shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wanda aka fi sani da hausa novel wanda ni Muhammad abba gana nake rubutawa dan wayar tare da fadakarwa ga mutane a yanayin da muke ciki.

Wednesday 7 September 2016

TANA TARE DANI...51--55

TANA TARE DA NI...

TANA TARE DA NI... PAGE 51
BY MIEMIEBEE


Nishi take sosai tana hak’i a yayinda zuciyarta ke bugawa d’ari bisa d’ari, ko damuwa ta kewayo dan ganin ya cikin gidansu Anas yake bataiba, abinda tasani kawai gidan nada kyau, bayan ta tabbata dawakan sun wuce tagwada bud’e k’ofar daidai lokacin Shettima ke dawowa daga yawonsa shima a tare suka tura k’ofar sede ya rigata. Suna had’a ido ya sakar mata da murmushi, murmushin ta mayar masa sede daga yadda take abu yagano tana cikin hanzari.
   
    “Fannah!”
    “Na’am Shettima.” Ta amsa.
    “Yau kece a gidan namu?” Ya tambaya yana mata murmushi.
   “A’a dawakai suka biyo ni, ina jiran Anas ne barin wuce please.” Ta fad’a cikin hanzari duk hankalinta ba’a kwance ba.
    “Fannah lafiya?” ya tambaya tare da sake blocking nata.
   “Shettima please ka matsa min in fice, kar Anas yaganni anan.”
    “Ya Anas? Shi yace karki shigo ne?” Shiru ta masa bata amsa ba hakan ya tabbatar masa da ‘eh’ ne amsar. “Karki kula sa haka yake shigo please kinji? Amal tayi missing naki.”
   “A’a Shettima, wataran zan dawo amman yanzu ka matsa min in fice please.” ta fad’a tana duba bayanta gudun kar Mr. Fauzi yaganta.
    “Haba mana Fannah yanzu baraki shigo ba? Yi hak’uri, Ummie naciki kinga seku gaisa kinji ko bahaka ba?” Kai ta girgiza masa tana tuna irin warning da Mr. Fauzi ya mata. “A’a I promise next time amman yanzu wallahi nashiga Anas ze sab’a min.”

    “Trust me ba abinda ze miki shi Ya Anas haka yake, sharesa please kishigo.” Nan ma kai ta kad’a “please mana Fannah sena had’aki da Allah ne? Kishigo please.”
    “Shettima wallahi Anas yace kar in shiga, kabari next time.” Kafad’a ya buga “ai wallahi sekin shiga Fannah, mubar musu kawai kinji? Bismillah.”
   “Shettima please...” Kai ya girgiza mata ganin ba mahalicci se Allah tace, “Shettima inyamin masifa fah? Seda yace min kar inshiga fa.”
    “Ai sharesa zakiyi, haka yake mushiga please.” A sanyaye tabi bayansa duk tsoro yabi ya ratsa ta tunanin wani erin masifa zata sha wurin Mr. Fauzi kawai take, sun kusa da bakin k’ofar ganin Shettima bai ganinta taja da baya zata gudu aiko tuni yaganta ta jikin mirron window karap ya cafko abayanta. “Fannah aini ba’a min wayo, mushiga kawai.”

    “Shettima kayi hak’uri please kabarni in tafi.”
   “Mushiga kawai Fannarmu.” Haka suka shiga cikin katafaren parlour’n su, dake d’auke da kayan tafiyar da imanin mutum a kowani second. Zaune ta iske Anas da Ummie kan kujera. Bayansa ta hango saboda kallon direction na Ummie dayake. A lokacin da idanunsu ya had’u da Ummie kuwa tayi saurin sunkuyar da kanta.
   “Shettima!” Ummie ta kira sunansa cike da mamaki ganinsa da budurwa. “Yau kuma budurwarka ka kataho mana da ita gida?” Jin an ambaci budurwa Anas ya juyo dan ganin wannan budurwar Shettiman yayi dariya.

    Ai zubewa ne kawai idanunsa basuyi ba a k’asa dan yadda ya warwarosu ganin FANNAH a parlour’nsu. Inba wai ya manta bane he made it clear to her karta kuskura tashigo. K’in d’ago kanta tayi su had’a ido tinda taji alamun blue eyes nasa a kanta. Yafi minti d’aya yana kallonta totally speechless bema san me zece mata ba dan yadda tabasa mamaki.
    “A’a Ummie ai wannan tafi k’arfina zubin billonaires ne da ita” cewar Shettima har yanzu Anas bebar kallon Fannah ba launin fuskarsa take ya koma ja dan b’acin rai ko sauraron Shettima ma beyi ba. “Dade Ya Anas kika tambaya bare rasa amsar da kike nema ba.”  Se yanzu hankalinsa yadawo, kallon Shettima yake tare da watsa masa wani irin wawan kallo.

     “Kai Shettima deh!” Cewar Ummie cike da zumud’i. “Fannah ga Ummie, Ummie ga Fannah.” Shettima yayi introducing nasu wa juna. Har k’asa Fannah ta tsuguna ta gaishe da Ummie cike da girmamawa, itama Ummien cike da fara’a ta amsa ta. “Taso ‘yata taso dan Allah” kafin ace meh Ummie taje ta r’iko Fannah tare da k’ariso da ita kan kujeran da suke zaune da Anas, a yayinda ta zauna kan hannun kujerar irakuma se kallon Fannah take kamar ta cinye ta, Fannah kuwa fitsari ne ya matse lokaci d’aya dan har yanzu Anas bebar kallonta ba.
    “Shettima kace wannan kyakkyawar ba budurwarka bace?”
   “A’a Ummie, Ya Anas kama Ummie explaining mana.”
 
    Kallonsa yadawo gare da Shettima, “wallahi inbaka min shiru anan ba zan maka duka.”
    “Kai Ya Anas a gabantan ma bara muyi koda shirin k’arya ba? Ai ganga ake bugi ba mutum ba. Zaka fad’awa Ummie wace ita ne ko in fad’a mata.” Takalmin k’afarsa yayi yunk’urin cirewa, Shettima na ganin haka ya lab’e bayan labule. “Fannah koh?” Ummie ta tambaya a nitse.
   “Eh Ummie” ta amsa ta cikin siriryar muryarta.
   “Toh Masha Allah ke da wa kuka shigo?” A hankali ta d’aga kai ta kalli Anas da ba abinda yake in banda hararan dayake watsa mata, miyau ta had’iye takasa amsa tambayar Ummie duk tsoro ya cika ta.

    “Ita da Ya Anas ne” cewar Shettima dake lab’e bayan labule. “Wai Ummie ke baki gane bane? Budurwar Ya Anas ce fah.” Ido gam Fannah ta matse tana niran sauk’an duka.
    “Budurwarsa fa kace Shettima? Alhamdulillah!” Rungumo Fannah tayi, se mammatse ta take a jikinta. Anas ji yake kamar ya k’urma ihu dan takaici da bak’in ciki.
     “Ashe Allah ze nuna min ranan da Babana ze kawo min mace gida, kai alhamdulillah. Fannah tunba yau ba nake jirar wannan rana, ranarvda zamu had’u. Allah miki albarka, kai nagode. Kinga sekina hak’uri da Baban nawa sabo-” bata k’are maganar ba Anas ya katse ta.

    “Wai me haka Ummie? Nifa ba budurwa ta bace, tsiyar Shettima ne kawai, ke tashi mu tafi.” Yace da Fannah alokacin daya dawo da kallonsa gareta yana galla mata wani erin harara.
   “Baba na meyayi zafi? Ai wannan ba abar b’oyewa bace iyyeh? Ko rowarta kake mana ne?” Shafo fuskar Fannah tayi “ ‘yata karki jisa kinji? Yi zaman ki.”
Cike da kunya da tsoro tace, “uhm Ummie ba buduwarsa ce ni ba, wasa Shettima ke miki.”
    Da murmushi sosai a fuakarta tace  “ni nagane ‘yata, Allah barmin ku tare. Barin kawo miki koda ruwa kinji?”
 
   “Wai Ummie meh haka ne? Kekuma tashi mutafi.” Anas ya fad’i a fusace.
   “Ba inda zataje, Shettima duba ko Abuu na gida ka masa magana.”
   “A’a Ummie karki damu please-” Fannah bata k’are maganar ba Ummie ta katse ta “ ‘yata karkiji komai kinji? Feel free, feel at home. Jeka duba Abuu Shettima.” Nan ta fice kitchen a yayinda Shettima yaje duban ko Abuu na gida shima, yarage daga Fannah se Anas. Hannunta ya kama tare da murd’awa cike da mugunta. K’ara ta saki “arghh! Mr. Fauzi please ka sake min hannu da zafi.” take hawaye ya soma cikowa a idanta.

    “Da zafi? Me nace miki amma, didn’t I tell you kar ki shigo? Mesa bakiya jin magana ne?” Azaban ne yamata k’ak’a har hawayen suka soma tsiyaya dan yadda ya murd’a hannun nata. Daidai nan Ummie tafito da tray cike da snacks da drinks akai. “Ya meke faruwa?” ta tambaya alokacin datake k’arisowa cikin parlour’n. Hannun Fannah ya sake da wuri gudun kar Ummie tayi suspecting wani abu amman ina ta riga ta hango hawayen dake mak’ale cikin idanun Fannah.
   
    “Ya Salam Mama na meya sameki?”
    “Bakomai Ummie abu ne yashiga mata ido.” Anas ya amsa tun kafin Fannah da aka tambaya tayi magana. “Sorry dear ya fita? Muga.” Kamar dagaske yawani sa hannu yana duban idanta harda hura mata iska.
    Hawayen ta had’iye “shikenan yafita” tare da kawar da kanta ba tare da ta kallesa ba. Serving nasu drinks d’in tayi. “Bismillah uwata” Ummie tace da Fannah. “Babana fad’amin mana toh ina kuka had’u da Fannah?”
     “Ummie please me haka ne? Fannah tashi mutafi.”
    “Yanzu Anas itanma se an mana rowanta?”
  K’arya ya mata, “Ummie we need to go ne, zan kawo ta some other day.”
    Dad’i sosai taji “ka yarda budurwarka ce kenan.” Ta fad’i dawani shu’umin murmushi tattare a fuskarta.
   
     Shiru yayi kamar be jitaba. “Anas fad’a min mana.”
    “Eh Ummie shikenan kinji? She is my girlfriend. Tashi mutafi Fannah.” Daidai lokacin Shettima ya dawo “Ummie Abuu fa bai gida kuma ga motarsa a pake.” Wani sanyi Anas yaji a ransa bashi kad’ai ba hatta Fannah dagajin Abuu bai gidah. Mik’ewa yayi itama haka, ko jiran tama Ummie se anjima beyi ba yasoma janta, itade Ummie cike da mamaki take kallon Anas budurwarsan ma bare saurara mata ba.

     Bayan sun shiga mota ya soma suburbud’a mata masifa wane an turoshi. “Wai ke mesa bakiya jin magana ne iyyeh? Didn’t I tell you karki kuskura ki shiga? You are not my girlfriend you are just a fake one banasan family na su ganki, kin huta ai yanzu da Ummie taganki mschww! Mutum ace mishi don’t amman seyayi.”
    Hawaye take sosai “Sir kad’au wai dagangan na shiga gidanku ne? Doki ne ya biyoni ta fad’i” cikin kuka tana share hawayenta.
    “I still don’t care!” Ya fad’a a tsawace. “Acikin motan me ze miki? Msschw! Kin d’au wasa nake ba, you’ll be suprised 1000 paper zan baki kiyi correcting.” Kukanta ne ya tsananta kamar ‘yar yarinya ta tsaya tana kuka harda me sauti tsuka yaja ya soma driving ganin kukan nata bana tsayawa bane ga kuma kukan ya soma damunsa ya tsaya gefe guda akan titi. Ko d’ago kai ma batai ba se kukanta da takeyi kanta cuse cikin cinyarta.

     “Toh kukan ya isa” ya fad’i a hankali. Banza tayi dashi ta cigaba.
     ‘Sorry’ yakeson fad’a mata amman bare iya ba, “ya isa I shouldn’t have shout at you kinji? Stop crying” namma bata bar kukan ba. “Okay barakiyi correcting 1000 papers d’inba, I take that back, bar kukan.” Bata d’ago kai ba har a yanzun sede ta d’an rage kukan nata. “Bafa dan wai inaso bane na shiga gidan naku, doki har biyu ne suka biyoni ni nikuma inajin tsoro, dana shiga na had’u da Shettima, shine yayi insisting sena shiga.” Ta sanar dashi cikin sautin kuka.
     Sekuma yaji wani iri amman ai still da ta shiga koda gidan neighbours ne. “Toh d’ago fuskarki, kukan ya isa na fad’a miki banasan jin kukanki.” Tana d’ago kai ya mik’a mata hand kerchief nasa, amsa tayi ta share hawayenta a yayinda yayi zaman kallonta, kukanta na d’aya daga cikin abubuwan da yake burgesa a gareta, abu kad’an setayi kuka. Ice cream shop ya wuce da ita bata ce dashi komai ba. Bayan yayi parking yafito ya bud’e mata nata tare da rik’o mata hannu mutane kad’an suka samu ciki.

   Kap flavours dayasani na ice cream seda ya siye mata amman kuma bece mata nata bane haka suka dawo cikin motar, zaman makoki suka tayi har seda ya kawo ta gaban gidansu, a nitse ta bud’e k’ofar ko se anjiman ma batayi niyyan fad’a masa ba “girlfriend” ya kirata, banza tayi dashi da sauri ya cafko abayanta kafin ta rufo k’ofar. “Your ice cream take it.”
  “Banaso” tace tana turo bakinta, har yanzu haushi yake bata jibi yadda ya riga mata masifa.
    “Girlfriend take it kinji?” Hak’urin nan de dayakeson bata ne ya kasa. Ganin battada niyan d’aukawa yace, “okay barin sake miki masifa ba, kema obey all my rules yanzu d’auka kinji?”

    Wato shi be iya bama mutum hak’uri bako? Tace a ranta. “Ni ka sakemin abaya in tafi.”
     “Fannah” yakira sunanta yadda takeso “take it kinji? Barin k’ara ba.” Kallonsa tayi na ‘yan seconds sannan ta ciro ledan tayi tafiyarta ko godiya babu.

★★★★★

    “Ummie dan Allah Ya Fannah tazo?” Amal ta tambaya.
   “Eh kai!” Ummie ta amsata se dad’i takeji Anas yakawo budurwarsa gida. “Yace ze sake kawo mana ita karki damu.”
   “O’o ni barin yarda ba. Ni zanyi inviting nata birthday party na.” Daidai lokacin Anas yake sa kai cikin parlour’n da alama yajiyo abinda Amal tace just now.

    “Wa zakiyi inviting a birthday nakin?”
   “Ya Fannah mana Ya Anas shine ko ka fad’a min zaka kawota, amman ka iya cemin kar in fad’awa kowa picture’nta dake wayarka.”
   “Rangem! Ya zama fashashhen k’wai” cewar Shettima yana daka tsalle. “Ashe abin kenan, wayyo! Ya Anas ka nunwa Ummie mana taga hoton surikar tata.” Dafe baki Amal tayi batasan lokacin data fad’a ba. “Ya Anas I’m sorry wallahi bansan ya akayi na fad’a ba.”
   Wani irin kunya ne ya ratse Anas dayakeji kamar ya tone k’asa ya shiga ai yanzu shikenan sekowa ya zata eh son Fannah yake, bece da Amal komai ba illa k’arisowa cikin parlour’n da yayi a gaban Ummie ya tsuguna.
    “Ummie please kar kowa ya fad’awa Abuu yau wata ta shigo gidan nan.” Cike da mamaki Ummie ke kallonsa “toh Babana ai abu ne me kyau kuma shima dad’i zeji.”

     “A’a Ummie ni kawai kar kowa ya fad’a masa kaji Shettima?”
   “Senayi tunani tukun” yabasa amsa yana kallon yatsunsa dan tsiya.
   “Zan baka kud’i wallahi yanzu ma kaje ka d’auka bundle na d’ari biyu ni kawai kar ka fad’a masa.” Shettima lashe money najin haka yace “karka damu Ya Anas your secret is safe with me” take yayi d’akin Anas. Instead ya d’au na d’ari biyun seya zari na d’ari biyar dan kud’in suna nan ne ba adadi. Bayan yafito Anas yace, “muga nawa ka d’auka.”

    “Ji Ya Anas de baka yarda dani bane?” Wayarsa yaciro kamar ana kiransa. “Lecturan?” Yayi pretending yana kan waya. “Toh gani zuwa.” Aiko sauraran Anas beyi ba yafice shopping, yau za’ayi renewing wardrobe.

**

     “Ya Anas amman please ka amince inyi inviting nata birthday na ran monday, please Ya Anas.”
   “Eh mana Babana kabarta tazo kaji?” Ummie tasa baki.
   “A’a Ummie nikam kunga matsalar dayasa banso shigowar yarinyan nan ba kenan.”
   “Toh meh aciki? Ai wallahi ko ka yarda ko in fad’awa Abuu yaso nan da wata ma ayi bikinn mu huta, in tanada k’anne ma duk su taho tare.”
   “A’a please na yarda zan fad’a mata ni kawai karku fad’awa Abuu. Ita kad’aice batada k’anne.”
  “Ya Anas amman fa akoi wata Aiman da muka tab’a gaisawa da ita.” Kunya yaji an kamasa yana k’arya. Wani kallo Ummie take masa ina irin angano kan nan.
  “Toh meh? Ai ba k’arya nayi ba na mance ne.” Nan ya tashi yashiga d’akinsa se huci yake shi ya tsani abunsa haka. Yanzu what if Abuu ya had’u da Fannah kuma fah? Mschww! Wayarsa ya zaro daga pocket nasa ya danna mata kira alokacin kuwa ita dasu Aiman da Afrah duka suna zaune suna shan ice cream nasu. Ganin shi ke kira tak’i d’agawa halan wani masifan yakeson mata. Seda yakusan tsinkewa ta d’aga “hello” tace a hankali, Afrah kam ko kyafta ido battayi dan gulma ganin haka Fannah ta bar musu d’akin.

    “Kin iya shiga gidanmu ba? Ai gashi yanzu Amal tace sekinzo birthday’n ta ranan monday mutum ace masa don’t amman se yayi.”
   “Birthday’n Amal? Toh Sir kace musu zanyi tafiya mana ai ba lalle ne senaje ba tunda baka so.”
    “You should have thought about that ai kafin kika shiga, daman abinda kikeso kenan kisamu kina shigan affairs na family na.”
   “Ni ba abinda nakeso ba kenan kuma barinje ba, shikenan?”
   “Miss Aleeyu don’t dare me, Monday by 4:00PM driver zezo ya d’aukeku dasu Afrah duka inform them, ni na fad’a miki” karap ya katse. Harara ta watsa wa wayar wane shine Anas d’in. Bayan takoma ciki tabasu Afrah labari ai ice cream da ba’a gama sha ba kenan dan dad’i. Kayan wardrobe nata ta zazzage duka ana neman kayan zuwa party ganin ba wanda ya gameta ta yafo mayafinta suka fice shopping da Aiman.

© miemiebee

TANA TARE DA NI...

TANA TARE DA NI... PAGE 52
BY MIEMIEBEE


English wears had’ad’d’u na ‘yan gayu maras tsireci ta siya wa kanta sannan wani had’ad’de wa Aiman itama bata damu da Fannah ba saboda tasan bara’a rasa d’aya cikin kayakin da Anas ya siya mata ba.

    2 days later...
   _Monday 3:30PM_

     Kaya ne wargaje cikin d’akinsu Fannah, su Afrah ana shirin zuwa party. Ba hassada tayi kyau, kayan ya mata kyau makeup nata yayi kyau, kamar yadda ta tsara kanta haka ta tsara Aiman ma dukansu biyu sunyi kyau banda Fannah dake zaune kan gado tana buga candy crush da towel d’aure a k’irjinta.
   “Wai Ya Fannah bara kije bane? Dubi time fa! Ga kayanki nan tun d’azu na cire miki kink’i sawa.” Cewar Afrah
     “Barin jeba in kun had’u kice masa banida lafiya.” Daidai da shigowar Mami kenan “waye ne baida lafiyan?”

    “Mami wallahi gatanan tak’i tashi ta shirya.”
  “Mami wallahi k’arya take, yanzu fitowa na daga wanka ko Aiman? Ina kayan nawa insa. Wane ni ace birthday na in-law na barinje ba.† Kallonta Afrah ke cike da mamaki. Kayan ta jawo ta zira wata maroon doguwar riga ne har k’asa me hannun vest da kwalya sosai a jikinsa ta saman, bayan tasa shi ta d’auko wata had’ad’d’iyar ash-ash jacket me siririyar dogon hannu dake shek’i ga kwalyan stones daya sha, yana nan da tsayi shima har kusan k’asa amman be gama kaiwa ba, ta d’aura akai. A bud’e yake saboda ya bayyano da kwalyan dake d’auke da doguwar rigar dake cikin. Afrah ce tamata makeup d’in basu d’au lokaci ba saboda ba wai gira za’a zana mata ba. Maroon gyale tayi rolling dashi seda ash jaka da takalmi data sa. Feffeshewa sukayi da turare 4:00PM on the dot driver’n yamata waya kan gashi nan.

   Allah kare Mami ta musu suka fice. Daidai gaban gidansu Anas ya tsaya bayan an bud’e gate ya shiga dasu. An k’ayata filin tsakar gidan da had’ad’d’en decoration na red and white, tsayuwa dan kwatanta kyan wajen ma b’ata lokaci ne. Bayan sun fiffito daga motar suka tsaya chak Afrah da Aiman kam se k’are wa gidan nasu Anas kallo suke bada jimawa ba gate ya bud’u motan Shettima ya  bayyana. Yana ganin Fannah yaji wani dad’i ko lura dasu Afrah beyi ba seda ya fito suka gaisa da Fannah sannan idanunsa suka sauk’a kan Afrah (fire) kasa dena kallonta yayi dan had’ewar data masa, ashe ba Ya Anas kad’ai keda rabo ba harda nima ya fad’a a ransa.
    “Ina wuni?” ta gaishe sa.
   “Lafiya sannu ko? Fannah kuna kama ko sister kice?”
   “Eh sunanta Afrah wancan kuma Aiman.”
   “Wow pretty ladies sede ma Afrah duk tafi ku kyau.”
    “Noi! Wani kyau tafimu? Kwalya de ta fimu, nida Aiman duk munfita kyau.”
   “A ganinki kenan nide Afrah tafi min kyau.” Afrah kam se blushing take, wani me kama da Blue eyes yace mata tanada kyau.

       “Fannah kushiga daga ciki su Ummie suna parlour you all are welcome.† Duk wannan magana dayake yakasa d’aga idanunsa daga kan Afrah.
   “Tam, taho muje Aiman, Afrah lets go.”
    “A’a ni dakaina zan kai Afrah koban fad’a miki tafi ku kyau duka bane.” A hankali ta d’ago idanunta da suka sha tozali da liner ta azasu kan Shettima dake d’auke da murmushin dayake k’ara masa kyau, murmushin ta mayar masa, “lets go ko? My lady.,By the way I’m Shettima, k’anin Ya Anas amman fa karki d’au wani babban bro na ne, dududu shekara d’aya da rabi yabani.”
   Murmushi sosai Afrah ke harda ‘yan hakwara a waje.

    “Nima ai, 1½ years ne kawai tsakani na da Ya Fannah.”
   “Owww really? Zo mud’an fita kafin programme d’in ya fara.” Motarsa ya bud’e mata tashiga se rawan jiki yake yasamu ‘yar kyakkyawa. A ice cream shop ya tsaya suka sauk’a, kud’in Ya Anas zeyi amfani.
      Bayan an kawo musu ice cream d’in suka soma sha a hankali. Cikin d’an k’ank’anin lokaci suka saba sosai, dake halayensu na neman tsokana da neman zance duk d’aya ne, labarin abubuwan da suke ma yayunsu suka rigayi, bayan sun gama chan suka tab’o b’angaren karatu Shettima harda zuzutawa wai yana d’an business. Afrah ta jima tana nan perfect boyfriend segashi tasamu kyakkyawa k’anin billonaire. Ba b’ata lokaci Shettima ya fad’a mata santa yake, tunda idanunsa suka sauk’a kan kyakkyawar fuskarta yaji yana sonta. Aiko itama ma hakan ne, take sukayi exchanging I love you da I love you too. Bayan sun k’are shan ice cream d’in yakaita shopping duk acikin kud’in daya sata gun Anas ranan.

    Afrah kam dad’i kasheni.

     ****
   Fannah kuwa tun shigarsu gidan bata had’u da Anas ba taji Ummie na cewa baya gida ma, Abuu kuwa yayi tafiya, hamdala ta saki. Birthday girl ansha kyau sosai tana ganin Aiman taji tana san miyar da ita little sister tunda ita batada. Bada dad’ewa ba programme ya fara har a yanzu su Shettima masu soyayya basu dawo ba. Bada dad’ewa ba gate ya bud’u had’ad’d’iyar benz na Anas ya shigo. Bayan yayi parking yafito ko kallon direction na mutanen baiyi wajen Amal nasa ya nufa yayi wishing nata happy birthday tare da ajiye mata present nata na iphone 6+. Direct parlour ya nufa bayan yasha ruwa ya ciro wayarsa ya kira Fannah yaji ko sunzo. Tana zaune abinta taga call na Anas. Me kuma zece mata yanzu? Da k’yar ta d’aga “hello?”
  “Kunzo?” Ya tambayeta a takaice
“Eh.” ta amsa sa.
   “Ina kike? Kizo parlour yanzu ina jiranki” karap ya katse. Inje kamin me ta tambayi kanta kamar wacce barata ba, sekuma ta mik’e taje zaune kan dining chair ta samesa ya aza k’afafunsa kan table d’in yana kad’awa da wayarsa rik’e hannunsa. Sosai shirin dayayi ya masa kyau kodan bata tab’a ganinsa da erin shirin bane?
   Shima kallon nata yake, gani yake kamar bata tab’a kyau erin na yau ba, kodan be tab’a ganinta cikin english wears bane? Kasa dena kallonta yayi, da k’yar ya iya cemata “zoki zauna” tare da ja mata kujeran gefensa.
    A sanyaye tanufa wajen sede bata zaunan ba gudun kar Ummie tazo ta kamasu bibbiyu.

     “Mr. Fauzi you called for me, wani abu ne? Kaga I need to get back.”
   “Sit toh.”,Yi tayi kamar bata ji saba. Hannunta ya rik’o “sit first.” Dan kawai ya sake mata hannu ne ta zauna. Bayam daya k’are mata kallo kusan na mintuna biyu yace, “kinyi kyau.” ‘Yar murmushi ta saki, “thank you.” Dad’inta kenan da Anas duk sanda tayi kyau ze fad’a mata. Cameran wayarsa ya shiga yayi muting, yasoma d’aukanta hoto seyi yake kamar amfani da wayar yake.

    “About business trip da zanje Morocco ne, nafasa zuwa dake tunda you are now my girlfriend, zamuje da Kacallah.” Dad’i sosai taji.
   “Okay Sir.”
   “Call me Anas.”
   “Okay Anas shikenan zan iya tafiya?” Besan meh ba seyaji bayason ta tafi yafison ya kasance tare da ita always.
   “Jibi ne tafiyan nayi rescheduling.”
   Nanma “okay” tace. So barata ce masa ko safe trip ko Allah kare ba wato.
    “What kind of an I don’t care girlfriend are you? I’ll be travelling ko d’an safe trip babu.”
   “Toh Sir nag-”,sekuma tayi shiru ganin battada abin cewa “I’m sorry, safe trip Allah ya kare ya dawo dakai lafiya.” Chan k’asa k’asa yace, “ameen seda na tambaya.” Ita Fannah bata aza abin boyfriend girlfriend nasun a ka ba saboda batasan ta sake bud’e zuciyarta ma wani na miji because a k’arshen ita zata wahala danko duk na mijin daya gano some day batada budurci ze guje ta, abinda bataso kenan, maganin bari kar ma a soma.

   “Zan tafi.”,Tace a hankali.
  “No I want you to stay Fannah don’t go.” Har a yanzu bebar d’aukanta hoton dayake tayi ba haka yak’i  barinta ta tafi, kuma bawai hira yake janta dashi ba kallonta kawai yake yana d’aukanta hoto. Da kallon ya isheta tace, “Sir kaifa kace adena kallo dayawa.”
    “Yes amman ni ai am your boyfriend me aciki dan na kalleki? You also enjoy it when ever I’m starring at you so kidena pretending.”
    “Nima ai am your girlfriend amman dana kalleka sekace bakasan kallo, kayi adalci kenan?”
        “Miss Aleeyu kallon soyayya kikemin nikuma banaso, ni kawai kallonki nake saboda kinyi kyau.”
   
        “Toh nima ai saboda kayi kyau nake kallonka.”
         “Ni ai kullum inayin kyau, am handsome kekuma time-to-time kikeyin kyau.” Ganin inta sake magana ze iya zaginta tayi shiru kawai bata sake cewa komai ba k’arfe 5:30PM nayi ta mik’e “Sir zamu tafi kar Maghrib ya mana anan.” Hannun ta ya rik’o “I will take you guys home.”
     “No please karka damu we can go on our own.”
    “Fannah I’m your boyfriend I insist.”
    “Toh Mr. Fauzi kasakemin hannu please.”

   “No Fannah, I enjoy holding your hand, allow me.”
   “Sir ba kyau ne.” Kafin yace wani abu ta b’arke masa da kuka, shark’af shark’af besan lokacin da ya ciro hanky ya soma share mata hawayen nata ba. “Fannah why are you crying? Na miki wani abu ne? Kodan danace time-to-time kikeyin kyau? I don’t mean it kinji? You are beautiful, always looking gorgeous saisa nake kallonki kullum. Bar kukan kinji?”  Har yanzun be sake mata hannun ba duk yabi ya kid’ime ganin yadda take kuka. Baya san ganin ta tana kuka bayyaso ko kad’an.

      “Niba wancan ba” ta ce tana kukan still.
Sosai taji dad’i daya yaba kyanta haka. “Toh meneh Fannah? Stop crying please”
      “Anas ba kyau, akace da namiji ya tab’a jikin macen daba muharramarsa ba gomma yatab’a garwashi, azabansa kuwa yafi ad’au k’usa a buga masa a kai har se ya nitse. Anas banason amaka wannan azaba, banaso please kadena rik’e min hannu gomma ace ma muna da aure ne kake rik’emin hannun I wouldn’t mind amman a yanzu haka haramun ne, kadena kaji? Banason amaka wannan azaba, please.” ta k’are maganar tana hawaye. Shiru yayi chan yace a hankali “shine dalilin da kike kuka?”

   Kai ta giad’a masa a hankali har yanzu bata bar kukan ba. Hannunta ya sake a hankali “toh ya isa daga yau barin sake rik’e miki hannu ba kinji? Stop crying.” Da murmushi a fuskarta ta d’ago kai tana kallonsa “promise?”
   Kai ya giad’a mata.
    “Bani kad’ai ba kowace mace baraka sake rik’e mata hannu ba?”
    Nanma kai ya giad’a, “what of Amal? Har itama?” Ya tambayeta.
    “Amal muharramar kace zaka iya rik’e mata hannu da ita da Ummie amman banda matan waje.”
   “Okay...” ya fad’a yana giad’a kai. “Cry nomore kinji? Barin k’ara ba”
    Tana murmushi ta giad’a masa kai “I won’t ever. Thank you Anas lets go?”
  “Yes lets go.” Yayi assuring nata, da a dana ne hannunta cikin nasa zasu fice amman banda yanzu. Side-by-side kawai suke tafiyar. Bayan sunfito suka sami Afrah da Shettima zaune kan wata doguwar kujera sun baje se hira suke suna dariya kamar wanda suka jima da sanin junansu.

      “A ina suka saba?” Anas da Fannah suka tambayi juna a tare.
   “Nima bansani ba” suka sake amsar junansu a tare. Murmushi kad’an suka saki. “Shettima fa baida matsala ina shi ina Afrah?” ya tambaya cike da mamaki.
   “No let them be please karka mishi magana.” Cewar Fannah cikin salon da dazaran tama Anas magana dashi yake amincewa da k’udurinta.
  “Fannah amman kina ganin is okay?”
   “Yes don’t bother, lets go.” Bayan ta ajiye wa Amal birthday present nata taja hannun Aiman, ai atapir Amal tace se Aiman ta kwana mata, ita a dole tasamu sister. Da k’yar ta amince tabar Aiman ta tafi bayan ta kwashe mata kusan rabin birthday present nata tabata.
    “Toh Afrah seki tashi ai mutafi ko? Soyayyar ya isa.” cewar Fannah. Murmushin jin dad’i Shettima ya saki a yayinda kunya ya ratsa Afrah musamman ma dataga Ya Anas gefen Ya Fannah yana kallonsu.
 
    “A’a kuje ni zan kaita.” Cewar Shettima. Anas zeyi magana Fannah ta dakatar dashi “lets go ze kawo ta yace.” Badan Anas naso ba yabi Fannah suka fice.

kuyi min uzuri please da rashin posting da nakeyi kwana biyu, somethings came up

© miemiebee

TANA TARE DA NI...

TANA TARE DA NI... PAGE 54
BY MIEMIEBEE


Ba Afrah ce ta dawo gidah ba se bayan Maghrib, hankalin Mami duk yabi ya tashi dukda kuwa Fannah ta tabbatar mata cewar Afrah is safe with Shettima k’anin Anas.
   
      “Shettima thank you for today.” Cewar Afrah alokacin da take k’ok’arin bud’e murfin motan. “No let me babe” nan ya zagayo ya bud’e mata tare da ciro shopping bags guda biyu daya cika mata da kayaki. “Will call you as soon as na isa gidah, I love you My Afrah.” Tana murmushin jin dad’i tace, “I love you too My Shettima” ahaka suka rabu.

     Taku take a hankali gudun kar a jiyota aiko tana shiga suka had’u da Aiman kafin tace meh Aiman ta sa ihu “Mami ga Ya Afrah ta dawo.” A 360 Mami da Fannah suka fito. “Ke Afrah zo nan” cewar Mami kai a sunkuye ta k’ariso kafin Mami ta fara mata masifa ta kare kanta ta hanyar yin k’arya “Mami wallahi motarsace ta samu matsala seda muka kira me giara.”
    “Uhn uhn fa Afrah kiyi a hankali daga had’uwan ki da yaro seku zarce da soyayya?”
   “La ilahi! Mami abakin wa kikaji wannan zance?”
   “Ni na fad’a mata ai ba k’arya bane” cewar Aiman. “Mami wallahi har zama sukayi gu d’aya.”
     “Ai Aiman barta-”
    “Mami yi hak’uri ya isa zan mata magana” Fannah ta katse ta a hankali cikin dabara. “Afrah mushiga daga ciki.” Amsar d’ayar ledan hannun nata tayi sukayi d’akinsu. Bayan sun baje kan gado Fannah ta soma mata magana; “Afrah ni bawai hanaki zanba amman ki bi komi a hankali kinji? Na miji na miji ne.”
    “Ya Fannah wai nikan hassada akemin neh? Me aciki keda Ya Anas nida Shettima darling kin-” bata k’are maganar ba wayarta ya soma ruri tana kai dubanta taga Shettima ne datayi saving da ‘hot baby.’ Karap ta d’aga. “Hello baby” tace a nitse cikin wata salon da Fannah bata tab'a saninta dashi ba. Baki ta bud’e cike da mamaki tana kallonta haka har Afrah tagama wayar ta katse Fannah bata bar kallonta ba.

      “Har haka soyayyar taku tayi nisa?”
      “Hummn!” Taja numfashi, “Ya Fannah kenan, guguwar son Shettima ne ya kamani, wallahi ya had’un had’ewa duk abinda nake nema jikin d’a na miji yaja dashi. Daman ni dream d’ina na auri kyakkyawa sega Shettima nan Allah ya kawo min.”
   “Awww! Har tunanin auransa kike?” Cewar Fannah baki wangalau.
    “Humm! aini barni kurum har yaran da muka haifa ma na hango, barni in duba kayakin da ya sissiyo min ma tukun.”

    ★★★★★

       “Ya Anas in shigo?” Cewar Shettima dake tsaye bakin k’ofar Anas.
     “Shigo” ya basa amsa. A nitse ya bud’e k’ofar ba kamar yadda ya saba ba, ‘yar vest na Anas dake k’asa ya d’aga “Ya Anas in sa maka wannan cikin laundry basket?”
   Kallonsa Anas yake yau wata rana. “Eh sa” yabasa amsa. Bayan yasa yadawo ya zauna kusa dashi. “Ya Anas dan Allah alfarma nike nema.”
   “Name fah?” Cewar Anas yana duban laptop nasa.
    “Ya Anas bundle na d’ari biyar zaka bani please.” Ajiye laptop d’in yayi gefe guda cike da mamaki, “Shettima yaushe ne na baka na 200 da zakace in baka na 500 yanzu? Me kake da kud’in. Awww! Kaima kasan kayi girlfriend ko? LOL ba abinda zan baka, go and work for it, earn it!”

      “Ya Anas mana please, wallahi na mayar da hanakalina wajen karatu yanzu ka taimaka please.”
    “Amman Shettima kai kanada hankali mah kuwa? Ina zaka kai Afrah?”
    “Ni Ya Anas banche ka zageni ba, kud’i kawai zaka ban.”
   “Aww kawai ne? Sekayi kashinsa ai tunda kawai ne.”
    “A’a Ya Anas please yi hak’uri.”
   “Naji banasan surutu ina ganinka bud’e safe d’in d’au d’aya kabani waje.” Tsalle ya daka yana masa godiya sannan ya zaro d’aya daya lek’a yaga Anas bai kallonsa ya k’ara d’aya tare da b’oyewa cikin kayansa.
     “Uhm Ya Anas dama nace batun mota ta wallahi ta tsufa tasoma shan mai ko za’a d’an canza min.”
   Maganar da yayi kad’ai yasa Anas shak’ewa harda tari. Dududu shekarar motar nawa ne? Da k’yar inya kai d’aya shine Shettima ke wannan zance.
     “Ai da fili kafito kawai kace min kayi budurwa kaima kanasan ka fara hawa babban mota irin nawa.”
   “A’a wallahi Ya Anas ni ko E350 ka siya min walillahil hamdh Allah zan karb’a, kaji Ya Anas.”
  “Hehehe! su Shettima an girma har ansan ayi budurwa.”
   “Ya Anas mana...”
“Naji in naga kayi hankali zan canza maka motar, inko a’a zaka cigaba da zama da C 230 d’inka.”
    “Thank you so much Ya Anas, nagode, Allah bar mana kai ya k’ara dank’on soyayya tsakanin ka da Fannah.” Bejira jin meh Anas zece ba yafice. Murmushi ya saki jin an ambato sunan Fannah, shi yau through out ma besha coffeen ta ba, yayi missing inshi kuwa sosai, wayarsa ya lalimo ya danna mata kira bada dad’ewa ba ta d’aga “hello Anas.”
    “Fannah” yakira sunanta.
   “Na’am” ta amsa.
   “Yau bansha coffee ba.”
    “Yi hak’uri gobe zanzo in had’a maka.”
   “Har gobe?” ya tambayeta cikin wani irin salo cike da damuwa.
     “Toh Anas ai bareyi infito yanzu ba yayi dare, goben kaji?” Shiru yayi bece komai ba. “Kaji Anas?”
   “Naji” yace chan k’asa k’asa.
   “Yawwa goodnight” sannan ta katse. Ji yake kamar ya sake kiranta bai gajiya da jin muryarta amman kuma bayyasan ta raina sa ta d’au ko sonta yake. Bayan ya idar da isha yayi forcing kansa yayi bacci da k’yar danko yunwa yakeji kamar hauka.

     Washegari ya tashi as usual ya soma shirin office yashiga wanka kafin yafito yaga an share masa d’aki anyi mopping an gyara gado, toh waye ne? Yaushe Amal ta share nata d’akin bale ta share masa nasa, ganin baida amsar wannan tambaya kawai yayi shirinsa yana fitowa yaga shock of his life, Shettima har yagama tsara masa breakfast da alama sharan d’akin ma shi yayi.
   “Shettima?” Anas ya kira sunansa still not believing abinda idanunsa suke gane masa.
   “Na’am Ya Anas good morning bismillah ga breakfast nan na had’a maka.” A hankali ya tako ya zauna kan kujerar Shettima ya zuba masa chips da scarmbled egg daya masa, sannan ya had’a masa tea.
 
      “Tsaya aljanu ne suka shige ka komeh?” Anas ya tambaya.
   “Aljanu kuma Ya Anas? Dan na had’awa wa Yaya na guda breakfast se ace aljanu sun kamani?”
    “Toh d’akina fah? Kai ka share?”
   “Eh Ya Anas bismillah ci kar kayi latti.” A zuci Anas yace ahhh lalle Shettima nasan in canza masa mota LOL gaba ta kaini, nasamu new man servant. Koda yagama breakfast d’in Shettima ne yakai masa jaka mota.
   Tuk’i yake hankalinsa kwance Baana ya danna masa kira cike da jin dad’i ya d’aga.
    “Maza ne!!” Yace yana murmushin jin dad’i.
    “Blue eyes nashigo gari fah jiya.”
  “Ohh haba! Shine baka fad’amin ba?”
   “Wallahi tafiyan dare ne, zanzo office naka yau.”
   “Toh sekazo, Kashim fah?”
    “Wancan? Ai yana chan a Bama ya washi tafiya.”
    “Kace be canza ba kenan, anyhow ina jiranka.” Ding! Ya katse wayar. Kamar kullum aka bisa da gaisuwa har zuwa office nasa, bada dad’ewa ba Kacallah yashigo da complain, na barin gidan man engine da akayi a dalilin haka ya b’aci se an kira me gyara. Bayan da ya gama karantawa yace, “fire him, ka kori me aikin ai ganganci ne yasa sa mancewa be rufe gidan man ba, ka kuma yi replacing nasa with someone better, clear?”
  “Yyy... Yes Sir.”

   8:30AM yama Fannah a building, kamar jirarta Sule me kula da engine yake, yana ganinta ya nufo ta dan yaji intama Boss magana yana saurarenta. Bayan ya gaisheta yake bata labarin abinda ya faru, “wallahi Hajiya waya aka min mata ta tana labour kuma ba motan da ze kaita sesa duk na rikice na mance ban rufe gidan man ba, dan Allah kima Boss magana ya dawo min da aiki na, in na rasa aikin nan bansan dameh zan ciyar da matata da d’an mu data haifa ba.”
   Tausayin sule ne gabad’ai ya ratsa ta. “Don’t worry kaji? Zan masa magana in shaa Allah ze dawo maka da aikinka.”
   “Godiya nake Hajiya, Allah saka miki da alkhairi.”  “Ameen” tace sannan ta fice. Bayan tayi knocking yace, “enter” a nitse ta bud’e k’ofar ta shiga tun daga chan yake kallonta, wata skyblue silky doguwar riga ne a jikinta me dogon hannu, seda kuma red gyale d’an siriri data yafa ta nannad’e a wuyarta. Jaka da takalminta kuwa fari ne. Kallonta yake har yanzu, yafisan ganinta ba hijabi tafi kyau, bayan ta k’ariso gaban table nasa ta gaishesa ba takan gaisuwar yake ba ko amsawa beyi ba “kinyi kyau” yace mata. Tana murmushin jin dad’i tace, “thank you” tare da juyawa nan da nan ta had’a masa coffee, ko ina taje idanunsa na kanta, bayan ta had’a ta kawo masa ta ajiye a gabansa.

     Ba tare da b’ata lokaci ba ya soma sha tana tsaye a gefensa seda taga ya ajiye cup d’in tace, “Sir.” Kai ya girgiza mata “Anas.” Ya gyarata.
   “Okay Anas nace ba batun firing Sule da kayi ne dama.”
   “What about him?” Ya tambaya yana kallonta. “Yabar min gidan mai a bud’e yayi destroying engine d’in sena kira me gyara fa yanzu, he is not paying attention to his work.”
   “Ayyah Anas ba haka bane, matarsa ce tashiga labour shine aka kirasa hankalinsa ya matuk’ar tashi. Dalilin dayasa ya mance kenan.”
    “Wancan kuma damuwansa, he is fired and that stays that.”
    “Anas ka dawo masa da aikinsa please, kaji? For me please.” Shiru yayi be ce komai ba. “Please kaji?” Nanma shiru. Kukan da baya bata wahalan yi ta soma take hankalinsa ya tashi. “Toh kukan me kuma?”
    Cikin kukan tace, “ka dawo masa da aikinsa please.”
   “Fannah NO!” Wani sabon kukan ta k’irk’iro harda me sauti. “Fannah for goodness sake me haka kitayin kuka? In na dawo masa da aikin zaki bari?” Kai ta giad’a “okay, okay naji stop crying.”
    “Se ka kira Adam kace adawo dashi zan dena.” Take yakira Adam, “bring back Sule aikinsa.” Ya katse. “Shikenan zaki bar kukan?”
   “Eh” tace tare da share hawayenta. “Thank you Anas.” Wajen coffee machine ta nufa dan had’a masa cikin flask. Knock ne yazo daga bakin k’ofa “come in” Anas yace. K’ofar na bud’uwa sega Baana bayan ya k’ariso sukayi manshake se hirar su suke irin tasu ta maza nan da nan Fannah tagama d’ura masa coffeen cikin flask, ko d’aga kai taga wayene batai ba. “Sir nagama zan tafi” kafin ya amsata ta fice.
   “Woooww!” Baana yayi exclaiming.
   “Maza wannan me zubin india fah?”
    “Kai de halinka na son mata na nan har yanzu ko?”
   “Me za’a fasa? Gaskia tamin inaso.”
  “Kanaso?” Anas ya tambaya tare da d’age gira. Kai Baana ya giad’a masa yana assuring nasa. “Lallai kam tun wuri ma gomma ka hak’ura wannan tafi k’arfin ka.”
 
    “Ban tsammanin akoi macen da zata fi k’arfi na yanzu, sufa mata kud’i kawai suke bi wallahi yau da za’ace biri goggo yazama billonaire mata zasu bisa su auresa, so ya za’ayi ne in samu lambarta?”
    “You are wrong Baana, kaga wannan duniya da abinda ke cikinta be dameta ba, your money will never impress her, she is different from all other women, saboda haka ka fita daga harkanta.”
   “Kode kaima kana ciki ne?”
    “Ai itace matar da zan aura.”
   “Aure Anas!” Ya tambaya yana zaro ido. “Yaushe a gari?”
“Nide na fad’a maka kafita kabar harkan Fannah wallahi dan akanta se mu b’ata.”
   “Allahu Akbar! Maza kaine kuwa? What changed you haka?”
   “Fannah, she is the one who changed me.”

★★★★★

     *MOROCCO, 2:15PM*
  Cikin _Royal Mansour Marrakech Hotel._
   
    Kwance Anas yke bisa kaftareren California bed ya d’aga pillow tare da jingina ajiki, da isarsu Morocco shida Kacallah awa biyu kenan yanzu. Jiran sim card daya aiki Kacallah siyo masa yake, through out yau be sha coffeen Fannah ba, besata a ido ba, bekuma ji muryarta ba, seji yake kamar ya rasa wani sassa a jikinsa Kafin subar Nigeria yaso kiranta amman girman kai ya hanasa sekuma yanzu yake regreting. Bada d’adewa ba Kacallah ya kawo masa yana sa sim d’in ko gida be kira ba ya zuba number’n Fannah.

**
    Tana kishingid’e a kan gado ita d’ayanta tana buga game a wayarta ya soma ruri ganin international number yasa bata d’aga da wuri ba. A hankali ta sa a kunne “hello.”
   “Fannah” ya kira sunanta.
  “Na’am Anas, ina wuni?”
   “Lafiya” ya amsa blankly.
   “Uhm har kun isa ne?”
   “Eh you didn’t even mind calling me.”
   “I’m sorry, so yaushe zaka dawo?”
   “Are you missing me already?” Ya tambaya yana jin dad’i.
    “Yes I am missing you, I’m missing your your girman kai da masifa.”
   “Ai nabar yin masifa yanzu.”
   “Anya kuwa?” Ta tambaya tana murmushi.
     “Yes, nikuma I’m missing your coffee, your crying and face.” Dad’i sosai taji ya ratsa ta, wannan na d’aya daga cikin abubuwan da takeson Anas, he is very sincere komin ya gaskia take yana fad’i unlike ita, itama tayi missing kyakkyawar fuskarsa sabida rabuwansu da juna tin ran tuesday yau thursday amman ta b’oye masa.

   “To be sincere I miss your face you too.”
    “I know you would, dole zakiyi missing handsome face d’ina ga kuma unguwan ku ba kyawawa ko?”
     “Mr. Fauzi kaga irin halinkan ba, sesa banasan fad’a maka abu kacika feeling dayawa, I have to go Mami na kira na.” Karap ta katse tana murmushi, bawani Mamin dake kirarta bata san me zata ce masa bane kawai, duk lokacin da take waya dashi setanajin wani iri.

      Shigowar Afrah d’akin kenan ansha gayu kamar ba gobe, “Afrah ina zuwa haka?”
    “Wallahi hot baby na ne yazo, yana jira na ma yanzu haka. Madubi nazo kalla in fice” aiko tana ganin kanta ta fice. Tsaye tasame Shettima yayi crossing arms da legs jikin motarsa sanye yake da wata farar half jampa.
  “My queen kinyi kyau” yace da ita alokacin data gama k’arisowa kusa dashi.
  “You too my king.” Hira suka sha kamar ba gobe se kusan Maghrib yace ze tafi  bundle na d’ari biyar ya tsakulo a aljihunsa ya bata. Ido tazaro “hot baby duka wannan?”
   “Eh nakine sweetie, jiya mun samu profit sosai a business namu shine nima nace barin kawo miki rabon ki.”
   “Thank you hot baby” ta amsa. Bayan ta dawo ciki ta wula kan gado ta sami Fannah. “Ya Fannah you won’t believe this.” Bandir na d’ari biyar d’in ta ciro ta miqa mata.

   “Ke ina kika samo wannan?”
  “Hot baby na yabani.”
  “Shettiman? Aina yasamu? Yana aiki ne?”
    “Yana business mana.”
   “Business? Toh aini bansani ba. Ke Afrah bafa haka ake soyayya ba, ai kika cigaba da amsar kud’i dayawa haka gunsa seki talautar dashi.”
  “Toh ai bani yayi ba rok’a nayi ba. Wayyo! A gobe zanje in siyo Iphone nima.”

**

   Chan dare misalin k’arfe goma sha d’ayan dare a Morocco ko bacci Anas yakasa se juye-juye yake, ga gajiya amman yakasa baccin ba abinda yake inbanda tunanin Fannah. “Oh God! What is wrong with me? Why can’t I think of anyone se Fannah? Why?” Pillow ya d’au ya rufe fuskarsa dashi ko ze d’an rage tunaninta, ai se worse ma yake. Wayarsa ya d’ago daga kan bed side drawer ya kirata. Tana cikin baccinta tajiyo ringing na wayarta kamar wacce zatayi kuka ta d’aga ko duba wanda ke kira batai ba.
  “Fannah” ya kira sunanta. Jin muryarsa ta tashi ta zauna.
   “Mr. Fauzi what is it?” Ta tambaya cikin bacci.
  “What are you doing?”
   “Bacci mana” ta amsa sa a takaice rai ad’an b’ace.
    “Okay shikenan” ya fad’a kamar d’an yaron da aka mai rowan sweet ya katse wayar. Wayar ta ajiye ta koma bacci sede kuma daga yadda Anas ya mata maganar kamar bacci ya kasa, sekuma taji tausayinsa yaje chan besan kowa ba wayar nata taja ta kirasa yana gani yak’i d’agawa.
   “Toh ko har yayi bacci ne? Barin sake gwadawa inga.” A karo na biyu ne ya d’aga “Anas” ta kira sunansa a hankali, jin shiru tace. “Anas are you there?”

    “Yes” yace chan k’asa k’asa.
“Ka kasa bacci ne?”
   Nama “yes” yace. Shiru tayi tana nazarin me zata ce masa chan tace, “uhm if you need someone to talk to I’m here for you.”
    “Just go, jeki kwanta.”
   “Anas kaifa?”
   “I can’t sleep” yanason yace mata saboda yana missing nata ne ya kasa bacci amman kuma yak’i.
    “I can’t either.” Ta fad’a.
   “Why? Ba bacci kikeyi ba yanzu?”
  “Not anymore, you can’t sleep I’ll stay awake with you.” Dad’i yaji sosai.
   “Are you sure?”
   “Yes” ta fad’a tana giad’a kai.
   “Thank you.”
   “So yaushe zaka dawo?”
   “Maybe in 3-4 days time.”
  “Okay Allah kaimu.”
  “Ameen, so ya Afrah da Shettima?”
  “D’azu ma yazo wajenta, wai dama Shettima na business?”
   “Business kuma wani erin business kenan?” Anas ya tamabaya cike da rashin fahimta.
    “Nima I don’t know haka yace mata wai yana business harda kawo mata bundle na N500 dayazo.”
    “Are you serious?? Lallai ma Shettima, abinda zeyi da kud’in kenan dama. LOL”
   “Kamar ya Anas?”
     Nan ya labarta mata yadda Shettima yasamu kud’in. Dariya sosai dukansu suka b’arke da. Haka sukata hira kamar ba gobe sekace ba Mr. Fauzi ba, sun fi awa suna waya har bacci ya sace Fannah.
Jin shiru ya kira sunanta, shiru bata amsa ba “kinyi bacci ne?” Nanma shiru. “Goodnight” ya fad’a ahankali, k’in kashe wayar yayi yana d’an jin nishin Fannah da haka shima ya samu yayi bacci wayar mak’ale a kunnesa.

 
   *©miemiebee*

TANA TARE DA NI... PAGE 54
BY MIEMIEBEE



    Se Asuba da Fannah ta tashi Sallah ta tuna ashe waya take da Mr. Fauzi bacci yayi gaba da ita. Wayarta dake kwance a gefenta ta d’aga to her suprise taga Anas be kashe wayar ba. “OMG! Whattt!!!” Ta fad’a cike da mamaki, yanzu Mr. Fauzi be kashe wayar ba tun tun tuni? Har zata kashe seta tuna kuma what if be tashi yayi Sallah bafah? Daman ba ma’abocin Sallah akan lokaci bane. “Anas” takira sunansa ta wayar softly. Bacci sosai Anas yake wayar na ajiye kan pillownsa.
     “Anas!” Tasake kira da d’an k’arfi nan ma shiru. “Mr. Fauzi!!” Ta kira da ihu kwanciyansa ya gyara kodaya bud’e ido seya rasa daga ina ake kirar sunansa ko kad’an hankalinsa bekai kan wayar dake kan pillon sa bane.”

    “Mr. Fauzi wake up, wake up kaji? Fannah ce.” Se a yanzu yakai dubansa kan wayarsan yaga Fannah ke magana ba b’ata lokaci ya kai kunne cikin gigin bacci “Fannah” ya kira sunanta.
  “Huh!” Ta saki numfashi. “Good morning.”
   “Morning? Har safiya tayi neh?”
   “Yes Anas and bakayi Sallah ba.” Ze mata k’arya yace yayi sekuma ya fasa instead yace “lokaci beyi ba anan.”
    “Aww haba? Ta fad’i cike da gatsine “dad’in abin lokacin Morocco da Nigeria d’aya suke tafiya nan kuma lokaci yayi kaga chan ma haka kenan.” Kunya yaji sosai Fannah ta kamasa yana k’arya.
    “Toh aini bansani ba.”
   “But now you do tashi kayi Sallah toh.”
   “I’ll bari in 6 yayi I need to sleep a little more.”
   “Anas har 6? Ana sallah 5:10-5:20 kace kai sai 6? Ba kyau jingina Sallah fa. Yi hak’uri ka tashi kaga nima banyi ba semuyi tare kaji Anas?”
   “No se 6 I’m hanging up.”
    “No boyfriend karka katse please, katashi muyi Sallah kaji? Yi hak’uri kaga inka idar se ka koma bacci...” Da k’yar ta samu tayi convincing nasa ya yarda

   ****
   12:30PM su Anas suka k’are first meeting daya kawosu Morocco, da k’yar ya iya yayi breakfast da safe dan yadda yake missing coffeen Fannah. Zaune yake da laptop nasa a gabansa yana ‘yan aiki alokacin da wayarsa ya soma ruri. “Hello” yace bayan ya d’aga “dama nace meetings d’innan bara a iya rescheduling muyi duka a gobe ba? Nagaji da zaman nan, I wanna go back home.”
    Ta wayan akace, “but Sir you just arrived yestarday, nan da 3 days duk komai ze k’are, ka k’ara hak’uri please.”
   “NO!” Ya fad’a a tsawace “hak’uri na ya k’are ni nagaji ko kayi rescheduling a k’are komai a gobe kokuma kuyi meeting naku ba ANAS IBRAHIM FAUZI.”
  “Sir please calm down, naga bawai family kake dashi achan Nigeria ba why in such a haste?”
   “Yes banida family amman inada girlfriend and I’m missing her ni na fad’a maka do what is need to be done.” Karap ya katse wayar. Laptop d’in ya rufe a fusace tare da jingina jikin couch dayake zaune akai. Duk yadda yayi denying he can’t he is missing Fannah, baya missing Amal kamar yadda yake missing Fannah. Number’n ta ya kira.

     Alokacin Fannah na zaune dasu Baba a d’akinsa se hira sukeyi tana ganin number’nsa da tayi saving da Anas ta saci jiki ta nufa d’akinsu bayan ta baje kan gado tayi picking “hello Anas.” muryarta kawai ya jiyo se kawai yaji duk wani b’acin ransa ya gushe.
  “Fannah I’m missing you.” Yace tsakani da Allah ba kunya ba tsoro ba komai, he needs to tell her saboda the more yana keeping secret d’in wa kansa the more yake missing nata a kowani second.
    Gatsau tajiyo abinda ya fad’a matan, kamar ya he is missing her? Ai coffeen ta yake missing a kullum ba ita ba, ta b’angare guda kuwa wani irin feeling da bata tab’a feeling ba taji ya ratsa ta.
   “Fannah are you there?” ya tambaya jin tayi shiru. Nanne ta dawo daga duniyar tunanin data wula.
   “Uhm... Ermm. Yes Sir.”
    “Stop calling me Sir.”
   “I’m sorry Anas ban-” katse ta yayi.
   “Fannah I miss you, I want to come back, I miss everything about you.” Wai meke damun Mr. Fauzi ne? Ta tambayi kanta. Rasa na cewa tayi chan tace, “Anas calm down kaji? Nan da 3 days zaka k’are komai kaga seka dawo, dama zama mutum kad’ai ba dad’i hak’uri zakayi kaji?”
   “But I miss you.”
    “I miss you too Anas hak’uri zakayi kaji boyfriend?” Shiru yayi be amsa ba, “boyfriend?”
   “Yes” ya amsa chan k’asa-k’asa.
    “Kayi hak’uri kaji? What are you doung now?”
    “Nothing, jus sitting alone.”
  “Call up Amal nasan she will have alot to tell you, kaji?”
     “But I don’t want to, ni dake nakeson nayi magana.”
   “Toh nikuma ai bansan me zance maka ba.”
    “Tell me anything.”
   “Anything like?”
   “Your boyfriend.” Shi kansa besan lokacin daya fad’a hakan ba, kawai seyaji yanason yasan ko Fannah nada wani saurayin.
    “Ni banida boyfriend.”
  “Yusuf fah?”
    “Anas Yusuf ba boyfriend d’ina bane kawai good friend ne thats all.”
    “Okay who is your boyfrined yanzu?”
   “Banida boyfriend.” Ta mayar masa da amsar d’azu.
     “What of before?” Ahmad nata ne ya fad’o mata arai, masoyinta na hak’ik’a da aka rabasu na k’arfi da yaji, incident daya faru da ita a Bama na yadda wani azzalimi yayi raping nata ne kawai ya soma dawo mata batasan lokacin da ta fashe da kuka cikin wayar ba.

      A rikice yace, “Omg Fannah why are you crying? Saboda question dana miki neh? I take it back bar kukan kinji?” Hannu tasa ta share hawayenta cikin kuka tace, “no ba kai bane, I’m sorry.”
    “Ex boyfriend nakin ne?”
    Kamar tana gabansa ta girgiza kai. “Shine?” Ya sake tambaya hankali a tashe. “Ba shi bane.”
    “Do you want to talk about it?”
   “No it makes me cry.”
   “Shhh! Is okay bar kukan kinji? We will talk later.” Nan ya katse wayar duk hankalinsa yabi ya tashi, meh yasa Fannah kuka? Meh saurayin nata ya mata da dazaran anyi maganansa take kuka?

    Through out ranan Anas be kira Fannah ba aganinsa karya tak’ura mata, itako har ta saba d’an kwana biyu da suke yin waya, dabe sake kirarta ba setaji wani eri, ita kanta bata san wani erin feeling take ma Anas ba. Tana enjoying every single second da take spending da Anas hakan kuwa na nufin sonsa take kenan. Amman sede tana tsoro, tsoron ta fad’a tarkon son sa wataran gaskia ya bayyana ya guje ta, abinda barata iya jurewa ba kenan sesa take yayyafa wa zuciyarta ruwan sanyi da son Anas.

   ★★★★★
1 day later...  
    Kamar yadda Anas ya buk’ata a washegarin akayi rescheduling masa duka meetings d’in, a ranan yayi attending duka kansa kamar ze fashe gashi rabuwar sa da waya da Fannah tunda da ta fashe masa da kuka a waya shekaran jiya. Yana son kirarta amman bayasan tak’ura mata kuma he is damn missing her.
    Itama Fannah ta b’angarenta haka ne, so take ta kirasa amman kuma tana tsoro kar ya gwale ta yace mata waya rok’eta.

    10:20PM
   Kasa hak’ura tayi ta kira sa, dan hankalinta ya matuk’an tashi seji take kamar ba lafiya ba. Har call d’in ta tsinke Anas be d’aga ba, yana gani amman yak’i picking se a karo na biyu nan ma bece komai ba ita ta soma magana. “Anas.”
    “Yes Fannah.”
    “How are you?”
   Be amsa ba ya tambayeta “how are you too?”
    “Alhamdulillah, just called to check on you, se anjima.”
    “Wait Fannah, I miss you.”
     “I miss you too.” ta fad’a sincerely kamar yadda shima yayi. Hira kad’an suka tab’a sam be fad’a mata gobe ze dawo ba he wants to suprise her.
 
    Washegari da misalin k’arfe 2:00PM jirginsu Anas ya sauk’o a International Airport dake Abuja daga chan yashiga na Maiduguri direct. 2:30PM yamasa agarin Maidugiri, already Shettima da Amal suna jiransa. D’an tafiyan kwana uku yayi amman Amal seji take kamar shekara tayi bataga Ya Anas nata ba, haka kowa ma agidan. Abinci suka gama chi ya shiga d’akinsa dan watsa ruwa, tsatsaf ya sami ko ina har cikin wardrobe nasa yaga an gyara masa, murmushi kawai yayi danko yasan wa yayi hakan, Shettima ne. Bayan yafito yasa baqar ¾ wando da baqar plane T-shirt. Key’n motar sa ya d’auka ya fice.

     Fitowarsa parlour kenan, “Babana daga dawowa se fita kuma?” Cewar Ummie tana taya Amal tsifa.
   “Eh Ummie aiki just came up a office.”
   “Toh Allah kare.” Nan ya fice be zarce ko ina ba se gidansu Fannah. Almajiri ya tura ya mata sallama bada jimawa ba tafito sanye dawani light purple hijabi me hannu kodan ya jima be sata a ido bane seyaga ta k’ara masa kyau dukda ba makeup bane a fuskarta.

   He can’t explain how he missed her, rashin ganinta ya kasance wani babban rashi tattare dashi wanda bare iya bayaninsa ba.
Mamaki sosai tasha ganin Anas, har ma kamar bata yarda ba ko decieving nata idanunta suke ne? Ai ko ajiya da sukayi waya bece mata zezo ba.
      “Senayi magana kice ba kallon soyayya kike minba.” Magnarsa ne ya sake tabbatar mata da eh Anas ne a gabanta a hankali ta tako zuwa gabansa. “Anas! Yaushe kadawo?”
    “Some few hours back.”
  “Welcome back” murfin motar ya bud’e mata “get in I have something to show you” ba gardama tashiga bayan daya zaga ya shiga shima ya ciro wasu files ya mik’a mata bayan data amsa taga heading d’in *CONTRACT MARRIAGE AGREEMENT* rubuce da babban bak’i. A hankali tabi ta soma karanta rules d’in.
    Duka sun mata sede na had’a gadon ne battaso dukda kuwa yasa a k’asa ba abinda ze shiga tsakaninsu amman still tana tsoro, bata son Anas yasan ba virgin ce ita ba. Pen ya mik’a mata “sign them.” Ba gardama tabi su one by one tayi signing bayan da tagama ya amshe “very good I hope my rules are clear? Don’t fall for me, don’t get jealous in kinganni da wata mace.”

      “Ka kwantar da hankalinka nima dan banida wani option ne yazama min dole in yarda da wannan aure if not ba abinda ze had’a mu kwanciya gu d’aya da kai”
   “Allah sa” yace a lokacin da yake miyar da files d’in cikin envelope daya cirosu. “So auren will take place in a month time, you have 4 weeks to prepare.”
    “Wata d’aya?!” ta dafe k’irji tare da zaro ido in disbelief.
   “Yes wata d’aya Miss Aleeyu.”
   “But Sir wata d’aya yayi kusa ina laifi biyu ko uku?”
    “Huh! Look at you nid’in ance miki dan inaso ne? So nake ayi auren muyi mu rabu in huta dake in huta da Abuu. So don’t think othwrwise ki d’auka ko dan inason ganin ki ne always na matso da bikin.”

    Itade har yau barata iya fad’in ga halin Mr. Fauzi ba, in baya kusa da ita ya riga ce mata yayi missing nata ayau suka had’u kuma yasoma gasa mata bak’ar magana.
    “Anas to gidan da kake ginawan fa? Ai ba’a gama ba kaga ba yadda za’ayi ayi bikin nan in a month time.”
     “Nasani saisa zamu zauna a hotel for the meantime, nanda 2 months za’a gama ginin semu tare.” Ita har yanzu hankalinta be d’au wata d’ayan nan ba, haka kawai tasoma jin tsoro.
      “Anas ai bamu keda ikon sa wa bikin date ba, iyayenmu ne ko ba haka ba?”
    “I have money Miss Aleeyu inma a gobe nakeson ayi bikin za’ayi inada komai under control. Bana buk’atar ki saya wani abu, komai ni zanyi just ki sanar da Mami maybe gobe ko jibi Abuu zasu so kinji?” Kamar wacce barata motsa ba ta gyad’a kai.
    “Can I go now?”
   “Yes you can, nima nagaji da ganinki cikin motar.” Bata bar bak’ar kalamunsa suka tab’a taba ta fice. “Fannah I’m sorry for hurting you banasan kigane ko ina sonki ne saboda nima har yau bansan wani erin feeling nake miki ba, a farko nace tausayi ne sekuma naga bakida abinda za’a tausaya miki ayanzu amman kuma har a yau I care about you, I’m afraid I love you amman barin bar wannan love yayi ruining d’ina ba, I will do whatever it takes in kashe ‘yar soyayyar because I'm Anas Ibrahim Fauzi its not in me to fall in love.”

    **
     “Anas, Ummie tace kanason magana dani.” Cewar Abuu dake k’arisowa cikin parlour’n da daga Ummie se Anas ke zaune ciki.
     “Eh Abuu.” Bayan Abuu ya zauna Anas yayi gyaran murya, “Abuu batun matan aurer da kace in nema ne nakeson sanar dakai na samu, ina sonta kuma zan aureta.”
   “Alhamdulillah! Alhamdulillah! Sede wace yarinyan? ‘yar wace gida ce?”
  “Ba ‘yar kowa bace Abuu, Fannah PA ta ce, tanada diploma a Business Admin am very sure she’ll bring a great contribution to my Enterprise bayan ta zamo mata ta saboda ko a yanzu with her beside me nayi achievibg abubuwa da dama.” Kai Abuu ke gyad’awa nufin he is convinced, ya yarda.

    “Toh Masha Allah Anas a gaskia ina me matuk’ar farin ciki da Allah yabani d’a me hankali kamar ka, Allah saka maka da alkhairi Babana. Ita kuma Fannah ko?” Kai Anas ya giad’a Abuu yacigaba “zanso kamin kwatancen gidansu sabida inje inji kuma ingani ko d’iya ce me tarbiyya.”
   “Ba matsala Abuu first thing gobe zan kaika har gaban mahaifinta.”
   “Toh toh masha Allah sannu ko Babana?”
    “Yawwa Abuu one last thing please.”
“Mene ne Baban tell me.”
   “Abuu inda hali banasan bikin auren ya wuce nan da wata d’aya, inason Fannah Abuu I can’t wait har zuwa nanda wani dogon lokaci bata kasance mata taba, if possible nan da one month ayi komi ya k’are.”
    “Wannan ai ba matsala bace Babana kaida kake da kud’i a hannu. Addu’armu de kawai Allah sa muji sheda mekyau a gareta goben, yaso ko a jibi a muku aure in iyayenta suka amince.”
   “In shaa Allah ma zasu amince Abuu nide kawai kar ya wuce nan da wata d’aya.”
   “Allah kaimun toh.” Nan duk suka amsa da “Ameen” sannan Anas yayi d’akinsa. A hankali ya bud’e k’ofar kamar ko yasan Shettima na ciki.

     “Aww ashe kaine b’arawon. Oya miyar! Miyar nace!”
   Shettima dake zaro bundle na d’ari bibbiyu daga safe na Anas ya tsule besan lokacin da ya zubar da kud’in daya kwasan duka a k’asa ba.
     “Wayyo! Ya Anas ka tsoratani wallahi.”
   “Naji miyar b’arawo kawai. Ashe kaine, tun dawowa na naga kud’in safe d’innan ya ragu ashe kaine b’arawon ka gama min sata kaje ka samu Afrah kace mata kana business koh? Toh k’aryanka ya k’are yau.”

    “Ya Anas fa basata nake maka ba, arranging kud’ad’d’den nake.”
  “Ka rantse” Anas ya katse sa shiru Shettima yayi yakasa rantsuwar. “Oya ina ganinka one by one mayar min da kud’i na.”
   “Ya Anas mana dan Allah ko guda biyu ne kabani please wallahi na mata alk’warari kaji dan Allah.”
    “Seka karya, nide miyar min kud’ina dan tsiya duk wanda ka riga d’iba basu isheka ba? Mayar min ka fice kuma.” Kamar wanda zeyi kuka yasoma miyarwa ganin idan Anas bai kansa ya zira d’aya cikin aljihu ai kuwa Anas ya gansa ta gefen ido. “Miyar fa na riga na ganka b’arawo kawai, kai barakayi karatu ba se soyayya da sata ka iya.”

     “Ya Anas d’aya fa dan Allah” ya maraice fuska.
  “D’auka ka bani waje.”
   “Yeyy! Nagode sosai Allah bar mana kai.”

   Washehari da misalin k’arfe 11:00AM Anas yasa Abuu dawasu uncles nasa guda uku cikin mota se unguwar su Fannah kafin su shiga gidansu Fannah seda sukayi tambaya gidan mak’ota kusan biyar kan halayen Fannah sede kowa shaida me kyau yake bata yana yaba hankalinta kuma. Dad’i sosai Abuu yaji daga nan suka shiga gidansu Fannah banda Anas. Maganar awa d’aya da mintuna aka sukayi aka yanke hukuncin date na bikin Anas da Fannah a wata d’ayan da Anas ya buk’ata, Abuu ya d’au nauyin yin komai, ko tsinke be yarda Fannah ta kai gidan mijinta ba saboda yadda ya karanchi basuda arziki. Shopping da Anas ya musu Abuu yasa almajirai suka shigo dasu. Inbanda godiya ba abinda Baba da Mami keyi. Afrah kam bakin nan har kunne Fannah zatayi aure, zata auri Nigerian’s youngest billonaire tasan dole suhau gidan TV suma.

   Fannah de ta rasa me ke mata dad’i, wani tsoron Anas da bata tab’a ji ba ta soma ji yanzu. Taya zata auri Boss nata? Taya zasu kwanta gado d’aya da Anas su zau
Share:

1 comment:

pls drop down your comment......
dan Allah ku ajiye comment.

Tallata Kayanka

Guide Tricks Blog

Be With Me Technology

Popular Posts

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).