shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wanda aka fi sani da hausa novel wanda ni Muhammad abba gana nake rubutawa dan wayar tare da fadakarwa ga mutane a yanayin da muke ciki.

Wednesday 18 May 2016

WAYE SANADI? 1

WAYE SANADI?
1
MUH'D*ABBA*GANA
09039016969
www.abbagana.pun.bz
Misalin karfe sha biyu na ranar lahadi mama ta
nufi gidan alhaji mukhtar dake unguwar dorayi.Dan
Allah malam ina son ganin mai gida hajiya zuwanki
wajen nan uku yana kin fitowa ni gaskiya na gaji
da zuwa kiranshi dan Allah.dana ka taimaka min
wallahi in dai bai fito ba daga yau bazan kara
zuwa ba yayi cikin gidan yana shiga can ya dawo
kinyi sa'a yana zuwa to na gode nafi minti goma
kan ya fito har nayi tunanin tafiya na hango
fitowarsa yana cikin yana batsuwa ya karaso
wajen.yau kuma da me kika zo? bbu abin da naxo
maka dashi sai alkairi Alhaji ka dubi girman Allah
ka tausayawa rayuwata rakiya kuma ka tuna kaunar
da ka kewa rakiya har kai mata mugun sakamako
kinfa malama ya isheki ni da kuke so ku cuceni ku
batan suna ku zubar min da mutunci sannan ku
raina hankali magajiya kar ki dauke ni wanda bai
san me yake ba in baki sani ba ki sani in kuma kin
manta in tuna miki ni din cikakken likita ne wanda
yasan meye ke na riga na saki yarki ba aure a
tsakaninmu sannan kizo min da batun tana da ciki
har na tsawon wata uku yau duka rabuwarmu wata
biyu ya akayi ciki a jikinta har na wata daya ban
san dashi ba? to wallahi magaji yau shine
maganata dake ta karshe duk ranar da kika kara
zuwa nan gidan sai nasa police sun kameki maza
ki fice daga nan yar ku taje tayi abin kunya ana so
a likan daman can na aura bisa tsatsayi yanzu
kuma Allah ya rabamu,kuke neman doran masifa
ya juya ciki hajiya kiyi hakuri in har kuna da
gaskiya komai daren dadewa zata bayyana na
gode ta juya zata tafi ya zaro naira dari ya
bata.WANE NE DR MUKHTAR?
Dr mukhtar isah, haifaffen garin kano ne cikin
unguwar yakasai su hudu mahaifinsu suka haifa
binta da lamratu sai kuma sadiya sannan shi dan
auta dukan su sunyi aure har ma sun aurar da
ya'yansu sun sami jikoki shi ka daine Allah bai
bashi haihuwa ba Allah ya zuba masa son yaya
yayi aure aure da dama duk dan ya samu haihuwa
amma shiru yana zaune a dorayi da matansa
biyu,hajiya zuwaira da hajiya saratu yana yawan
karbar yayan yan uwansa ya rike amma rikon baya
zuwa ko ina saboda makircin matansa ana cikin
haka ya hadu da rakiya bafula ta nace suna zaune
a fanshekara,a salinsu yan gongola ne rakiya
yarinya kyakkyawa dr mukhtar ya nuna mata
ra'ayinsa nasan ya aureta ka ba a sha wata wahala
ba, ta amince nan da nan magana ta kankama har
takai batun aure sai dai tun shigarta gidan bata

taba farin ciki ba koda na minti daya ba,

MUHD*ABBA*GANA

Abbagana hausa novels @cfacebook.

Share:

0 comments:

Post a Comment

pls drop down your comment......
dan Allah ku ajiye comment.

Tallata Kayanka

Guide Tricks Blog

Be With Me Technology

Popular Posts

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).