shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wanda aka fi sani da hausa novel wanda ni Muhammad abba gana nake rubutawa dan wayar tare da fadakarwa ga mutane a yanayin da muke ciki.

Wednesday 7 September 2016

TANA TARE DANI...41--45

tana-tare-dani.jpg


TANA TARE DA NI...

TANA TARE DA NI...PAGE 41
BY MIEMIEBEE

Haka har da aka tashi Anas be sake neman Fannah ba. So yake ya nisantar da kansa daga gareta as possible enough as he can, saboda ya soma ji kamar maganganun Shettima gaskia ne. Saboda when it comes to Fannah he is weak abubuwa dayawa take masa wanda yaci ace ya koreta koya hukunta ta amman seyaji bare iya mata komai ba. Yasoma yarda eh he is feeling something for Fannah amman ba love bane tausayi ne kawai, yana tausayawa mata sede ko daya tambayi kansa tausayin me take basa yakasa answering. Fannah is his weakness.

Fannah kuwa dad'i taji da be sake nemanta ba dan da wannan kayan kunyan da tama kanta na masa shisshigi harda karance diary'nsa bata san da wani idan zata sake kallonsa ba. Ita abinda yafi bata mamaki ma shine yadda Anas yabata hanky wai ta goge hawayenta bayan abinda ta masa, shin meke damunsa yau? Ta d'au atake zeyi firing nata kokuma ya mata wani abu makamancin haka amman seyayi sab'anin abinda take expecting. He is acting wierd yau, bata tab'a ganinsa haka ba shida yake fad'in kukanta bai damunsa segashi yau bayasan ji.

Hanky'n ta ninke tasa cikin jakarta sannan ta mik'e tare da rufo k'ofar ta dan ganin lokacin tashi yayi. Ta rufe k'ofar office nata ta juya kenan sega Anas shima yafito suna had'a ido tayi saurin kawar da kanta. Public elevator tabi a yayinda Anas ke binta da kallo so yake yace mata ta zo su shiga elevator'nsa amman kuma girman kansa bare bar sa ba, wai mesa ma yakesan su shiga elevator'n sa bayan abinda ta masa d'azu? Sanda ta b'ace sannan ya nufa nasa ya shiga shima, kafin ya sauk'o kuwa tuni Fannah ta k'ara mai. A d'an wani shago ta tsaya tare da yima family'nta d'an siyayyan kayan k'walama. Isarta gida keda wuya.

Mutane biyun data gani tsaye cikin gidansu ne suka mugun razana ta. Ido wuru wuru ta zaro tare da dafe k'irjinta tana me salati a zuci. "Baffah Khaleel?! Ya Farouq?!" Kai tasoma kad'awa danko bata yarda da abinda idanunta suke gane mata ba. Mami dasu Afrah dake tsaye gefe guda suma fuskarsu d'auke yake da damuwa.
"Mami dan Allah kice min basu bane, tell me idanu na wasa suke min."

"Fannah manyan gari wato har gidan TV ake nuna ki, 'yan matan nawa fa duk sun girma sosai tunba Fannah surikata ba." Cewar Ya Khaleel yana wani murmushin mugunta.
"Kai Farouq baka ga matarka bane da baraka mata magana ba? Jeku gaisa mana." Wani tantirin dariya ne a fuskar Farouq a yayinda ya soma takowa gaban Fannah. Baya tayi take ganin haka "Fannah mata ta ya haka kuma? Mijinki ne fa ni, bekamata kina min haka ba, matso mana mu gaisa." Sosai Farouq ya sake girma yazama cikakken na miji yanzu kyansa ya sake fitowa, sede iskancin nan nasa daya saba har yanzu yana yi be bari ba.

"No don't touch me." Kamar kyaftawan ido Mami tashigo tsakaninsu, "Ya Khaleel meh amfanin haka dan Allah? Nasan kai da d'anka kunfi k'arfin mu dan Allah kuyi hak'uri ku koma inda kuka fito. Fannah bata san Farouq Ya Khaleel kayi wa Allah ka hak'ura da kai da d'anka dan Allah."
"Maman Aiman kenan, in kinga mun koma Bama toh wallahi da Fannah ne. Wace karuwar 'yarkun ma wacce ko martaba battada, dan ni da Farouq zamu rufa mata asiri zaku wani tsaya kuna mana tsiya yau shekarunta nawa takasa yin aure, ba d'a na mijin da ze amince ya auri Fannah inba Farouq ba."

"Baffah Khaleel dan Allah kayi hak'uri ka rufa min asiri banasan sake komawa Bama, banasan Ya Farouq ni na rungumi k'addara zan gama rayuwata duka ba aure dan Allah kar ka aura min Ya Farouq." Fannah ta fad'i hawaye na gangarowa kan kumatun ta abin tausayi. Tajima bataji tashin hankali kamar na yau ba. Ta riga da ta ajiye past nata a gefe mesa su Baffah Khaleel zasu dawo su hargitsa mata komai??

"In baki son shi to shi yana sanki sakariya kawai, aure tsakaninki dashi kuma farillah ne nan da 'yan watanni, gomma tun wuri ku fara shiri, karatu ne Farouq yayi. Yanada diploma'nsa dakuma aiki me albashin da ze iya rik'eki. Kinga ko wannan karan ke zakiyi kayan d'akinki tunda kema kinada aiki. Abinda ya kawo mu dama kenan, bayan biki zaki bi mijinki Bama ku fara zama acan, in qaninan ya tashi ku gaishesa. Farouq mu tafi."

"A'a Baba ni ba yanzu ba semun gaisa da matar tawa tukuna."
"Karka damu akoi gobe ai, gobe zaka dawo har girki seta maka tunda matar kace, mu tafi." Nan suka fice. Kuka me k'arfi Fannah ta rushe da. Mami na bata hak'uri haka Afrah da Aiman ma. "Mami ni shikenan Ya Farouq zan aura? Duk inda mukaje se sun tsakuro mu. Mami dan Allah do something wallahi banasan Ya Farouq mugu ne, azzalimi banasan sa Mami." Ta k'ara shigewa jikin Mami tana kuka me tsuma zuciya.
"Yi shiru Habibti in shaa Allah baraki auri Farouq ba kamar yadda Allah ya k'wato ki kwanakin baya haka ma ze miki yanzu mu dage da addu'a kawai."

"Ya Fannah kiyi hak'uri zamu tayaki da addu'a" cewar Afrah cike da tausayi. Kuka sosai Fannah takeyi haka yadda taga rana taga dare ta kasa bacci. A ranan kowa hankalinsa tashe yake basu san kuma ina zasu sake zuwa ba, basu san ko in sun bar Maiduguri akoi inda zasuje Fannah tasamu aiki me kyau kamar na nan ba. Baba ya tausaya wa 'yarsa sosai ba kuma abinda yafi bak'anta masa rai kamar in ya tuna ba abinda ze iyayi ya cheto 'yarsa daga halaka. Dan auren Farouq halaka ne yaron da besan darajar mace ba ko kad'an, d'an giya d'an iska.
Daga Fannah ta rufe ido seta soma mafarke mafarke ganin ba mahilicci se Allah ta tashi tayi alwala tariga nafilfilu har seda k'arfinta ya k'are sannan tayi zaman istighfaar. Da safe ta tashi tana shirin office sanyi sanyi kamar wacce k'wai ya fashe ma aciki duk Afrah na kallonta takasa koda ce mata uffan dan tausayi. Mami ce tashigo ta tarar da ita tana sa kaya bayan gaisuwa Mami ta tambayeta cike da tausayi "Fannah ba se kinje office ba yau ki huta"

"Mami gomma inje saboda zama anan ba abinda ze haifar min inbanda bak'in ciki jiya Baffah Khaleel yace Ya Farouq ze dawo yau, bana san ganinsa Mami na gwammaci naje office."
"Toh shikenan Fannah Allah kare kicire damuwa daga ranki kinji? Muna nan muna kan miki addu'a."
"Nogode Mami ni na tafi." "Allah kare" both Mami da Afrah suka mata sannan ta fice.

8:01AM daidai ya mata a office na Mr. Fauzi kanta sauk'e a k'asa ta gaishesa, sama sama ya amsa. Jakarta ta bud'o tare da ciro hand kerchief daya bata jiya ta ajiye kan table nasa. "Gashi, nagode." D'gawa yayi ya sake mik'a mata "na baki keep it."
"But Sir-" katse ta yayi "I said keep it" yace a hankali. Amsa tayi tare da masa godiya ta mayar cikin jakar ta.
Har yanzu basu had'a ido ba dan kanta a sunkuye yake.

"Ina schedule d'ina na yau?" Ya tambayeta yana danne danne a laptop nasa.
"I'm sorry bansamu na had'a ba excuse me yanzu zanje in had'a maka."
"Mesa? Me kikeyi tun jiya da baki had'a ba?" Ya tambayeta cike da tsiwa.
"I'm sorry" tace nan ma bata d'aga kai ba sede daga yadda take maganar Anas ya gano wani abu na daminta ya tambayeta meneh kuma girman kansa bare barsa ba. Kallonta ya tsaya yi kusan na minti biyu amman sam bata gwada yunk'urin d'ago kai ba bale ya kalli cikin idanunta ma. "Miss Aleeyu" ya kira sunanta a hankali.
"Yes Sir" ta amsa ba tare da ta d'ago kai ba. "Make me coffee" ya fad'i. A sanyaye ta juya ta nufa wajen machine d'in sede hankalinta ko kad'an baya jikinta tayi nisa tunanin abubuwan da suka faru jiya she actually can't believe Baffah Khaleel da d'ansa Ya Farouq sun dawo suna san maida ita Bama da bata sake tsammani zata koma wataran ba.

Bayan ta gama had'a jagual-gualenta ta juyo dan ba coffee ba sunan abinda ta had'a. D'an k'usa ne ya kama mata hijabi agarin cirewa tayi b'arin coffeen duka ya zube a k'asa cup d'in kuma ya fashe. Kid'imewa tayi a lokaci guda batasan lokacin da ta tsuguna ba dan tattarawa. "Don't Miss Aleeyu karki ki tab'a" Anas yayi warning nata da ihu chak ta maida hannunta. "I'm sorry" ta fad'i hawaye na cikowa a idanta. "I'm sorry please" ta sake basa hak'uri.
Toh kuma kukan meh? Ai be tab'a taba, bekuma mata masifa ba kodan d'an ihun dayayi dan kar ta tab'a glass d'inne ya sata kuka? Tasowa yayi daga mazauninsa ya nufo gabanta har yanzu tana tsugune "get up" yace mata. A hankali ta mik'e kanta sunkuye se hawaye takeyi side bag nata ya mik'a hannu yaja a hankali, batace masa komai ba, bud'ewa yayi ya ciro handkerchief daya batan "wipe off your tears" amsa tayi ta na gogewa sede the more tana gogewa the more kukan yake k'aruwa harda me sauti da k'yar ya zaunar da ita.

Besan me ba se kawai yaji ya damu da ita bayasan ganin ta tana kuka. "Miss Aleeyu mesa kike kuka na miki wani abu neh?" ya tambayeta a hankali. Kai ta kad'a masa da nufin a'a tana me cigaba da kukan.
"Toh mesa kike kuka? Sabida glass cup da kika fasa min ne? Don't worry I have lots more."
Kukan take har yanzu ba makawa hasali se k'ara volume na kukan nata ma take. "Miss Aleeyu what is it?" Kai kawai take kad'a masa chan ma ta tashi ta ruga office nata a aguje kan table nata ta baje sekuka take shark'af shark'af abin tausayi. Anas nason bin bayanta amman girman kai irin nasa bare barsa ba. "For goodness sake what is wrong with me? Mesa nake damuwa da Fannah? She is not my responsibilily so let her be, duk abinda ke damun ta ita taji wajen." Mik'ewa yayi tare da zama kan kujerar sa yana me cigaba da abinda yakeyi. Sede inaa mind nasa gabad'aya yana wajen Fannah. What if har yanzu kuka take? Me aka mata ko daga gida ne aka b'ata mata rai? Wayarsa ya d'ago dan kiran Mami se in ya soma shiga se ya katse haka ya kasa kirarta dan tambayen meke damun Fannah. Meeting dayake dashi ma yau shi kad'an sa yaje saboda yasan there will be no point yaje da Fannah tunda haka ta taho yau tana kuka. Shi kad'ansa yaje though shima duk hankalin sa na kan Fannah bayan da meeting d'in ya k'are as usual driver ya wuce dashi hotel dan cin abinci.

Ga abincinsa a gabansa amman yakasa chi, dududu sau nawa suka chi abinci da Fannah amman yaji yau inba ita bare iya chi ba kuma bawai fa baya jin yunwa bane kawai seda ita ze iya chin abincin. Kacallah ya kira kan ya sanar da Fannah driver ze zo d'aukanta yanzu dan bayasan ya kirata da kansa ta raina sa, hakan kuwa akayi bayan 20minutes aka kawo Fannah hotel d'in tana shiga tagansa zaune dan bata masan nan za'a kawo ta ba ce mata kawai akayi Boss na nemanta. Idanunta sun kumbura sunyi ja dan kukan datasha a hankali ta k'arisa gaban table nasa ta tsaya ba tare da tace uffan ba.
"Sit" yace mata hakan ko tayi bada jimawa yasa aka kawo mata abinci sak irin na jiya. Nan ma "eat" yace mata.
"I'm not hungry" ta masa k'arya dan kuwa ko breakfast batayi ba yunwa takeji amman batada appetite na cin abincin saboda damuwar dake kanta kad'ai ya isheta. Spoon biyar yakai yaga ko yunk'urin tab'a abincin ta batayi ba.
"Miss Aleeyu bakiya so ne akawo miki wani daban?"
Kai ta kad'a masa. "Then why are you not eating?"
"Sir I'm sorry bana jin yun-" bata k'are maganar ba cikinta yayi wani irin kuka.
"Yes kinajin yunwa eat." Nanma kai ta kad'a masa. "Kichi kokuma in baki 500 papers kiyi correcting nasu" ya gwada taorata ko dan haka zata chi. "Okay I'll do it in muka isa office d'in." Mamaki sosai amsarta ya basa itan da kullum take had'asa da Allah in ya bata aikin yau ita ke fad'in zatayi kai tsaye? Toh meke damun ta?

"Miss Aleeyu meke faruwa? Meke damunki? Tell me." Ya tambayeta cikin sanyin murya dan duk yashiga cikin damuwa ganin Fannah a damuwa."
"Babu Sir thanks for your concern, zan jiraka a waje in ka gama se mutafi in fara correcting papers d'in da wuri saboda in gama on time."
"Barakiyi correcting komi ba, I don't mean it kawai kichi abincinki kinji? You are sick har yanzu zama da yunwa won't help, eat." A hankali ta d'aga spoon nata ta soma ci sede ba hab-hab kamar yadda ta saba ba. Anas ko da jimawa yagama cin nasa yayi zaman jiranta saba'anin yadda ya saba. Dududu quarter kawai taci tace ta k'oshi. "Are you sure?" Ya tambayeta kai ta gaid'a masa. Bayan ya biya kud'in suka fice.

Shigarsu mota Anas yace da driver "ba office zamu wuce ba gidansu Miss Aleeyu zaka kaimu." Cike da mamaki ta d'ago kai se yanzu suka had'a ido dashi tun had'uwansu yau. "Gidan mu kuma Sir? Mesa?"
"Saboda inji meke damunki." Yabata takaicaccen amsa.
"No Sir please don't ba abinda ke damuna kawai fad'a mukayi da Afrah" tanasa k'arya
"Ban yarda ba" ya bata amsa yana duban agogon sa.
"Sir I'm serious." Ita tsoronta kar in sunje su had'u da Baffah Khaleel kamar yadda ya saba kiranta da karuwa ko karya ya kirata gaban Anas. "Sir please mu juya na bar wayana a office I need to get it." ta masa k'arya ko ze canza mind nasa.
Resting kansa yayi jikin kujerar "karki damu zansa Ahmad ya kawo miki."
"Sir-" hannu ya aza kan lips nasa "shhh! Banasan surutu dayawa." Ahaka har suka iso gaban gidansu Fannah zuciyarta se bugun d'ari d'ari yake. Driver na parking Fannah ta fito da sauri dan duba ko su Baffah Khaleel suna gida takai da shiga k'ofar gidansu kenan kawai suka ci karo da Ya Farouq kafin tayi wani k'wak'waran motsi ya cafko ta da hannu daidai lokacin Anas yake fitowa daga motan shima, idanunsa basu tsaya ko ina ba se kan hannun Farouq rik'e dana Fannah se k'ok'arin k'wata take amman ta kasa. Wani erin mahaukacin kishi yaji ya bugesa inba wai kashe koma waye mutumin yayi ba yana ganin bare samu sukuni ba.

A fusace ya k'ariso wajen. "Matata me haka dan na kama miki hannu? Ke wai bakiyi missing d'ina bane? Ko d'an shafaki bara ki bari inyi ba?" Cewar Farouq dawani shu'umin murmushi fal a fuskarsa.
"Ya Farouq ka sake min hannu niba matar ka bace let me go" ta fad'i tana hawaye tare da k'ok'arin k'wace hannunta.
"Ka sake mata hannu!" Anas ya fad'a cike da isa. Fannah da Farouq tare suka juya suna kallon Anas. "Waye kuma wannan baturen?" Farouq ya tambaya.
"Mr. Fauzi please ka tafi, don't involve yourself in here."
"Kinsan sa kenan" Farouq ya sake tambaya. "Bade shima saurayin ki bane kina kwana dashi, kinsan sana'a sa'a." Anas be san lokacin daya kai wa Farouq naushi a fuska ba da zobobin azurfa a hannunsa. Take hancin Farouq ya fashe gefen bakinsa yasoma na d'igan jini.


© miemiebee

TANA TARE DA NI...

TANA TARE DA NI... PAGE 42
BY MIEMIEBEE

          Baki Fannah ta bud’e tare da aza hannunta bibbiyu kai cike da mamaki da tsoro duka. Hannu Farouq yasa tare da tab’a inda yaji moisture a fuskarsa yana dubawa yaga jini ta hanci da bakin sa, “Kai! Ni ka fasawa baki? Dama nasha jin cewa ku turawa bakuda tarbiyya yau zan koya maka.” Hannu ya d’aga da k’arfin da Allah ya bashi shima ze kai wa Mr. Fauzi punch ai karap Anas ya kama hannun nasa tare da murd’awa cike mugunta ta bayansa. K’ara sosai Farouq ya saki dan azaba.

    Fannah duk ta rikice “Mr. Fauzi please ka sake sa ya isa please” ko saurarenta Anas beyi ba k’ara murd’a hannun nasa yayi a bayansa k’ara sosai Farouq ya sake saki dan azaba. “Repeat what you just said.” Anas yace dashi, daga yadda yake magana ma kad’ai za’a san ransa a b’ace yake, na bala’i ma kuwa. Duk zafin da Farouq ya keji be hanasa misbehaving ba. “K’arya nayi dan nace kuna kwana tare karuwarka ce”
     “You really want to die” Anas ya sake shi, kafin Farouq ya sake wani k’wararren motsi Anas ya sake kai masa punch a fuska fiye da yadda yayi d’azu sosai jini yake fita daga baki dakuma hancin Farouq.

     “Mr. Fauzi please ya isa dan Allah” Fannah ta fad’i duk a kid’ime idanta tuni suka cike da hawaye.
    “Kai ko kasan waye ni? Mijinta ne fa ni, aurenta zanyi banza da kai zakazo kana intruding. In ita karuwan kan bata fad’a maka yanzu ai kaji I’m her husband. Ke Fannah dan iskanci ya miki yawa kin kusa aure ma baraki fad’awa ‘yan iskan samarukan kin su hak’ura bako?” Hannu ya mik’a ze jata dan wanke ta da mari. Kamar a kyaftawan ido Anas yajata bayansa kamar ‘yar baby tare da rik’e hannun Farouq, rik’o kawai ya masa amman idan Farouq sanda ya cike da hawaye. D’ayan hannunsa ya d’aga ze sake kaiwa Farouq mumunar punch Fannah ta rik’e hannunsa da nata bibbiyu. Hawaye take sosai “Mr. Fauzi please ya isa kayi hak’uri ya isa please.”

     Hawayen da takeyi ne kawai ya hana Anas kaiwa Farouq punch da ze iya kwantar dashi a asibiti. Kwalan rigar Farouq ya chukumo. “In bakada manners na magana wa kamilallaiyar mace I will teach you some, the next time ka sake kwatanta Fannah da wad’annan munanan suna I assure you zakayi kwanan cell, pathetic fool kawai, idiotic bastard.” Sannan yayi wulli dashi har k’asa Farouq yayi landing, daidai lokacin Ya Khaleel ya yanko kwanan gidansu Fannah shi a dole yazo cin abincin ranan da surikarsa ta dafa masa kamar yadda yace jiya.

     Ai ganin his only son a k’asa ga kuma jini ko ta ina fuskarsa ya falfala da gudu yayi kan Farouq. “Farouq meya same ka? Wani d’an shegiyan ya maka wannan tsiyan, waye shi?”
       “Baba kafin ka kira wani da d’an shegiya make sure ka cire sunan d’anka daga number a list d’in. Nayi warning nasa but I think I have to warn you too, the next time ya sake shiga harkan Fannah bare kwana a garin Maiduguri qalau ba.”
 
     “Tohh sannu fa, sannu shugaban k’asan Nigeria. Toh kaine d’an shegiyan ba d’ana ba, kai har kanada da right da zaka hana Farouq shiga harkan Fannah ne? Ka tab’a jin inda aka shiga tsakanin mace da miji?”
   Fannah dake tsaye bayan Anas tace, “Baffah Khaleel Ya Farouq ba miji na bane.”
    “Ke karuwa rufa min baki.”
   Ran Anas in yayi dubu be b’aci ba, taku yayi yunk’urin yi zuwa gaban Ya Khaleel dan kai masa had’add’en punch shima, “how dare you call Fannah karuwa!” yace a yayinda Fannah ta rik’e rigansa dan hanasa aiwatar da abinda yayi niyyar yi. “Mr. Fauzi let them be please, ya isa ka tafi wannan problem d’ina na ne bansan na jaka ciki, please go.” Wayarsa ya ciro a fusace bayan an d’aga yace, “Hello send me 10 men, I mean 10 a unguwar Polo...” Nan ya masa kwatance. Baki na b’ari police d’in yace, “yy.yyyes Sir right away!”

    Aiko cikakken minti biyar da gama wayan Anas beyi ba sega motan polisawa guda biyu. Farouq harda rud’ewan ciki Ya Khaleel kuwa sanda ya saki fitsari a wando shi be d’au dagaske baturen yake ze kira polisawa ba, toh waye shi.
     “Take them both, kuje ku rufesu right away” ya fad’a a fusace.
    Farouq da baki ke jini yace, “wallahi kayi k’arya me mukayi da zakace aje a rufe mu?” Can k’asa k’asa Ya Khaleel yace, “kai kayi shiru se yanzu nagane waye wannan mutumin, ba bature bane shine wanda aka nunasa da Fannah ranan a BRTV wallahi babban mutum ne mu basa hak’uri in bahaka ba in aka rufemu me bailing namu se Allah.”

     “Mr. Fauzi ko? Dan Allah kayi hak’uri, wallahi misunderstanding aka samu anan my apologies please karka sa a rufe mu dan Allah. Farouq baraka basa hak’uri bane?”
     “Officer take them away banasan jin komai.”
    Nanne bakin Fannah ya bud’u. “Mr Fauzi please kayi hak’uri karka rufesu dukda cewar basuda kirki ‘yan uwana na ne, Ya Khaleel Baffah na ne Ya Farouq kuma cousin d’ina kayi hak’uri and set them free please.”
    “Miss Aleeyu why? Bakiji munanan sunan da suke kiranki dashi bane?”
    “Naji Sir just please set them free, please.” Ta fad’a idanta na cikowa da hawaye.
    “Officer let them be zaku iya tafiya sorry for the disturbance.”
   “Ba komai Mr. Fauzi muna da godiya”
  “Zuwa anjima zakuji alert thanks.”
    “Mungode sir, mungode sir” a haka suka ja motocinsu suka fice.

    “Miss Aleeyu kinasan in samusu retricting order from the law yadda barasu sake zuwa kusa dake ba? So they won’t disturb you in na bar nan?”
     “Sir thank you but karka damu in shaa Allah ba abinda zasu iya min you can go kadena b’ata lokacinka akaina please, thank you”
    “Call me in wad’annan foolish mutanen suka sake miki wani abu” ya k’are maganan yana ma Ya Khaleel da Farouq kallon banzaye cikin banzaye. Farouq zeyi magana Ya Khaleel ya taka masa k’afa dan haka yayi shiru.
    “Ki shiga ciki.”,Ba musu bale gardama ta shige ciki sanda ya tabbata ta shiga ya dawo da kallonsa kan like father like son yana nuna su da yatsa “kun ji na rantse in kukayi ma Fannah wani abu zaku k’are rayuwanku a jail, assholes.” Yana kaiwa nan yashige motarsa driver ya rufe yajasa suka fice.

      Se yanzu bakin Farouq ya bud’u. “Shege se meh? Wallahi kasani ka tab’o tsuliyar dodo, zancen kakeso.”
    “Kai Farouq ya isa saurayin nan babban mutum ne a garin nan ka rufa mana asiri muyi abinda ya kawo mu mukoma da Fannah Bama cikin kwanciyan hankali.” cewar Ya Khaleel.
    “Wallahi Baba be isa ba ya zubar min da jini ya kwana lafiya Allah kaimu gobe. A ina yake aiki kace?”
    “Wai meka isa kayi masa ne dawani fashasshen bakin ka da hancin ka, se uban kurin baki wai kana zuwa gym ji yadda kabari wancan Fauziya ne ko Fauzi ya maka tatas. Kona fad’a maka inda yake aiki me ka isa ka masa?†
   “Niko nasan me zan masa just tell me ina yake aiki?”
    “A Flames Enterprises shine CEO’n wajen naga sun sa a TV”  
   “Good” Farouq yace tare da ficewa. Babansa na kiransa ko a kwalan rigarsa, Ya Khaleel kuwa shegen tsoro ne dashi sekace farar kura. So yake ya shiga cikin gidansu Fannah amman kuma yana tsoron abinda Mr. Fauzi  ya fad’a masa. Dan haka ya nufa masauk’insu kawai.

    Anas kuwa isar sa gida ya wuce d’akinsa tare da sa lock ba tare da yace da kowa komi ba. Wani irin tausayin Fannah yaji ya kama sa, ba abinda yakeso yanzu kamar yayi protecting Fannah daga wannan shegun Baffan nata da d’ansa. Mesa zasu na kiranta da karuwa? Mesa zasu na kiran yarinya me tarbiyya kamar Fannah da karuwa? To kode ta tab’a yin hakan ne da a baya se Allah yamata shiriya? “No!” ya fad’a a fili no matter what Fannah batayi kalan wanda zata iya aikata abinda uncle nata yake fad’a ba. Ai inhar dagaske karuwan ce da bare so ya aura wa d’ansa ba k’azafi kawai suke mata, ayyah ashe shiyasa taketa kuka a office yau, shiyasa ko abinci ta kasa ci. “I will protect you Fannah no matter what.” Ya fad’a a fili.

   *****

9:23PM
     Fannah da family’nta ne zaune d’akin Baba yanzu tagama basu labarin abinda ya faru d’azu, abinda Mr. Fauzi yama su Ya Khaleel. Kowa wajen yasha mamaki matuk’a.
   “Alhamdulillah! Alhamdulillah! Allah sak’a wa Anas da alhkairi, abinda yama Ya Khaleel daidai ne Allah saka masa da alkhai”  “Ameen” kowa ya amsa wajen.
     “Habibiti amman har duka Anas yama Farouq?” Mami ta tambaya cike da mamaki.
   “Eh Mami, Mami tsoro nakeji wallahi Ya Farouq ze iya cewa ze rama dukan akaina.” Rungumota Mami tayi gam ajikinta tana shafa jelar gashinta da d’ankwalinta be samu ya rufe ba. “In shaa Allah ba abinda ze miki kina da Allah bayan haka kuma ga Anas na tabbata bare bari wannan shegen Farouq d’in ya miki wani abu ba.”

    ***

    10:30PM
“Wai ina wannan hegen yaron yajene?” Cewar Ya Khaleel da kansa for the 100th time yana duban k’ofar one room apartment da suka d’an kama da d’ansa. Chan ya hango shadow’n mutum, torchin hannun sa ya haska, ganin Farouq ke tahowa ya saki hamdala tare da nufan wajensa. “Kai Farouq ina kashiga tun d’azu? Kasan na rasa mahaifiyarka barin iya juran rasaka ba kaima. Kuma dan rashin hankali haka kata yawo a gari da fashasshen baki da hanci?” K’eyarsa ya tand’e “wuce ciki mu goge maka.”

5 minutes later...
 
    Farouq ne mik’e kan ‘yar katifarsu a yayinda Ya Khaleel ke treating masa ciwon da Anas yaji masa a fuska da dettol. “Ina kaje ina tambayarka tun d’azu kamin shiru.”
    “Kai de Baba Allah kaimu gobe se Mr. Fauzi ne ko Fauziyan nan ya raina wa kansa nan gaba ko kafad’an juna muka buga bare min koda kallon banza ba.”
   “Wai me kake nufi Farouq? Kaga fa ka rufa mana asiri ni na fad’a maka kokuma in anzo tafiya damu in ce mai kai kad’ai ne banda ni, am warning you.” Lebb’an sa yacize irin mazan nan mana aikuwa yacize wajen ciwon.

★★★
Washegari...
 
      K’arfe 8:10AM ya ma Fannah a office na Mr. Fauzi tun 8:00AM yake jiranta a zatonsa ma ko barata samu zuwa ba se kawai ya ganta, har cikin ransa yaji sanyi sede yau ma fuskarta ba walwala kamar jiya. As usual ta k’ariso gaban table nasa ta gaishe sa kanta a sunkuye. “Good morning Mr. Fauzi.”
     “How are you feeling?” ya tanbayeta a hankali.
   “Alhamdulillah, thank you for yestarday.”
   “Ba komai” yace mata.
    “Sir bansamu nayi making schedule naka jiya ba am sorry.”
  “Is okay” yace mata ba tare da ya nuna damuwa ba. “Mesa baki fad’a min ba?” Ya tambayeta. A hankali ta d’ago kanta idanunsu na had’uwa ta sake sunkuyar da kanta, “I’m sorry” tace sincerely.
    “Baki amsa min tambaya na ba, mesa baki fad’a min abinda wad’ancan biyun suke miki ba. Saisa kikazo jiya kika ta kuka kenan koh? Akansu ne?” Kai ta giad’a a hankali.
   “Mesa baki sanar dani ba?”
  “Sir I thought there will be no point in fad’a maka sesa kawai nayi shiru.”
    “Next time call me up and tell me kinji?” Kai ta giad’a tare da godiya.
   “Sun sake miki wani abu?”
   “A’a.”
     “Dagaske ne zaki auri wancan Farouq d’in?” Ya tambayeta kamar me jin kishin ta. Kai ta giad’a a hankali.
      “Mesa? Kina son shi ne?” Nanma kai ta giad’a.
    “Miss Aleeyu” ya kira sunanta “na’am” ta amsa kan ta a sunkuye. “Look at me.” A hankali ta d’ago kanta tana kallonsa kamar yadda shima yake kallon nata. Ba komi ne tattare da idanunta ba inbanda tsoro. “Do you really love him?” Ya sake tambayar ta cikin sanyin murya.

      Hawaye tajiyo na ciko mata, “no Mr. Fauzi banasan sa, ban tab’a san sa ba, mugu ne, azzalimin da besan daraja ta ba.”
     “Shhh is okay kar kiyi kuka, bakiya sansa baraki aure sa ba kinji?” Har hawayen nata sun soma sauk’owa ya ciro hanky ya mik’a mata amsa tayi ta share hawayen. “Sir how? Baffah Khaleel is powerful ni nasan dole zan auri Ya Farouq.”
  “No baraki aure sa ba I promise, jeki huta Kacallah ze kula da aiki ki yau.”
   “Sir don’t worry zan iya yin aik-” bata k’are maganar ba ya katse ta “banasan musu idanunki sun riga sun nuna baki samu bacci ba jiya so just go before I change my mind.” A hankali ta juya sanda takai bakin k’ofa sannan ta juyo tana kallonsa taga yana tattara files na gabansa “Mr. Fauzi” ta kira sunansa chak ya bar abinda yakeyi tare da d’ago blue eyes nasa yana kallonta. “Yes?” Ya bata amsa.
    “Thank you” tace dashi. D’an murmushi ya saki wanda ya sake bayyano da kyan sa. Giad’a mata kai yayi as an answer sannan ya cigaba da abinda yake a yayinda tafice zuwa office nata ita kuwa.

    Batasan me ba amman kwana biyun nan in _TANA TARE DA_ Mr. Fauzi setaji she is safe kuma setaji ta ba damuwa. Kan cushion nata ta baje a hankali bacci me uban nauyin gaske ya isketa wanda takasa yi jiya da daddare dan yadda damuwa suka mata yawa.

  30 minutes later...

A nitse kuma a hankali Anas ya bud’e office na Fannah. Taku d’ai d’ai yake a hankali har yashigo cikin office d’in zube ya sameta kan 3 seater tana bacci peacefully. Har gabanta ya tako tare da tsugunawa d’an hijabin daya tare mata fuska yasa hannu ya gyara dogayen eyelashes nata yatsaya yana kallo sannan yakoma kan girarta dayake nan kamar na Kajol na india yadda ya had’e me kyan bala’i. Sekuma d’an siririn hancinta dayake nan madaidaici dakuma d’an bakinta dakenan ba k’aramin chanba bakuma babba ba tsakatsakiya.

    Besan dalili ba amman kawai ya tsinci kansa cikin jin dad’i, killer murmushi ne kwance kan kyakkyawar fuskarsa wanda ya lotsar da dimple nasa na gefe d’aya. Jakanta dake saqale a kafad’arta ya zira hannu ya cire a hankali yadda bare tada ita ba, tare da ajiye wa a gefe guda, k’afafunta ya daidaita kan kujerar tare da kunna AC’n a medium ta yadda beyi yawa ba bekuma yi kad’an ba. Ficewa yayi zuwa d’akinsa ya d’au wani arabian bargonsa me uban laushi da pillow yazo ya rufeta dashi tare da aza kanta kan pillow’n    ya juya ze fita kenan Fannah ta kama bakin suit nasa ta baya chak ya tsaya tare da juyowa hannun nata ya raba da kayansa a hankali sannan ya rufo mata k’ofar ya fice zuwa office nasa. Yau yagama had’a model nasa sauran asalin gini yanzu. Already filinsa na nan kawai abinda yarage shine asa drawing d’in into action.

© miemiebee

TANA TARE DA NI...

TANA TARE DA NI... PAGE 43
BY MIEMIEBEE


Bacci meh rai da lafiya Fannah tayi wanda ta jima ma batayi ba se chan bayan azahar ta tashi. A hankali ta bud’e idanunta jin kanta tayi kan pillow cike da mamaki ta duba harda bargon ma, toh waya shigo ya rufeta? Waya kunna mata AC? Ko kad’an bata kawo Mr. Fauzi arai ba saboda tasan halinsa, toh kode Yusuf ne? Toilet ta nufa ta wanke fuskarta tare da brushing sannan tafito ta ninke bargon tsab ta had’a da pillown sannan ta d’aga tafito dashi a hannunta floor na office nasu Yusuf ta nufa akan table nasa ta tsincesa bayan sun gaisa tace, “gashi nagode, shine akan ka tada ni narufe kaina kayi min wahala haka?”

    Cike da mamaki Yusuf ke kallon Fannah totally speechless. “Nikuma?” ya fad’a a k’arshe. “Ina zan samu bargo da pillow a office Fannah? Kode har yanzu baccin naki be wassake bane?”
     “Yusuf banasan wasa please amshi kayan ka, inkuma so kake kabarmin seka fito fili kace Fannah na baki.”
    Murmushi me sauti ya saki. “Fannah wallahi am serious ni banma san wai kina bacci ba kide zagaya ki tambaya waya sani ko Boss ne dakanshi nema ya rufe ki.”

    “Dariya kakeson bani komeh? Boss ya rufeni ina bacci? Impossible barinje in tambayi Ahmad da Kacallah.”
       “Zaki b’ata lokacin ki ne saboda Boss ya aikesu tun d’azu.” Yi tayi kamar bata jisa ba what if abinda Yusuf ke fad’i gaskia ne? ahaka har tashiga elevator ta hauro sama tana tsaye bakin k’ofar office na Anas amman takasa shiga inkuma ba nashi bane fah? Yace tacika shisshigi da k’yar de tasamu tayi knocking a hankali.

   
     Daidai Anas ya d’au bottle na beer nasa ze sha kenan knock yashigo. Haka kawai yau yaji yana san yad’an bugu saboda ya kwana biyu be sha ba tunda Fannah na bacci bare d’an sha abinsa kuma ba ma haka ba so yake yabar tunanin Fannah, ba abinda ya tsinana wa kansa yau, wai mesa ma yaje ya rufeta d’azu da take bacci? Tausayi ne ya fad’a a fili. I don’t love Fannah I just pity her yayi reminding kansa. “Who is it?” Ya tambaya.

    Chan murya k’asa k’asa a hankali tace, “Fannah ce.” Da sauri ya rufe bottle d’in tare da jawo drawer’n gefensa ya rufe. Turare ya feffesa cikin office d’in dan kashe warin giyan tare da kimtsawa sannan yace, “come in.” Tana shiga yaganta da pillow da bargon, kallonta yake har sanda ta k’ariso gaban table nasa. Shiru tayi tana nazarin taya zata fara masa maganan, shima shirun yayi tare da had’a hannayensa biyu k’ark’ashin hab’ansa yana kallonta kamar hoto. Can ta fara kamar haka;
 
   “Ermm Mr. Fauzi ban sani ba ko wannan naka ne, na tambaya su Yusuf duk sunce ba nasu bane.”
    Kallonta har yanzu yake da wani murmushin tsiya karara a fuskarsa.  “Wato dan kin maidani dustbin shine zaki kawo min?”
     Kai ta d’ago tana kallonsa “No Sir ba abin da nake nufi ba kenan-” katseta yayi
   “Shine mana, kin tambayi saurayinki Yusuf yace ba nashi bane shine kikace bari ki kawo wa dustbin shikam ze karb’a koba haka ba?”
    “No Sir thats not what I mean, in ajiye maka a ina?”
   “Ba nawa bane” ya bata takaicaccen amsa. Kanta ne ya d’aure. Kamar ya ba nasa ba? Toh na waye? Ita se yanzu ma ta tuna ranan da Mr. Fauzi ya rufeta a d’akinsa ai taga bargon nan akan gadonsa, to mesa zece ba nasa bane?
    “Sir but ranan naga bargon nan a d’akinka.”
    “Aww mak’aryaci kikeson ki kira ni dashi kenan, ince miki ba nawa bane kice nawa ne”
   “No Sir ba abinda nake nufi ba kenan.”
    “Inma tunani kike wai da kike bacci ni naje na rufe ki toh you are mistaking dan ni ko shiga office naki banyi ba.”
    “I’m sorry” tace cike da kunya ita de tasan ranan tabbas taga wannan bargo a d’akin Mr. Fauzi kuma gashi yace ba nashi bane. “Jeki ajiye kidawo am waiting for you.” Bayan minti d’aya Fannah ta dawo “yes Sir.” So yake ya ce mata suje suci abinci amman girman kai ya hanasa. Seya bud’e baki ze fad’a se yayi shiru.
 
   Ganin baida niyyan magana Fannah tace, “Sir you called me.”
   “Ina sane ai” yabata amsa. “Ko ban tambaya bama nasan kinajin yunwa lets go and eat.” ya fad’a in an I dont care tune.
       Qarya tayi niyyan masa tace tana azumi seta tuna yasan batada tsarki.  “Sir I’m not hungry thanks.”
    “Toh ni inaji lets go” zata sake magana yace, “banasan musu” bayan sa ta nufa bayan ya rufo k’ofar office nasa Fannah ta juya zata nufa public elevator, hijabinta ya rik’o. A tsorace ta juyo tana kallon had’add’un yatunsa daya k’ayata su da zobunan azurfa masu tsada rik’e da hijabinta sannan back to fuskarsa. Beso suka had’a ido ba “mu shiga nawa” yace mata. Kai ta giad’a masa a sanyaye tabi bayansa suka shiga private elevator’nsa ba wanda yace ko uffan ahaka har suka sauk’a driver yayi driving nasu zuwa wani hotel na daban ma yau. Abinci me rai da lafiya Anas ya mata ordering. “Eat” yace mata alokacin daya d’aga spoon nasa, ba musu ba gardama itama ta d’au spoon suka soma ci.

    Ko da yagama cin nasa zaman jirarta yayi data gama ya tambayeta, “a k’ara miki?” Kai ta kad’a masa bayan ya biya suka koma office d’an errands kad’an Fannah tayi wa Mr. Fauzi, lokacin tashinsu nayi ta wuce gidah.
     Shima Anas yana gama abinda yakeyi ya kama hanyan gida, tuk’i yake hankalinsa kwance ya d’ibo bottle na giyansa biyu yau a paint house nasa ze kwana, unguwar shiru yake ba mutane sosai yana cikin tuk’i yaga mota ya fito from nowhere yayi blocking nasa, ikon Allah ya tsaya gani reverse ya gwadayi a take yaga bayan san ma anyi blocking. Toh su waye ne? Kafin yanemi amsa wa tambayan daya ma kansa yaga maza uku sun fito daga motar gaban nasa da angansu anga ‘yan maye ‘yan bayan gari. Murmushi kad’an ya saki dan in ‘yan su uku ne acikin minti biyar ze gama dasu. Kafin ya yi yunk’urin yin wani abu yaji ana knocking jikin window’nsa. Window’n yayi wining “munada problem neh?” Ya tambaye gayen.

      “Dade ka fito tukuna.” cewar gayen. Ba gardama ya fito ya tsaya nanne yaga duka duka mazan guda biyar ne. “Will you guys let me pass or senayi muku abinda bakuwa so?”  Familiar murya ya jiyo daga behind nasa yana cewa;
    “Kokuma mu mu maka abinda baka so ba Mr. Fauzi” yana kai dubansa gun da ya jiyo muryan idanunsa suka sauk’a kan Farouq yawani pake kan driver’s sit cike da isa ya taso tare da takowa gunsu Anas.
    “You’ve had your time the other day now is mine.”
    Wani erin dariyan rainin hankali Anas ya saki harda tafi “you are such a genius Farouq. Wai ka d’au dakai da wannan mashirmatan daka taran zaku iya min wani abu ne?”

   Dariyan bosawa Farouq ya saki “Mr. Fauzi kenan kasani sarkin yawa yafi sarkin k’arfi. Apologise to me, tell me sorry akan abinda kamin jiya and I will let you a save passage.”
   “Ni in ce maka sorry?” Yayi murmushi “never!”
   “ATTACK!!!” Farouq ya fad’i nan maza biyar d’in suka soma nufuwa wajen Anas. Sleeves nasa yayi rolling tare da ciro Rolex agogonsa kafin ace me suka b’arke cikin mumunar fad’an BIYAR akan D’AYA. Farouq na tsaye a gefe yana kallon yadda Anas yake destroying masa mutane, duk se kamar yafi k’arfinsu dukda suma suna k’ok’ari dan har sun fasa masa baki amman yafi cin uwarsu. Tsawa Farouq ya daka musu “wai zakuce shi kad’ai yafi ku duka k’arfi ne?”

    Ai se kamar maganar Farouq k’arfi ya k’ara musu. Sunayi Anas yanayi har suka samu sukaci galaba akansa hanci, baki ba wanda basu fasa masa ba. Hannayensa suka kama ta kowani gefe a lokacinda Farouq ya taso daga inda yake. “Ohhh look at you Mr. Fauzi abin tausayi, ina k’arfin naka yaje? Ina polisawan naka? Kud’in ka ya ceto ka mana.” Fuskar Mr. Fauzi dayake yoyon jini Farouq ya d’ago “tell me meh had’inka da mata ta Fannah?”
 
    Murmushi Anas yayi dukda azaban dayake ji. “Kaikuma tell me meh had’inka da alak’a na da ita? Mind your damn business.”
     “Bakinka be ruhu ba kenan har yanzu. Rik’e min shi dakyau” yace da mazan nasa. Gagam suka sake damk’e Mr. Fauzi punch me rai da lafiya Farouq ya kai masa wanda seda idanun Anas suka juya. “Nace meh alak’arka da matata?”
   “Fannah is not your wife” ya fad’a a wahalince. “Take note”
     “Har yanzu baka bugu ba.” Naushi yakai ma Anas a ciki wanda sakamakon hakan ya saki k’ara sosai dan azaba.
    “For the last time me had’inka da Fannah?”
    “Kanason kaji me had’ina da Fannah? FANNAH IS MY GIRL, I LOVE HER.
    Cike da b’acin rai Farouq ya cukumo kolar rigan Anas “me kace? Sake nanata abinda ka fad’a inji”
   “I LOVE FANNAH, KUMA NI ZAN AURETA BA KAI BA, FANNAH TAWA CE!!!”
    “You really want to die.” Naushi lafiyayyu guda uku ya kai wa Anas aciki biyu kuma a fuska. Kaca-kaca suka ma Anas, duk wanda ya kallesa bare so sake sa idanunsa kansa ba duk jikinsa jini.
 
   “Me alak’ar ka da Fannah? Kace min baka son ta kuma baka santa ba.”
     Da k’yar yake maganan “NEVER!! I LOVE FANNAH, ko kasheni zakayi bare canza komai ba.”
    A fusace Farouq yace, “Baaba” na gefen daman Anas “je cikin trunk na motan can kaciro min sandan chan nakega inba dukan mutuwa na masa ba bare shiga hankalinsa ba. Zakace baka son Fannah ko yaya?” Shiru Anas yamasa bece komai ba se nishin wahalan dayake yi abin tausayi.

     “Farouq ga ‘yan patrol zuwa fa!” Baaba yayi exclaiming da ihun gaske ai kamar kyaftawan ido su Farouq suka lodu a mota suka bar wajen a 360. Anas na kwance helplessly a k’asa. Bayan motan patrol d’in ya k’ariso polisawan suka diddiro ganin mutum a k’asa, plate number’n motar Anas d’ayan ya karanta yaga “Mr. Fauzi.”
    “Guys Mr. Fauzi ne!” da gudu sukayi kansa suka d’ago sa zuwa motar sa tare da miqar dashi a back seat. “Abba lets go, mu kaisa asibiti push the start button.” d’ayan officer’n ya fad’i. A wahalince Anas yace, “no karku kaini asibiti just drive me home, to my paint house.”
   “Sir but you are badly injured.”
    “I know, ku kaini paint house d’ina kawai.”
   “Okay sir ina ne paint house d’in?” Nan Anas ya musu kwatance murya yana d’aukewa. “Sir su wa suka maka haka?” Har ya bud’e baki ze kira sunan Farouq seya tuna in ya fad’a musu definately zasu kama Farouq su rufe sa kuma, in hakan ya faru kuwa Fannah barata ji dad’i ba. “Nima bansan suba” yama officers d’in k’arya “ ‘yan iskan unguwa ne kawai.”

    Daidai gaban paint house nasa suka iso. “You can go now zan k’arasa da kaina nagode.” Cewar Anas idanunsa suna kafewa.
    “Sir amman kace barakaje asibiti ba? Wannan mutane sunji maka ciwo fah.”
   “Don’t worry I can take care of myself.” Bottles na giyansa guda biyu yaciro da k’yar yake iya tafiya dan kalan dukan dayasha wajen Farouq da mutanensa, ahaka har ya samu ya isa ciki ko k’ofan ma yakasa locking. Bayi ya nufa da rarrafe da taimakon sink ya mik’e ya kalli fuskarsa a madubi. Sam beso sake kalla ba dan irin ciwon da suka ji masa. Ruwa ya gwada wanke fuskar nasa dashi. Aiko ruwan na tab’a fuskar ya saki k’ara dan azaba daga k’arshe hak’ura yayi yakoma d’aki tare da rage kayan jikinsa yabar short nicker kawai. Kwalba d’aya ya kwankwad’e tas dan samun bacci, yana shanye wa kuwa bugeggen bacci ya d’ibesa ko sallan maghrib beyi ba bale na isha. Wayoyinsa dake cikin mota kuwa se kiransa su Ummie suke ba iyaka amman bai d’aukawa hankalin kowa ya tashi, ko da sukaje office nasa suka tambaya kuwa, kowa ya shaida Mr. Fauzi yabar building d’in lafiya.

***

    Washegari...
    8:10AM yama Fannah a office sede tata knocking a bakin k’ofar office nasa amman shiru chan ta gwada bud’ewa taji a rufe alaman Mr. Fauzi bezo bama kenan! To meya rik’esa? Shida ko lattin minti d’aya baya yi. Meya faru? Mesa bezo ba? Ko baida lafiya ne? Minti 15 ta k’ara tana jiransa amman ba alamansa. Gashi yanada board meeting by 10:30AM. Ganin ba mahalicci se Allah kawai ta sauk’a k’asa ta samu Kacallah tare da tambayansa ko sunyi waya da Mr. Fauzi.
    “A’a wallahi nima Fannah na kirasa ta duka layinsa baya d’agawa tun jiya na rasa dalili.” Kawai setaji gabanta na fad’i. “Toh nagode” tace masa.
   Wayarta taciro ta kirasa har ya tsinke be d’aga ba. Tashin hankali. To ina yashiga? Amal ta kira ta tambayeta ko Anas na gida cike da tashin hankali Amal tace mata itama tun jiya suke neman Anas bedawo gida ba.

    Napep ta tsara bata tsaya ko inaba se paint house na Anas motarsa tagani fake gaban gidan wani hamdala tasaki har ta ciro wayarta zata kira Amal ta sanar da ita se kuma ta fasa, bari de ta tabbata ko yana ciki tukuna. Door bell ta danna sau uku amman ba response. Tana gwada murd’a hannun taga k’ofar abud’e ba sak’e sak’en da bezo mata ba toh kode barayi ne suka shigo masa? Subhanallah amman ai kuma ga motarsa. Ciki tashiga ta lek’a kitchen ba alaman ko motsin mutum “Mr. Fauzi!” ta kira sunansa shiru d’ayan d’akin ta bud’e taga nan ma bayanan toilet dinma haka, guest toilet ma ta duba bata gansa ba. Daga k’arshe d’ayan d’akin ta bud’e a hankali kwalban giya ta soma cin karo dashi, se fad’i gabanta yake ta d’aga tare da k’arisawa cikin d’akin tana taku a hankali cike da tsoro. “Mr. Fauzi!” Ta kira sunan sa alokacin data gansa kwance kan gado yayi ruf da ciki se bacci yake yi ba ko riga jikinsa se bedsheet daya ja zuwa tsakiyar cikinsa.

    A nitse ta k’arisa gefen gadon tare da ajiye kwalban kan side drawer. “Mr. Fauzi!” Ta sake kiran sunansa shiru be amsa ba. Toh kode mutuwa yayi ne? Sede kuma tajisa yana numfashi. Jijjik’asa ta hau yi har se lokacin daya soma motsawa. “Waye ne?” Ya tambaya cikin bacci.
    “Sir Fannah ce, Fannah Aleeyu.”
   “Fannah? Me kikeyi anan? Ban rufe k’ofan bane?”
   “Eh sir baka rufe ba, you need to get up kanada board meeting by 10:30AM.”
   Cikin bacci yace, “barinje ba kiyi cancelling, tell them barin samu zuwa ba.”
    “Sir but why? Kayi hak’uri ka tashi please.” Bece da ita komai ba ya cigaba da baccinsa. Pillow’n daya rufe fuskar sa dashi ta d’aga. Ido ta zaro tana salati alokacin da taga irin ta’addancin da aka ma Anas a fuska. Meya samesa? Waya masa duka haka?

    “Subhanallahi Mr. Fauzi meya sameka? Omg!” ta tambaya a kid’ime a lokacin da ta tsuguna gabansa.
     Da k’yar ya iya bud’a baki yace, “ki rufe min fuska banasan hasken nan.”
     Ignoring nasa tayi “Mr. Fauzi waya maka haka da fuska? Fad’a kayi da wani neh? Meya sameka?”
     “Bansani ba nima just leave me get out.” Haka kawai yaji baya san Fannah tagansa a bad condition irin na yau, bayasan yasa ta cikin damuwa bayasan taji tausayinsa.

   “No Mr. Fauzi I’m not leaving you like this.” Hannu tasa ta dafe goshinta bata ma san ta ina zata fara ba. Hawaye kawai taji yana gangaro mata kan kumatu dan uban tausayi irin nata. Hannu ta aza ta tab’a gefen idansa daya kumburo dan bugun daya sha. K’ara ya saki wanda yasa ta mayar da hannunta baya da wuri. “Sorry” tace cikin kuka. Idanunsa na sauk’a kanta yaga tana hawaye abinda baya so kenan.
   “Miss Aleeyu leave please, goo.”
    “I can’t leave you like this, Mr. Fauzi asibiti yakamata muje su duba ka.”
   

      “Barinje ba” yabata takaicaccen amsa idanunsa a rufe.
   “Please” ta rok’esa tana hawaye ganin yadda aka masa destroying kyakkyawar fuskarsa da a yanzu mutum bare so ya kalla sau biyu ba.

 
   *© miemiebee*

TANA TARE DA NI...

TANA TARE DA NI... PAGE 44
BY MIEMIEBEE


      “Miss Aleeyu barin je ba kema leave I can take care of myself” hannu ya mik’a ze amsa pillow’n se kawai ya saki k’ara dan zafin dayaji a cikinsa saboda blows da Farouq ya riga kai masa. A rikice tace, “meneh Mr. Fauzi?” Kafin ya amsata ya mata k’arya ta kwaye bedsheet d’in daya ruhu dashin, hannu ta aza kan bakinta cike da mamaki “Subhanallahi Mr. Fauzi dan Allah meya sameka? Ina kasamu wannan ciwuka? Kalli cikin ka? Ya Salam!!!” Ta fad’i tana hawaye tana kallon cikin Anas da yayi har wani purple brownish colour dan azaba.
 
       “Mr. Fauzi meya same ka please?” Ta sake tambaya hankali tashe.
      “Nace miki babu in kinsan kuka zaki tayi anan kuma go, leave, I can take care of myself.”
    Innalillahi! what do I do now ta tambayi kanta barata iya barin Anas haka ba he is badly wounded ga fuska ga ciki meya samesa ko b’arayi ne suka shigo suka masa duka? Amman kuma ai gidan tsaf yake ba abinda aka b’arnata. Toh meneh?
          “Mr. Fauzi please kayi hak’uri mu kaika asibiti kaji? Yi hak’uri.” Ta fad’a still tana hawaye dan tsantsan tausayi. Danko ba wanda zega ta’addancin da aka ma Anas be tausayawa masa ko be zubda hawaye  ba.

             “Nace miki barinje ba kitafi please.” Wayarta ta ciro zata soma dialing number’n Amal dan sanar da ita halin da ake ciki.
    “Me zakiyi?” ya tambayeta.
   “Zan kira Amal ne in sanar da family’nka I’ve found you tun jiya suke neman ka.”

     “No karki kira su hang up.”
  “But Sir-” katse ta yayi ta hanyan daka mata tsawan da seda shi kansa ya masa ciwo “I said hang up!” Kansa ya dafe yana muntsika fuska cike da azaba. Nan ta katse ta matso kusa dashi “Sir kanka ke ciwo?” Niyan shareta yayi da farko sekuma ya giad’a mata kai a k’arshe. Jakarta ta ajiye kan side drawer ta nufa toilet tare da fitowa da bowl cike da warm water data d’iga dettol ciki dakuma towels guda biyu, jakarta ta ture gefe tare da ajiye bowl d’in akai. Kallonta yake “me zakiyi?”
   
    “Sir your face is a mess, zan goge maka ne.”
   “Banaso just leave.”
   “No Sir I’m not leaving mesa kai zaka taimaka min amman ni bakasan na taimaka maka? Saboda bankai inyi offering maka help bane? Saboda ka raina ni banida standard? Saboda ni talaka ce? Is that it Sir?”
   “No Miss Aleeyu that is not my point...” sekuma yayi shiru.
    “Toh kabari in biyaka taimakon dakake min koda na yau ne.” Shiru yayi chan ya giad’a mata kai.
   A ranta tace, Ya Allah kar ka kamani da laifi saboda zan tab’a na mijin da ba muharrami na ba, baida lafiya ne taimako zan masa, astaghfirullah.

   Nan ta tsoma d’ayan towel d’in cikin ruwan d’umin tare da matsewa a hankali ta d’an tab’a gefen bakinsa daya fashe. Towel d’in na tab’a wajen yajiyo zafi sosai hannunta ya kama “Sir nasan zeyi zafi hak’uri zakayi kaji? Sorry” a hankali ya sake hannun nata. Tana sake tab’a wani waje ya saki k’ara “arghhh! Ya isa kibari ze warke da kansa, go home”
    “Mr. Fauzi please mana kabari koda germs d’inne a kashe tunda baraka je asibiti ba. Please”
    Haka a nitse cike da tausayi ta riga bin duk ciwon da ke kan fuskarsa tana gogewa a hankali, sosai Anas ya riga sakin k’aran azaba in towel d’in ya tab’a masa kan ciwon ita kuwa duk lokacin daya yi d’an ihu seta basa hak’uri. Tagama da fuskarsa sauran cikin. D’ayan tsumman ta d’aga ta sa cikin ruwan kamar yadda tayi d’azu bedsheet daya rufe jikinsa dashi tasa hannu ta kwaye zuwa cibiyar sa.
    “Me kuma zakimin?” Ya tambaya yana k’ok’arin jan bedsheet din gam ta rik’e tana me hanasa yin hakan. “Ba abinda zan maka Sir zan d’an matse maka wajen ciwon ne.”
    “Don’t worry ze warke da kansa. Wai ke bakia jin tsoron zama da namiji kad’ai ne under thesame roof?” ya gwada tsorata ta ko zatace ta hak’ura zata tafi.

      “Ina ji amman in da kaine bana ji, I trust you Mr. Fauzi nasan ba abinda zaka min shiyasa. Yi hak’uri in d’an matse maka cikin kaji?” sanda ya k’are mata kallo sannan ya giad’a kai.
    A hankali ta aza hannunta kan cikinsa ta matse towel d’in kai. K’ara ya saki sosai dan azaba tare da rik’o hannunta. “Awwchh! Kibari ya isa ze warke da kansa, arghhh!”
     “Sir hak’uri zakayi sauran kad’an sorry.” Haka tata lalashinsa kamar d’an yaro. Towel tasake canzowa tare da k’aro ruwan zafi kan ruwan dan ya riga ya huce. Bayan ta zauna ta sake tsoma towel d’in ciki, cikin siririyar muryarta tace, “Sir did you get drunk yestarday”  Shiru yayi kamar be jita ba. “Sir?” Ta kirasa. “No” ya mata k’arya danko besan taga kwalban a bakin k’ofa ba.

     “Toh wancan fa kwalban meh?” Ta tambayesa a nitse. Kai ya d’aga yaga kwalban sekuma yaji kunya. “Toh me ruwanki dan nasha? You are not my mother ko ita mahaifiyar tawa bata isa ta hana niba, stay out of my personal li-” be k’arisa fad’in ‘life’ ba yasaki ihu “arghh!” Sanadiyar tab’a masa kan inda ke masa zafi sosai da Fannah tayi. “I’m sorry” tace “sauran kad’an.” Chan ta nisanta, “Mr. Fauzi will you listen to me in na fad’a maka wani abu?” Kamar wanda bare ce komai ba seyace “meh abun?” Sanda ta sake matse towel d’in ta mayar kan cikinsa tana daddanewa kan ciwon a hankali tace, “if I were you, in za’a maidani kai abani kyanka da kud’inka da ilimi da komai da kake dashi I will thank God barin na wasting rayuwa na akan shaye shaye ba. Masu shaye shaye sune wanda basuda aikin yi, wanda basuda ilimi basuda komai se shaye shayen da sukeyin. Amman kaga kai komai Allah ya baka Mr. Fauzi, you are handsome, rich and very intelligent, me kake nema? Don’t you think bakayi adalci wa Allah ba ta hanyar masa godiya da shaye shayen da kakeyi?” A hankali ta d’ago idanunta tana kallonsa shima kallon nata yake da blue eyes nasa sannan ya kawar da kallonsa daga gareta.

       “Kayi shiru Mr. Fauzi, do you think you are fair to Allah? Bayan ya gama baka komai seka gode masa ta hanyar bijire wa dokokinsa na hana kowane muslimi shaye shaye”
     “No I’m not” ya fad’a ransa b’ace, muryarsa cike da weakness. “Ke bakisan mesa na mayar da drinking abinyi ba kidena intruding min cikin personal life. Get up and leave” yace a lokacin daya d’aga hannunta daga kan cikinsa.
       “Yafi ace ka rasa mahaifiyar ka ko mahaifinka kokuma d’aya daga cikinsu ya gudu ya barku? Is that the reason kake shaye shaye?” Kallonta yake totally speechless chan kuma ya tuna ashe ranan ta karanta masa diary, cikin chan tagani. Hannunta ta raba da nasa ta mayar kan cikin nasa.
 
   Hannun nata ya kuma d’aga daga kan cikinsa “ya isa you can go banasan maganan nan, saboda kin karanta min diary hakan be baki daman fad’a min whats right or wrong ba. I’m still your Boss”
        “I know Mr. Fauzi, you are my Boss. Ammana in saboda mahaifiyar ka kake misleading precious rayuwarka ta hanyar shaye shaye you are destroying your bright future. Hakan na nuna you are weak yana nufin ka barta taci nasara kanka kenan. Show her you are strong ko ba ita you can live your life, ka mance da ita and move on if possible forgive her if not ka mance da ita. You have a very bright future kadena b’atawa ta hanyan shaye shaye kaji Mr. Fauzi?” Shiru yayi bece komai ba as ya wula cikin duniyar tunani yana nazarin duk abinda Fannah ta fad’a masa. Tabbas ba k’arya ko d’aya cikin abinda ta fad’a masa dan kuwa haka Shettima ma kullum ke fad’i masa sede koda Shettima ya masa magana bai san sauraro amman yau da Fannah tamasa maganar seyaji yanasan yayi moving on ya manta da abinda Ummimi ta masa sede bawai ze yarda ko ya aminta da mace bane a rayuwarsa ever again he is already broken.

    “Can you do that Mr. Fauzi for Amal’s sake?” Kai ya kad’a mata da nufin “a’a.”  “For mahaifinka?” Nanma ya girgiza kai. “Ummie?” girgiza kai still yayi. “For Shettima?” Nan ma haka. Cike da kunya tace, “for me?” Jiran masifar sa take setaji yace, “yes” a hankali sounding defeated.
     Idanunta ne suka sake bud’uwa cike da jin dad’i da murna. “Dagaske Sir? Zaka dena shaye shaye and move on?”
    “Yes” ya sake fad’i. Dad’i taji sosai wanda ta kasa b’oyewa. “You promise Sir?” ta tambaya dan sake tabbatawa.
   “I promise” yace. Sede duk maganan nan da suke baya kallonta. “Look at me please Sir” tace cikin murya me dad’in sauraro. Yi yayi kamar be jita ba. “Please” ta rok’esa a hankali ya dawo da blue eyes nasa kanta. “Da gaske baraka sake tab’a giya ba?” Ta tambayesa suna kallon juna. Kai ya giad’a a hankali “I promise.”

    “Mr. Fauzi thank you, thank you so much nakega am the happiest woman on earth yanzu, tun ba yau ba nake addu’ar Allah nuna min rananda zaka dena shaye shaye se gashi Allah ya nuna min yau, thank you so much.” bece me komai ba. Nan da nan ta gama matse masa cikin yadawo clean ba jini ko d’igo d’aya jikinsa sede zafin da yakeji. Tashi tayi zata toilet ta zubar da ruwan Anas ya rik’o hannunta a hankali takai dubanta kan hannun nasa sannan kuma zuwa kan Anas d’in tanasan tace masa ya sake mata hannu amman kuma tana tsoro kar yace ze canza mind nasa batun shaye shayen da yace ya dena.

       Godiya yakeson mata amman girman kansa ya hanasa, seya bud’e baki zeyi magana se wani abu ya tsaida shi. Da k’yar ya iya ya sauk'e girman kan yace;
 
      “Thank you.” ya fad’i a hankali ko kallonta baiyi. For the first time daya soma mata godiya kenan. Ita kanta abin ya bata mamaki, yau Mr. Fauzi ne yake mata godiya?! “You’re welcome Sir” ta amsa sa a takaice da murna fal a ranta. Hannun nata ya sake ta fice zuwa toilet bayan ta fito ta zauna bakin gadon kamar d’azu “sir kayi sallan Asuba?” K’arya yakeson mata yace ‘eh’ sekuma yaga ba amfani tunda ta riga tasan kad’an daga cikin sirrinsa. Kai ya girgiza mata. Kawai se jikinta ya bata ko isha ma beyi ba.
    “Isha fa?” ta tambayesa a hankali cikin dabara yadda bare fusata ba. Nan ma girgiza kai yayi. “Toh Maghrib da La’asar fah?”
  Can k’asa k’asa yace, “nayi la’asar.”
   “Masha Allah its not too late, barin had’a maka warm water sekayi wanka dan jin dad’in jikinka sekuma kayi yi alwala ka rama sallolin da ake binka koh?” Haka kawai ya tsinta kansa cikin san cika wa Fannah qudiri dakuma burinta.

    Kai ya giad’a mata. Nan ta mik’e cikin minti biyu ta had’a ta dawo. “Sir ina bath towel naka?” Nuni ya mata da hannu wajen ta nufa ta ciro “gashi” ta mik’a masa zan jira ka a parlour tana kaiwa nan ta fice.

    Sanda yayi dagaske sannan ya samu ya miqe daga kan gadon, bayi ya fad’a. Shigansa bayi da minti d’aya Fannah ta dawo ta nemi sallaya ta shimfid’a masa bayan tayi amfani da wayarta ta gano Qibla. Nan ta fice, kitchen nasa ta nufa ta d’anyi dube dube sede bataga abinda zata dafa masa ba. Fridge nasa ta bud’e froze chicken data gani ciki ta ciro takoma kitchen d’in. Soya masa tayi duka incase ko zeci zuwa rana. Flask ta nema ta juye ciki, tare da had’a masa coffee cikin flask sannan taje tayi arranging dining table masa. Daidai lokacin Anas yafito, k’amshin designer turarukan daya feshe kansa dashi tun daga sama har k’asa ne ya bugi hancin Fannah. Kai ta d’ago tana kallonsa. Sanye yake da ¾ wando fari da farar vest wanda ya bala’in masa kyau, ga wani sheqin da jik’ak’k’en gashinsa ke, kumburin fuskarsan ma ya ragu sosai, sede alamun ciwo da yankan dake ta bakinsa da gefen ido. Da sauri ta kawar da kanta kafin yace ta cika kallo dayawa. A hankali yake tafiyar har ya iso kan dining table d’in, zaman ma da k’yar yayi harda d’an k’ara “argh!” Tare da rik’e cikinsa.

     “Does it still hurts?” Ta tambayesa cike da damuwa. Kai ya girgiza mata amman ita tasan zafi yake masa. “I made you breakfast I hope you like it.” Yana kallonta tayi serving nasa kajin tare da juye masa coffeen cikin cup ta tura masa gabansa. “Zan jiraka a parlour, eat please.” Kallon abincin yayi sannan ya kalli Fannah. A hankali ta juya zata fice, hijabinta ya rik’o chak ta tsaya bata juya ba.

    “Lets eat together” yace da ita.
     “Sir naci abinci I’m full nagode.”
    “Please.” Ya fad’i wanda besan lokacin daya fad’a ba shi kansa, meke damunsa? Haka kawai yaji in ba ita bare iya cin abincin ba.
   ‘Please?’ ta nanata a zuciyar ta. Dagaske Mr. Fauzi ne yau yace mata please? Lallai!
   A nitse ta juyo, kujera opposite him ta zauna tana watsa da yatsunta. Plate ya jawo ya juye mata ragowar kazan duka. “Eat” yace da ita. Baki ta bud’e data d’ago kai taga uban kajin daya tara mata gabanta.
     “Sir ina zan kai wannan? Yayi yawa.” Hannu ta mik’a zata ja flask d’in a yayinda ya d’aga daga kan table d’in gabad’aya ba tare da yace komi ba.

    “Sir please ka rage yayi yawa.” Ignoring  nata yayi “lets eat I’m hungry.” Nasa ya soma chi itako har yanzu bata tab’a plate d’in ba ina zata kai wanga kaji?
     “Miss Aleeyu eat.” Miyau ta had’iye a hankali ta d’au cinya d’aya ta soma ci. Zaman makokin ne ya isheta tayi gyaran murya sannan tace, “Sir do you want to talk about it?” Sanda ya nisanta sannan yace, “about?” Ba tare da ya kalle ta ba.
     “Abinda ya sameka.” Kai ya girgiza “No.”
  “Okay...” tace a hankali “but Sir next time ka kiyaye please koma mene neh.”
    “Okay” yace mata kamar d’an yaron da mamansa ke masa fad’a. Haka kawai yaji bayasan fad’awa Fannah gaskian al’amarin yasan definately zatayi blaming kanta zatace duk akanta fad’an ya tashi kuma hakan ne komai a sanadin ta ya faru sede bayasan tayi feeling guilty.

      “Sir?” ta kira sunansa. “Yes” ya amsa yana sipping coffeensa. “Mesa kace kar na kira Amal na sanar da ita I’ve found you?”
   “Saboda banasan susan inada gida anan.” Sam bata fahimce me yake nufi ba, so yake yace bawanda yasan yanada gida?
    “Ke kad’ai na fara kawo wa cikin nan, ko Shettima besan I have a paint house ba.”
   
    Meh Mr. Fauzi yake nufi kenan? Does this mean tanada wani matsayi a zuciyarsa da har ya b’oye wa kowa gidan sa hatta family’naa amman ita ya sanar da ita ya kuma barta tana shiga???


© miemiebee

TANA TARE DA NI...

TANA TARE DA NI... PAGE 45
BY MIEMIEBEE


THANK YOU SO MUCH DA ADDU’O’INKU MASU SO DA K’AUNA TA, ALHAMDULILLAH NAJI SAUK’I SOSAI


          Shiru tayi bata ce komi ba as tana nazarin abu a ranta.
      “Say it out” yace yana kallonta. Mamaki ne yacika ta how comes ya gane ta nada magana a ranta.
   “Errm babu” tayi k’arya.
   “Akwai say it.”
   “I was thinking ko za’a zubar da abubuwan da suke cikin fridge d’in kar in-” katse ta yayi “jeki d’iba ki zubar, kiyi flushing duka.” Dad’i sosai taji nan take ta mik’e. “After kin gama cin abincin ki amma.”
    “Sir na k’oshi thank you” bata tsaya jiran me zece ba ta nufa fridge d’in tafito da duka kwalabe guda 15 d’in. “Sir akwai wani bayan wad’annan?” kai ya gyad’a mata.
    “Are you sure Sir?”
    Kai ya girgiza “akwai kwali d’aya k’ark’ashin gado na a d’aki.”
   “Thank you Sir.” Uku-uku ta riga d’iba tana kaiwa toilet tana zubarwa har tagama duka kwalaben kuwa tayi disposing nasu. Bayan ta gama ta d’au first aid box daga toilet tafito dashi zuwa dining space inda ta tsinci Anas zaune yayi zurfi cikin tunani. “Sir?” Ta kirawosa tare da dawo dashi daga duniyar tunanin daya wula. Kallonta kawai yayi ba tare da yace komi ba.

     “I think ciwon fuskan kan zefi healing da wuri in aka rufe” ta fad’i tana ciro wasu transparent bandages guda biyu. B’antare d’aya tayi. “May I?” Ta tambayesa kai ya giad’a mata nan ta manna masa na gefen bakin nasa a hankali sannan na kusa da idansan shima a hankali. “Get well soon” tace dashi a lokacin data rufe first aid box d’in ta mayar toilet, fitowarta ta nufi bakin k’ofa.
   “Miss Aleeyu” ya kira sunanta chak ta tsaya tare da kewayo wa. “Yes Sir.”
    “Ina zakije?”
    “I’m going home, jikin naka da sauk’i ba?”
    Alokaci d’aya kuma se yaji bayasan ta tafi, shi yake korarta d’azu amman yanzu kuma so yake ya cigaba da kasancewa _TARE DA_ ita, bayasan ta tafi wanda shi kansa besan dalili ba.

     “Must you go?” Ya tambayeta.
    A hankali tace, “Sir I have to, bareyi in cigaba da zama anan ba.”
    “Okay” yace blankly. Bata ce dashi komai ba ta fice. So yake ya tsayar da ita yace mata ta zauna dashi baya san ta tafi amman bayasan ta raina sa bayasan ta d’auka da wata manufa, ta zata ko santa yake.

    Isar Fannah gida ke da wuya ta tarar da Farouq tsaye bakin k’ofa da alama ita yake jira. Bugun zuciyarta taji ya k’aru in akwai d’an Adam data tsana a doron k’asa toh Ya Farouq ne.  Bayan ta sallami meh napep d’in ta sunkuyar da kanta tayi kamar bata gansa ba se tafiyarta take a yayinda idanunsa suke biye da ita. Takai da shiga cikin gidansu kenan kawai Farouq ya jawo ta da k’arfin gaske, kafin tayi yunk’urin yin wani abu ya matseta jikinsa gagam shi a dole yana hugging nata. “Ya Farouq me haka? Ka sakeni” se k’ok’arin k’watan kanta take amman ta kasa. Batasan lokacin data fara kuka ba. Se bugin k’irjinsa take amman kamar super glue yak’i sakinta. “Fannah mesa bara ki soni ba? Mesa Fannah? Ke bakisan ina sonki bane? Akan ki kowa ze iya mutuwa, mesa se wancan me idan turawan zaki so? Me yake dashi da banida? Tell me mesa bakiya sona?” ya k’are maganar yana wani erin zakin nishi kamar ze cinye ta tare da shunshuna hijabinta sekace ze cire.

       “Ya Farouq ka sa
Share:

4 comments:

pls drop down your comment......
dan Allah ku ajiye comment.

Tallata Kayanka

Guide Tricks Blog

Be With Me Technology

Popular Posts

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).