shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wanda aka fi sani da hausa novel wanda ni Muhammad abba gana nake rubutawa dan wayar tare da fadakarwa ga mutane a yanayin da muke ciki.

Friday 20 May 2016

WAYE SANADI?? 13&14

waye-sanadi.jpg

[3:31PM, 5/15/2016] Ábbā-Gãñå: WAYE SANADI?

13


MUH'D*ABBA*GANA
09039016969

www.abbagana.pun.bz

na katse na ja tsaki har kin sallami yayan naki okey ke ba ya yanki bane abin ba kara nao dariya sorry sahiba gaskiya na fada saboda ni dayace banda yaya mamana ta haifa ai ko inda kina da yaya dai sai nace ina a aiki cikin mamaki nace saboda me? don nasan zai kasance kyakyawa kamarki kinga ko kasami namiji mai kyanki ko haye bbu inda baza ka shiga ba ke,wallahi kin fiye ban dariya karfe biyu da rabi na koma gida kaka tana zaune tana kada lagwani na shigo ban ko kalleta ba na shiga ciki sai nayi wanka nayi sallah sannan na dauko sallaya da jakata na fito soro madam kaka ina abincina naji gidan kanshi dambu kike yi,"sai yanzu kika san da mutum a gidan mara kunya tana maganar tana cigaba da kada lagwaninta keh kaka me kuma nayi na rashin kunya na shiga ukuna kullum cikin laifi nake a wajenki ban taba yi miki gwaninta ba,amma shi kenan inna gudu na barku kwa nemin wata rana.in kin gudu sai me baki ji wani tsohon mawaki ba yace yawon duniya mafarki kowa yayi shi dole ya farka,kaka sharrin da zaki min kenan koh? ina batun sharri ko gaskiya ni kinga rabu dani in kuma yanzu ma kashe ni zaki yi to baki na bude kamar me hamma.wane ni na kashe kaka mu rayu dawa? oho miki sakarya kawai okey kakas magana ta wuce "wai wani rashin mutunci kike ji kike batan suna saboda wuyanki ya isa yanka to wallahi ki bi duniya a hankali "wai kakas meye haka ina ta binki ta lallami in kuma kin fiso muyo fada to ki ban abincin kin tsaya wani wa'azinki sai kace malamar gaske nan ko karatun sallah sai anci gyaranki inda bani nake koya miki karatu komai ba 'kin wa rakiya ita ce bata iya komai ba shegiya mara kunya wallahi indai haka ki kace zaki ringayi kinyi asara kuma in kinci dambun nan kinci hantar uwarki dan ba ubanki ne ya ban kudin ba.can ta matse miki dambun kuma kici ke daya kashen sa zakiyi.....wani yaro ne ya shigo shigan lagwani kai zo ka karbon lemon kwalba na shiga na dauko safayar kwalba na bashi bayan ya dawo ya cillan bakar leda a fuskata gashi nan inji kado (Dan malam mado ne shege kado har ya hado yaji kudin yaji banza ta wadi to ni kaka me zanyi da kudin kya kara jari ki kuma rike a hannunki.au ni zaki tsokana tana magana tana hararata "Allah vaba bada wasa nake ba in kuma ba kya so na fita na bayar sadaka kinga kin hutar da kanki"


Abbagana hausa novels @ faceebook.
[3:33PM, 5/15/2016] Ábbā-Gãñå WAYE SANADI?

14


MUH'D*ABBA*GANA
09039016969

www.abbagana.pun.bz

ai shedanne mai maida alkairi bazan so na zama shedaniya ba,na gode Allah yayi miki albarka" wai yau wace rana kaka ta samun albarka haba takwarata ai ke kike jawo abinda zamuyi fada,wallahi duk abinda zan fada miki gaskiya ne nake gaya miki,nana yau ko namiji anayi mishi fada ballantana ke mace duk abinki wata rana gidan wani zaki je,in kuma ki kaje da wannan halin wallahi ba zaki taba jin dadin rayuwa ba son......" kinga abar maganar yanzu zaki ban dambun ko na hakura? ya za ayi na hanaki dazumma ke kika bata min rai wallahi nana dan muna kaunarki ne shi yasa muke miki fada kum....."ringing din wata ne ya sata tayi shiru tana kallona na zaro na daga in ka kara kirana ban yafe maka ba ina fadan haka na katse.ke kuma da wa? kaka take tambayata wallahi kaka wani ne yake neman ya takuran haka kawai yake ta kiran wayata.to ki dai a sannu tana maganar ta mikon plate ta juya tayi ciki ina cikin ci text message ya shigo"wallahi ba zan taba daina kiranki ba,har sai kin tsaya mun yi magana ta nutsuwa na san wrong number na kira to amma kuma sai naji zuciyata tana ban sha'awarar ci gaba da kiranki,banza wahalalle sai kai tayi can ta matse ma.bayan sati daya yau tun safe nake ta hada kaya kaka sai dariya take to nana ta dan Allah in kin je karkice zaki gwada musu halin naki ki tausayawa uwarki karki sata magana tun da zaman aure ne ya kai mahaifiyarki ciki.dabara tayi min saboda tayi min nasiha amma saboda zumudi sai amsa mata nake da to_to karfe takwas muka ji sallamar alhaji nasir kaka ta fito tayi masa shinfda lokacin ina sallah a tsakar gida,bayan sun gaisa ta debo masa ruwa Alhaji ya iyalin? vaba lafiya klau da tare da rukayya zamu taho kan na koma gida ka ta shirya mutaho sai naga lokaci yana kara kurewa dan haka na taho ni daya,daukar ta nazo yi dan munyi kewarta ya juyo yana kallona lokacin ina addu'a ina juyowa naga yana kallona na harareshi naci gaba da addu a kaka ina kayan nata nasa a bot,ai gasu a gabanta nana yau tun safe ake faman zumudin hada kaya za a ga umma ita ma umman tayi kewarta kullum hiranta daya nana"yana fitar da kayan na hau kan kaka da masifa meye zaki wani ce ina ta zumudin sai kace zani wani gidan gwal ni bana son irin haka mutum sai wani rawar jiki yake yaga mai kudi na mike na fita bbu ko sallama zuwa nayi na jingina da motar yana gama gyaran kayan ya ganni a tsaye "ah safiya har kin fito? ban ko kalle shi ba na amsa a dakile.


Abbagana hausa novel@ facebook.
Share:

5 comments:

pls drop down your comment......
dan Allah ku ajiye comment.

Tallata Kayanka

Guide Tricks Blog

Be With Me Technology

Popular Posts

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).