ku danayi shine babban kuskuren dana tafka a rayuwata Anas, kuskuren da har a yau ina nadamar sa kuma har in mutu zan cigaba dayi, wallahi sharrin shed’an ne it wasn’t my intention to leave you guys my family.” Ta tsaya ta share hawayenta tare da jan hanci “Anas I love you, wallahi ina sonka fiye da yadda nakeson kaina, tun tafiya na a kullum da tunaninka dana mahaifinku dakuma na k’annenka nake kwana nake kuma tashi dashi, da abinda na muku tun aduniya na fara ganin sakamakon sa ina ace na tafi lahira ban nemi gafararku ba? Anas dan Allah kayi hak’uri, baka bani dama ba amman ni na baiwa kaina kayi hak’uri ka yafemin please na tuba Anas ka tausaya min mahaifiyarka dan Allah d’ana barin iya samun kwanciyan hankali ba har se in ka yafemin ka tausaya min please.” Ta rushe da kuka miqewa Fannah tayi takoma gefenta ta tsaya tana shafa bayanta cike fa tausayi idanunta itama sunyi jazir. “Ummimi please kibar kukan haka nan ya isa dan Allah.” ‘‘Yata dan Allah kimasa magana ya tausaya min ya yafemin.” “Anas Habeebi ka tausayawa mahaifiyarka please.”Kai ya girgiza cike da takaici “mahaifiya? Yanzu ke Ummimi bakiji kunya ba da kike kwatanta kanki da mahaifiyata nikuma da d’anki? Bakiji kunya ba? As far as I’m concerned Ummie itace mahaifiyata. D’an da kika tunkud’esa kamar kashi 15 years ago, d’anda kika k’yamata d’an da kika masa permanent tabo a hannu” ya yi rolling hannun shirt nasa ya nuna mata tabon tabbas ta tuna itace taji mai ciwon danko kafin ta fice daga gidan taga yadda hannunsa ke yoyon jini amman saboda yadda shaid’an yafi k’arfinta alokacin ta fice ta barsa. Wani sabon kukan ta rusheda. “Kin tuna ciwon?” Ya tsamota daga duniyar tunanin data fad’a. “You think you still have the right to call me your son? Kinsan kalan k’uncin rayuwan da mukayi witnessing bayan tafiyarki? Kinsan ya akayi aka girmar damu aka girmar da Amal jaririyan da kika turo bayan tafiyarki precisely? Kinsan ya aka tarbiyyattar damu?” Zuciyanta taji yawani buga tare da sarin da kanta ke mata tana me k’ara tsanan kanta. “Kinsan ya akayi muka taso ba gatan uwa har muka fara mancewa da labarinki? Kinsan dare nawa muka kasa bacci saboda tunanin ki? Kinsan kwana nawa na d’iba inayi a waje ina tunanin ko zaki dawo mana? Kinsan what hell you made Abuu went through? The answer is No baki sani ba saboda alokacin kina chan da sabon mijinki kina more rayuwa. Its all over Ummimi I’ve loved you, we’ve loved you so dearly bu not anymore banida gurbin da zan sake ajiye soyayyan ki a zuciya na saboda na dawo daga rakiyarki, ke kika haifeni I can’t change that amman abinda nakeson kisani shine ki sa a mind naki baki tab’a haifan d’a me suna Anas ba, so nake ki mance dani kamar yadda na manta dake a rayuwa na cause I can‘t forgive you I will NEVER forgive you.” Yana kaiwa nan ya miqe da sauri tare da juyawa gudun kar hawayen dayake maqewa su fito seda ya shanyesu sannan ya juyo alokacin kuka sosai Ummimi ke wane zata cire ranta ayayinda Fannah ke bata hak’uri. “Anas tabbas ba k’arya cikin kalamunka tabbas nasan namuku laifi, laifin da yayi babban tabo duka a zuqatanku wallahi nayi nadama Anas kabani dama in biyaka 15years that passed, let me make it up for the past 15years da mukayi ba tare ba please kar ka hanani performing obligation d’ina as your mother.” “You are not my mother so you don’t have to saboda I don’t need you ko ayau akace Ummie wacce ta girmar dani wacce nake regarding nata as my mother ta rasu zan cigaba da rayuwa na balle ke, because I’m a grown up now as you can see I’m married saboda haka I don’t need you na yafe miki tsawon 15 years da mukayi ba a tare ba, ba sekin biyani ba, kitafi ki koma inda kika fito banasonki a rayuwa. Flower lets go” yaja hannunta suka soma tafiya, k’ok’arin jan hannunta daga nasa take amman takasa har seda suka isa mota tana kuka tana mai magana “haba Habeebi ban tab’a sanin your heart is as cold ba se yau, mahaifiyarka ce fa your own mother koda laifin kisan kai tayi be kamata ka mata haka ba, ka duba yadda tayi nadama mana kodan haka baraka saurara mata ba?” “Yes Flower barin saurara mata because I don’t need her 15years danayi ba ita yasa na mutu ne? No saboda haka bana buk’atar ta taje tasamu family’nta we don’t need her.” “Hab-” katsesa yayi “enough okay?!” Yayi maganar cikin sautin tsawa ganin yadda ta firgita sekuma yaji ba dad’i hannayensa ya aza kan shoulders nata “Flower I’m sorry banason ina miki tsawa, banason muna musu banason Ummimi ta zama sanadin samu fad’an da bama yi please stop crossing me kibarta let her be kinfi kowa sanin kalan k’uncin data jefa mu especially me, data tafi ta barmu without turning back. Ko kin manta saboda ita nasoma shaye shaye har ya kaiga nayi raping naki Flower duk kin manta? It because of her you suffered itace silan komai Ummimi batada advantage se disadvantages.” “Tabbas ba k’arya cikin maganganunka Anas” cewar Ummimi dake tsaye some inches away from them da alamun ta saurari dukkannin abinda Anas ya fad’a. “Tabbas duk wani abin haramun da ka aikata nima me laifi ce kuma nice sila saboda da ace ina nan da na hanaka aikata hakan, kayi gaskia da kace banida advantage se disadvantages all am asking for is kabani dama to be a mother to you again Anas koda baraka yafemin ba kabani dama insake rik’eka a hannayena in dafa maka abinci this is all I ask Anas please.” “You should hace thought about this 15years ago kafin kika tafi, alokacin ne wad’annan kalamu naki zasuyi tasiri akaina amma banda yanzu da kika riga kika karya min zuciya in baki sani ba kisani I’m not the Anas you left 15 years ago wannan Anas bayida tausayi saboda tafiyar mahaifiyar sa yakoya masa rashin tausayi da imani, my heart is as cold as stone dan haka kibar b’ata yawun bakinki kina bani hak’uri barin tab’a hak’ura ba Flower lets go.” “Okay Habeebi zan bika amman please kabani koda minti biyu ne inma Ummimi magana kaji?” “Flower me zakice mata? Kibarta please.” “Habeebi dan Allah fa nace please minti biyu kad’ai.¢ Kai kawai ya gyad’a mata “thank you so much my Lion.” Wajen Ummimi ta nufa taja hannunta suka b’ace daga kallon Anas bisa wani bench suka zauna Fannah na sharewa Ummimi hawaye. “Please kibar kukan hakanan ya isa dan Allah.” A raunane ta d’ago idanunta tana kallon Fannah “ ‘yata ya sunanki?” “Fannah, Fannah suna na.” “Masha Allah Fannah nagode da kulawarki a gareni Allah sak’a miki da alheri yakuma sauk’eki lafiya” (agarin share mata hawaye da Fannah ke hijabinta ya d’agu anan ne Ummimi taga cikin nata.) Mamaki ne ya mamaye fuskan Fannah taya Ummimi tasan tana da ciki? Cike da kunya tace, “ameen Ummimi please kibar kukan haka nasan Anas haka yake yanada taurin kai ne kuma sonki da yake yasa yake treating naki haka amman in shaa Allah wataran se labari Anas ze yafemiki nan bada jimawa.” “Haka kike gani ‘yata Anas ze iya yafemin abinda na masa?” “Allah ma muka mai laifi ya yafe mana balle d’an da kika haifa? Trust me ze yafe miki kidage da addu’a kawai nima zan saki cikin nawa.” “Nagode sosai ya Shettima yake dan Allah?” “Shettima nanan girmansa kusan d’aya da Anas yana kan karatu.” “Masha Allah nasan da kunya ma in tambayeki ya baby’n dana turo musu da ita bayan tafiya na wanda ko halittan fuskarta ban k’arewa kallo ba.” “Amal? Amal sunanta she is 15 years now itama ta na nan lafiya tana ss2 kinsan wani abu?” Kai Ummimi ta kad’a “sautin muryanku d’aya dakika fara min magana na zata ma Amal ce.” Murmushin takaici ta saki “Allah sarki Amal Allah yi mata albarka” “Ameen barikiga pictures nasu” nan taciro wayarta tana gwada wa Ummimi, hawaye sosai Ummimi ke kamar ba gobe tana me sake tsanan kanta abinda ta ma family’nta. “Amal da Anas sak kaman ni na, Shettima ma ba laifi, ‘ya‘yan Albarka Allah ya cigaba da raya min su yamusu albarka, yamuku albarka gabad’aya” tafad’a tana share hawayenta. “Ameen Ummimi.” “Ya Babansu yake? Wace Ummie da Anas yake fad’a kuma?” “Babansu na nan k’alau, Ummie k’anwar mahaifinsu ce.” “Ohhh Allah sarki nako ganeta itace ta girmar dasu?” “Eh itace.” “Allah sarki Allah ya saka mata da alheri, Babansu be sake aure ba?” “Gaskia be sake ba” “Allah sarki Ya Ibraheem, Fannah awani gari kuke yanzu da zama?” “Dukan mu a Maiduguri muke.” “Okay kunzo nan shaqatawa ne?” “Eh munma kusa komawa zaman nan ya ishemu gida yafi dad’i.” “Hakane ‘yata no place like home, dan Allah kitayani ma Anas magana nasan yana jin magananki koda bare yafemin ba yabani izinin zama mahaifiyarsa again, I want to make up for the past 15 years da mukayi ba a tare ba.” “In shaa Allah Ummimi karki damu sede wani gudu ba hanzari ba am sorry to ask mesa kikesa uniform na cleaners?” Murmushin takaici ta saki tare da share hawayenta. “Anan nake aiki Fannah as a cleaner.” “Subhanallahi cleaner kuma Ummimi? Meya faru? Meyasa?” “Long story ‘yata da wannan aikin kad’ai na dogara.” “Ummimi ina mijniki da ‘ya‘yanki? A yadda Anas yabani labari aure kikayi bayan tafiyanki.” “Tabbas aure nayi, Fannah mijin dana aura d’an cult ne nagudu nabarsa har a yau nemana yake.” “Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un to ‘ya‘yanki fa ko babu?” “Akwai har uku nafarin mata ne twins Basmah da Barrah sekuma autan Aleeyu wanda yake nan sak Anas har blue eyes nasu wanda sukayi inheritting dagu gun mahaifin kakana iri d’aya.” Hannu tasa a aljihunta taciro picturen ta nuna wa Fannah. “Woww masha Allah kyawawa dasu.” “Barrah da Basmah are 13 years, Aleeyu kuma 10 daganan ban sake haihuwa ba.” “Ayyah, wallahi Aleeyu sak Anas inda bansani bama cewa zanyi Anas ne haske kawai Anas ya d’ara sa kad’an but Ummimi a ina suke su yanzu? Suna wajenki ne ko wajen mahaifinsu?” “Ko d’aya ‘yata suna wajen mahalicinsu.” Tasa hannu tana share hawayenta. “Ban fahimce kiba Ummimi.” “Babansu yayi kud’i dasu Fannah, ya siyar da ‘ya‘yan cikinsa wa k’ungiyansu.” “Innalillahi wa inna ilaihi raji’un!” take itama Fannar tasoma kuka. “Ummimi I’m so sorry kiyi hak’uri dan Allah, Allah sa k’arshen wahalansu kenan Allah sarki kiyi hak’uri dan Allah.” “Bakomai nima abinda yasa na gudo na barsa kenan saboda nice next target nasa jini na ne next abinda k’ungiyansu suke buk’ata dana gano hakan na gudu na barsa.” “I’m so sorry Ummimi shi rayuwa haka yake kowa da kalan jarabawarsa, ki cigaba da musu addu’a bale ma yara ne dukansu Allah sa masu cetoh ne.” “Ameen ya rabb-” bata samu daman k’are maganan ba ganin Anas datayi. “Flower lets go.” yayi i terrupting nata. “Toh Anas ina zuwa yanzun nan” bayan daya koma ta dawo da kallonta kan Ummimi. “Ummimi yanzu a ina kike kwana?” “Anan a d’akin da aka tanadarwa cleaners.” “Subhanallah mesa baki fad’a min ba? Bari zanyi wa Anas magana inshaa Allah zaki biyomu gida.” Hannunta Ummimi ta rik’o da sauri “a’a Fannah karki ma b’ata yawun bakinki please I don’t want to be a burden ni abinda nakso kimin d’aya ne hanyan da zesa Anas yayi accepting d’ina as his mother.” “Duka biyu zanyi Ummimi bareyi kina kwana agidan cleaners ba bayan da gatanki ina zuwa” nan ta fice taje tasamu Anas dake tsaye gefen motansu yana jiranta seda ta iso gab dashi ya saki mata murmushi wanda itama ta miyar masa “lets go?” Kai ta gyad’a masa tare da ajiye masa picture’n su Basmah akan bayan motar. “Meshi?” Ya tambayeta. “Ka duba kaga” ba gardama ya d’aga hoton yana kallo. Be sansu ba amman seji yake kamar yasansu gakuma me kamanninsa dayake gani cikin hoton harda blue eyes d’inma, tunaninsa ne ya jagule alokaci guda he seems puzzled. “Flower suwaye wannan? Waye wannan yaron?” “Kaga kuna kama koh?” “Sosai kuwa the eyes the face everything please suwaye ne?” “Your siblings Habeebi, k’annenka ne.” “K’annena?” Ya d’ago kai yana kallonta cike da mamaki. “Inada k’annen da sukafi Shettima da Amal ne?” “Yes step siblings naka ne.” “You mean yaran Ummimi?” Seta gyad’a kai pucture’n ya miyar mata “gashi banason ganinsu.” “Ayyah Habeebi basu maraye bale kace haka.” “What do you mean?” “Dukan su nan Allah yayi musu rasuwa, babansu your step-father d’an cult ne ya siyar da yaransa wa k’ungiyansu bayan nan yadawo kan Ummimi dalilin dayasa ta gudo tabarsa kenan har kaga take aiki anan ayanzu haka batada wajen kwanciya, Habeebi ka tausaya mata please...” © MIEMIEBEE

TANA TARE DA NI... PAGE 92 BY MIEMIEBEE Tunaninsa yaji ya katse kwatsam! sam yakasa yarda da abinda Flowersa ke ce masa, cikin sauti me rawa yayi maganar “Flower what did you just say?” Sake nanata abinda ta fad’i tayi. “Subhanallah! Flower are you sure?” Yayi maganar tare da karb’e picture’n yana sake kalla. “Kina nufin dukansu nan basuwa nan yanzu?” “Yes Habeebi” ta yi maganar tana gyad’a kai. “Allah sarki... They are in a better place in shaa Allah.” “Toh Habeebi Ummmi fah?” “Meh had’i na da ita? Infact ni banma yarda ba who knows ko duk k’arya take tanason in tausaya mata ne tayi coming up da plan d’innan.” ”Haba! My Lion don’t be like that, taya zakace haka wa mahaifiyarka? Inhar k’arya kake tsammanin tamana uniform na cleaners dake jikinta kad’ai sheda ce, Habeebi mahaifiyarka cefah feel sympathy towards her atleast yara uku fa ta rasa one, two, three” ta irga da hannunta. “Toh Flower laifi na ne? Nine na siyar mata da yara? Kwad’ayinta ya kaita kinga erin disadvantage da nake fad’a miki ai yanzu itace silan mutuwan yaran nan, mschw! What a pity.” “I know Habeebi bara mu iya canja komai ba abinda ya faru ya riga ya faru please ka taimaka wa Ummimi.” “In taimaka in mata meh?” “Mutafi da ita hotel da muke.” D’an dariyan rainin wayo ya saki “intafi da ita? LOL lallai kam Flower you are such a wonder ni magananta ma ya isheni kimiyar mata da photo d’in ki taho mutafi.” Haka Fannah ta riga lalashinsa tana basa hak’uri da k’yar d’in k’yar ya yarda Ummimi ta bisu amman ba’a cikin motarsa ba hakan kuwa akayi. Bayan taje ta taho da Ummimi ta tsare mata cap (taxi) kafin Ummimi tashiga taje gun Anas dan masa godiya, yana zaune cikin mota yana jiran Fannah. “Assalamu Alaikum Anas nagode da taimakon dakamin, Allah saka da alheri ya kuma maka albarka.” Tayi maganan tana tsaye ta bakin windon side na Anas. Ko kallonta beyi ba se latsa wayansa yake chan yace, “thank her not me bani na taimaka miki ba excuse me please” Shiru tayi bata kuma cewa komai ba takoma taje ta shiga cap d’in hawaye na bin k’uncinta har suka isa hotel d’in kuka bata bar kukan ba. Bayan isansu Fannah ta kalli Anas sannan cikin salon da inta mai magana yakeji tace, “My Lion nace zakayi wa Ummimi booking room koh?” Tayi maganan tana murza hannunsa a hankali. “Flower kinga ba haka mukayi dake ba cewa kikayi zata biyomu nan bakice zan mata booking room ba saboda haka figure out me zakiyi da ita” yana kaiwa nan yafito daga motar ya wuce ciki. Binsa da kallo tayi “Habeebi yau ko kafi babarka k’ok’ari seka mata booking room d’innan” ta fice daga motar ta sallami taxi driver’n. “Ummimi muje reception ki zauna achan kafin amiki booking room.” “Nagode ‘yata Allah miki albarka.” “Ameen Ummimi” anan tajata zuwa reception daidai zata juya Ummimi ta riqo hannunta “Fannah karki b’oye min Anas yace bare kama min d’aki bakoh?” “A’a Ummimi ya kike magana haka-” katseta Ummimi tayi “please karki min k’arya” zama Fannah tayi a gefenta hannunta riqe cikin na Ummimi. “Inason kisa a ranki Anas ze yafe miki saboda mahaifiyar sa ce ke kinji?” Kai Ummimi ta gyad’a mata “good kuma please kukan ya isa haka zan masa magana ina zuwa” ahaka suka rabu. ** Miqe Anas ke akan gado da newspaper a hannunsa yana karantawa yana jin k’aran bud’e k’ofa ya ajiye yasoma baccin k’arya agefensa ta zauna “My Lion nasan ba bacci kake ba.” Shiru yayi be tanka taba. “Habeebi katashi please kaji?” Ta hau jijjiqa sa badan yanaso ba ya bud’e ido. “Meh?” “Habeebi Ummimi mana kamata booking room.” “Banida kud’i.” “Youngest billonaire d’in? Habeebi please ka tashi” nan ta miqe ta hau jansa daga gadon sam takasa murmushi ya saki sannan yajata ta fad’a jikinsa. K’ara ta saki sosai sanadin cikinta data buga. “Arghhh! Habeebi ciki na.” “Sorry Mom Hanan” ya zaunar da ita kan cinyansa. Kukan k’arya ta soma tana riqe cikinta. “Flower nayi hitting naki sosai ne?” Kai ta gyad’a tana murzq idanunta. “Am sorry kinji? Muje asibiti?” “A’a nikayi booking wa Ummimi d’aki.” “Flower barinyi ba.” Rushewa takumayi da kuka, “Flower wai bara kibar kukan nan ba?” Ta gyad’a kai ba yadda beyi tayi shiru ba amman taqi daga k’arshe seda ya yarda da k’udirinta. “Okay, okay naji zan mata for Hanan’s sake.” Koma meh tace a zuciyarta tare da share hawayen k’aryan nata. Tana ganinsa ya fice ta saki murmushi. Nan da nan ya sauqa yaje yama Ummimi booking d’aki a chan last floor ta yadda bare ma na kallonta ba bale yana jin baqin ciki. Tana zaune a reception d’in Anas yazo ya wuceta batareda yace mata ko k’ala ba bayan daya gama komai ya nufo inda take tare da ajiye mata key d’in a kujerar dake gefenta “room 116” kad’ai yace da ita. Hannunsa ta riqo kafin ya kub’uce mata. “Anas nagode Allah saka maka da alkhairi.” Hannunsa ya fisge ba tare da yace da ita komai ba. “Anas dan Allah kayi hak’uri kamin magana barin iya jure fushinka ba please talk to me your mother” ba tare da yace da ita komai ba ya haye sama d’akinsu da Fannah. *** Haka nan tun daga ranan Ummimi tasoma zama dasu Fannah ko kad’an Anas baya shiga harkarta magana ma ba mata yake ba, koda ta mai magana baya amsata ba yadda Fannah batayi dashi ba amman yak’i yafewa Ummimi, a dalilin haka tasoma tashi Sallan dare tana roqan Allah. Cikin d’an k’ank’anin lokaci Fannah suka shaqu da Ummimi dan yadda Fannah kebata kulawa tamkar uwarta abinci kullum ita ke kai mata dan kuwa tsoron placing order ma take, haka Fannah tasa Anas agaba seda ya siya wa Ummimi kayan sawa da sauran abubuwan da zata buk’ata. Dukda shariyan da Anas ke mata hakan be hanata yimasa magana anytime she gets the chance to ba fatanta Allah sa Anas ya bata daman da take nema. Sunyi zaman two weeks tare Anas ya fara zancen komawa gida, Nigeria badan komai ba dan ya rabu da Ummimi. 4:30PM Yana cikin harhad’a musu kayaki kasancewar gobe zasu tafi Fannah ta shigo d’akin bayan fitowarta daga d’akin Ummimi, akan gado ta zauna “sannu da aiki Habeebi.” “Yauwa Flower.” “Uhm nace in zamu koma Ummimi zata bimu ba?” Barin abinda yake yayi “waze bi wa?!” Yayi maganar cike da rashin yarda. “Ummimi zata bi FAHNAS nace.” “Humm!” yaja numfashi “sede in wani FAHNAS d’in kam ba wanda nasani ba.” “Toh My Lion ita kad’ai zamu bari anan ne?” “Dama dawa muka sameta? Ita kad’an ta muka sameta haka kuma zamu barta” “Haba! My Lion katuna fa batada family yanzu we are her only family.” “Flower I’m not her family kuma ba inda zanje da ita ta sake messing min family like she did before.” “But Hab-” “Period!” Ya katse ta. Bata sake ce masa komai ba gudun kar suyi fad’a. Chan bayan sallan isha bayan sun k’are chin abinci ta matso ta zauna kusa dashi akan gado tare da riqo hannunsa cikin nata. “Habeebi please badan niba dan Allah kar kabar Ummimi anan baka tunanin in rananda step father’nka ya ganta ze siyar da ita kamar yadda ya siyar da su Barrah? Baka tunanin barinta anan had’ari ne Habeebi? I’m not asking you to forgive her all am asking is mutafi da ita kar mu barta anan please Habeebi don’t say no please.” Shiru yayi harga Allah bai tunanin ze iya ce ma Flowersa no this time akan abinda yasan ba gagaransa zeyi ba sede yanzu in yabar Ummimi tabisu dole gida ze kaita abinda bayyaso kenan yafison kamar yadda suka saba ba ita su cigaba da kasancewa ahakan shi bama wannan ba mezece wa Amal da batasan tanada wata mahaifiya ba bayan Ummie? Abinda ke damunsa kenan. “Habeebi please kayi hak’uri mutafi da ita kaji?” Kai zallah ya gyad’a mata yana me nazarin aina ze kai Ummimi bayan isansu Nigeria. “Thank you so much My Lion” tayi pecking nasa tare da miqewa. “Ina kuma zakije Flower?” “Zanje ince ma Ummimi ta shirya kayanta zamu tafi gobe.” “Flower shine baraki iya kiranta a waya ba? Ni banason kina unnecessary zirga-zirga kinde sani bakida lafiya kuma munada tafiya gobe.” “Don’t worry Habeebi I won’t take long” tayi mai blowing kiss, murmushi ya mata sannan ta fice. Zaune ta tarar da Ummimi kan gado as always ta had’a tagumi bayan tayi sallama ta shigo tazauna a gefenta. “Ummimi ki shirya kayanki zamu tafi gobe.” Cike da rashin fahimta ta d’ago kai tana kallonta “ina zamuje Fannah?” “Nigeria! Zakije kiga su Amal!” ta sanar da ita cike da jin dad’i. “Nigeria?! Kina nufin Anas ya yarda zan biku? “Ai na fad’a miki Anas na sonki he is just taking time to adjust nan bada jimawa zakuyi sorting out komai.” “Allah sa Fannah nagode kuma sosai Allah biyaki.” “Ameen Ummimi ba komai tashi mu shirya miki kayan naki.” “A’a please karki damu kayan nawa dududu nawa ne? Keda bakida lafiya ma kije ki huta dan Allah kar gajiyan ya miki yawa.” “Tunda haka kikace fine kiyi ki shirya ki huta kema Allah kaimu gobe.” “Ameen nagode kima Anas godiya please nasan koda mutuwa zanyi ina mai magana ba amsani zeyi ba.” “Bakomai Ummimi zan masa in shaa Allah seda safe” ta rufo mata k’ofar. ** Bayan Anas ya kashe musu wuta suna kwance kamar yadda suka saba Fannah ta kira sunansa, “Habeebi.” “Yes Flower.” “Thank you so much for everything.” Ta fad’a tare da sake shigewa jikinsa. “You don’t have to thank me Flower, ma godiyan me kike?” “Aika fini sani d’azu Mami takirani tace in maka godiya mekayi musu, nayi nayi da ita ta fad’amin tak’i.” “Haha!” yayi dariya kad’an “hakane?” “Eh mekayi musu?” “Babu.” “Kamar ya babu Habeebi duk alkhairun da kake musu da a baya Mami bata tab’a cemin na maka godiya kamar na yau ba meh ka musu please?” “Nace miki babu lets sleep tomorrow is a big day.” “O’o ni seka fad’amin wani alkhairi kamusu.” “Nace miki babu please kiyi bacci ko Hanan ma zata samu tayi, goodnight” yayi pecking kanta. Shiru tayi chan ta kira sunansa “Habeebi.” “Yes Flower lets sleep.” “Thank you kaji? Allah k’ara bud’i.” Magana yake cike da gyangyad’i “Flower nace miki banason godiyan nan.” “Bakasan akan mefa nake maka godiyan ba.” Ya nisanta “akan meh?” “Ummimi ce tace na maka godiya.” Shiru yayi bece komai ba. “Kaji My Lion?” Nan ma shiru data d’ago kai ta kallesa setaga idanunsa a rufe she is sure ba bacci yake ba, bayason maganan Ummimi ne. “Liar nasan ba bacci kake ba kadeji Ummimi tace ta gode” nanma bece komai ba murmushi ta saki tare da jan hancinsa. “Awwch!” Ya sakar da k’ara “kinsan da zafi koh?” “Aww! kana jina kamin shiru kenan.” “Sa’an ki d’aya Baby Hanan if not da na rama.” Gwalo ta saki masa sannan yajata jikinsa suka kwanta*** washegari... As early as possible suka shirya luggages nasu duk na acikin mota Anas yabari asa akwatin Ummimi a motansu yak’i taxi aka tsare mata ta shiga ciki, kusan a tare suka isa airport akayi musu ciki da akwatinansu. A sama su Fannah suke a yayinda Ummimi ke k’asa ita kad’ai ba yadda Fannah batai da Anas yabar Ummimi ta samesu ba yak’i. 2 hours later... Miqe Anas yake kan wani medium sized bed se baccinsa yake sha ayayinda Fannah ke zaune a d’ayan side d’in da Qur’ani a hannunta se karatu take tayi daidai takai inda k’arfinta ya k’are ta tsaya tare da miqewa ta sauk’a k’asa gun Ummimi as always ta sameta ta ta had’a tagumi bayan ta zauna a gefenta ta dafe kafad’arta se anan Ummimi tasan da shigowarta. “Fannah” takira sunanta a bit suprised. “Na’am Ummimi kin zauna shiru ko TV ne ki kunna mana.” “A’a barshi karki damu, ya Anas yake?” “Yana bacci kema ya kamata ki kwanta.” “A’a nikam, se hankali a kwance ake iya bacci ai.” D’an murmushi Fannah ta sakar mata “toh ga Qur’ani ki karanta” ta miqa mata. “Nagode kema kije ki huta wannan hawa da sauqan ze dameki kinga already k’afafuki sun kumbura.” “Toh Ummimi.” “Nace yaushe ne jikan nawan ze fito?” D’an dariya ta saki dan kunya ma takasa fad’a mata. “Surikar tawa tana jin kunya na ne?” Ummimi tayi teasing nata. “Nanda wata uku in shaa Allah.” “Ahh ashe ma kin kusa toh Allah raba lafiya ‘yata Allah ya sauk’eki lafiya.” “Ameen Ummimi nagode barinje in huta nima.” “Yawwa ‘yata” ahaka suka rabu beside Anas taje ta kwanta alokacin har ya tashi. “Flower ina kikaje?” “Gun Ummimi.” “Baraki koyi zama gu d’aya ba ko kinga k’afafunki kuwa? Wai bakiya jin tausayin kanki ne?” “Habeebi please ya isa ai dama kumburin dole ne kaide kace kanason min surutu ne saboda gun Ummimi naje inda toilet nace na shiga ai barakayi magana ba.” “Ohkayyyy haka kika ce? Toh har mu isa banason kisake sauk’a wajenta am not asking you am ordering you as your husband.” “Sekayi ai” tayi maganar k’asa k’asa. “Kuma najiki nide na fad’a miki.” Baya ta juya masa ba tare da tace komai ba haka tundaga nan bata sake masa magana ba kodaya tasheta Sallan Azahar haka La’asr ma shima be mata magana ba. 10 hours ya d’aukesu sannan suka iso Nigeria inda suka sauk’a a Sandralia Hotel Abuja har anan Fannah bata sake ma Anas magana ba, ruwa ta watsa taso shiga duban Ummimi amman Anas ya hanata. Bayan ta shirya cikin kayan baccinta ta zauna kan gado tana ma kanta tausa a k’afafunta, fitowan Anas daga wanka kenan singlet da nickers yasa ya hauro gadon yana k’are mata kallo. “Flower.” Shiru tayi bata tanka sa ba. Kusa da ita ya matso “Flower bara kimin magana ba?” Nanma shiru se massaging kumburarrun k’afafunta take hannunta ya d’aga daga kan k’afan nata nanma bata ce masa ko k’ala ba. “Flower wai barakimin magana?” Nanma shiru. “Okay I’m sorry kinji? I’m sorry.” “Kasakemin hannu as you can see am massaging my legs.” “Flower I said I’m sorry.” “Naji sakeni toh.” “Bari zan miki.” “Banaso zanyi abuna da kaina.” “I’m sorry” ya sake hannun nata tare da kama kunnuwansa ko kallonsa batayi ba ta cigaba da massaging k’afanta. “Flower please.” “Wai hak’urin me kake bani? Nace kamin laifi ne?” “Baki fad’a ba amman nasan na miki laifi and I’m sorry kije kisameta in kinaso.” “Banaso” ta fad’a stubbornly. “Yi hak’uri mana Mom Hanan” ya sake matsowa kusa da ita closing the gab between them, gashin kanta data barbaza a kafad’anta yahau shafawa. “Yi hak’uri kinji barin sake ba.” Kallonta ta miyar garesa “I’m sorry sweetheart” d’an murmushi ta sakar masa ma’anan ta huce. “Thats my woman!” Lips nata yasoma laluba bata hanasa ba se dab da bakinsu ya kusa had’iye tasa hannu ta kama mai baki “no kisses today thats your punishment” tayi maganar tare da miqewa daga kan gadon ta sanya hijabinta. “Oh common please Flower ko peck ne.” “Nace NO! Gobe zaka sake repeating abinda kayi yau.” Tana kaiwa nan ta fice zuwa d’akin Ummimi. Some minutes later ta dawo har anan Anas beyi bacci ba yana jiranta, a nitse ta cire hijabin ta haye gado ta kwanta ganin bata matso kusa dashi ba yasa ya matso dakansa tare da zama. K’afanta ya miqar kan cinyansa sannan ya fara mata massaging. “Ta nan ka b’ullo kenan? Saboda in ka gama in baka kiss as token of appreciation, uh-uh yau ba kiss na fad’a maka smart guy, wannan logic nakan bareyi aiki ba yau.” Dariya yaso yi dankuwa ta kamasa amman seya matse. “Ni ba haka nace miki ba am massaging your legs because I love to” “Humm! Allah sa de, nagode” bayan daya gama yaja d’ayan ma yamata godiya ta masa sannan ya kashe musu wutan ya koma ya kwanta agefenta yana wasa da gashin kanta duk wani salo nashi yayi applying amman Fannah tak’i bari yayi kissing nata haka yatayi har ya gaji seda tajishi yayi shiru sannan ta juyo tana kallon shi unexpectedly tayi pecking nasa a lips. Kafin ta d’ago kanta ya riqeta gagam yasoma sarrafata haka sukata romancing junansu har seda bacci b’arawo yayi gaba dasu. © MIEMIEBEE

Share:

1 comment:

pls drop down your comment......
dan Allah ku ajiye comment.

Tallata Kayanka

Guide Tricks Blog

Be With Me Technology

Popular Posts

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).