shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wanda aka fi sani da hausa novel wanda ni Muhammad abba gana nake rubutawa dan wayar tare da fadakarwa ga mutane a yanayin da muke ciki.

Tuesday 3 January 2017

Waye Sanadi?? 100 (karshe)




💘WAYE SANADI?💘 1⃣0⃣0⃣ 💘💘💘 💘💘💘 💘💘💘 💘💘💘 💘💘 💘💘 💘 💘 💖MUH'D*ABBA*GANA💖 www.MuhdAbbagana.blogspot.com Mun sauka Kano ranar da za a yi dinner sai da na fara zuwa gidansu Momy da Sadiyya, sannan na tafi gidan Baba. Duk inda na sa kafa nan Imran zai sa tasa har muka tafi gidan Abbana. Na yi matukar farin cikin ganin Ummata. Bayan na gama cin abinci ina tare da Hassan Imran ya shigo dakin da nake Safiyya amaryar Imran kamar yau aka yi tamu dinner ana hararata tare da takan 'yanyatsu Na ce Me ye haka kai kai ka fiya tuna baya, wacce irin kulawa ce bana baka? Ya zauna kusa da ni, ki yi hakuri Safiyya Abba ya hana zuwanki dinner. Na dago da sauri kar ki damu mu yi zamanmu nima babu inda za ni, mu yi zamanmu mu yi tamu dinner mai tarin lada. Na dan yi murmushi Nima bana jin dadin jikina tunda za mu taho marata take ciwo Ya mike da sauri, 'Ban san shirme baki da lafiya tun safe baki gayan ba, ta so maza mu tafi asibiti cikin sirri kamar unguwa za mu, tunda daman da kayanmu a mota Ban yi musu ba na bi bayansa muka fita, don nima marar tawa dada takuran take. Ya yi kiran Doctor Khadijah ya tambaye ta tana asibiti ko gida? kai tsay asibitin Nassarawa muka nufa. Awa biyu da zuwanmu cikin iko na Ubangiji na haifi yarinyata mace. Imran ya rasa inda zai saka kansa saboda farin ciki. Ya shigo dakin hutun ina zaune na zubawa bayna ido cikinso da kauna. Duka awarmu biyar a asibitin muka fito tare da dankareriyar kyautar da Ubangiji ya yi mana Iokacin da muka shiga gate din gidanmu Abbana ne a zaune su da Abban Imran Lokacinda Abba ya ga na fito dauke da yarinya a hannuna bai san lokacin da ya mike tsaye ba Dadyn Imran ya ce Kai Imran yarinyar wace ce? Ya karasa yana dariya ya ce, “Dady ‘yar Safiyya ce daga asibiti muke ta haihu Duk wanda aka gayawa haihuwata ba karamin mamaki yake ba, haka ‘yan party da suka dawo. Ina gani aka tafi aka kai Momy da Sadiya gidajensu. Ba mu yi wani gagarumin taron suna ba sai walima da muka yi. Baby ta ci sunan mahaifiyar Imran Amina. bayan na yi arbain na koma gidana wanda ba mu da nisa da Rukayya illa Sadiyya da take Kano. Zaman da kauna muka shiga shimfidawa. Aminatu ta taso cikin kulawa da soyayya daga kowane bari Alhamdulillahi. Nan na kawo karshen wannan labari nawa mai suna *💖Waye Sanadi?? 💖* *SADAUKARWAR: Na sadaukar da wannan littafin ga masoyana* GAISUWA TA MUSAMMAN A GAREKU 🍄Raheem Jega 🍄Baby Afreen 🍄Hajiya Zahra B.B 🍄Abdul mr smile 🍄Abdulaziz A.A J 🍄Mrs Bilkisu 🍄Kurratulayn 🍄Herleematus Serdeeya 🍄Billy gero 🍄mrs umar 🍄Hauwa jabo 🍄Autan Hajiya 🍄jeedah aleeyu BAN MANTA DA KU BA ... . ➡ONLINE HAUSA WRITERS ➡HOME OF NOVELS ➡NOVELS ➡Hype Hausa Novels ➡ Novels Only ➡ Duniyar Marubuta ➡Home of Nobel ➡Hausa novels ayau Members na group na 📚HOUSE OF NOVELS 1-5📚 da dukkan wanda ban ambata ba nagode INA MIKA SAKON GAISUWATA GAREKU MASOYA NA ALLAH YA SADAMU DA ALKHAIRINSAH *💖Muhammad Abba Gana💖* *09039016969*
Share:

0 comments:

Post a Comment

pls drop down your comment......
dan Allah ku ajiye comment.

Tallata Kayanka

Guide Tricks Blog

Be With Me Technology

Popular Posts

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).