shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wanda aka fi sani da hausa novel wanda ni Muhammad abba gana nake rubutawa dan wayar tare da fadakarwa ga mutane a yanayin da muke ciki.

Thursday 29 September 2016

TANA TARE DA NI... PAGE 89---90

tana-tare-dani.jpg

TANA TARE DA NI... PAGE 89
BY MIEMIEBEE







      Daidai tashiwan Anas daga bacci kenan, da k’yar ya iya ya raba jikin Fannah da nasa dan wani sabon salon baccin da ta koya bata bacci se in akansa. Bayan ya tura ta gefe yasake lullub’eta da bargo sannan yayi pecking nata a goshi. Bayi ya nufa yayi wanka agurguje yasa mint blue shirt da farin ¾ wando. Kitchen ya nufa yasoma had’a musu Chocolate-chip cookies for breakfast, in less than an hour yagama komai se coffee daya had’a musu, dining table ya shirya tsab sannan ya koma d’aki dan tayar da ita, zaune ya tarar da ita se murza idanunta take. “Good morning Flower har kin tash-” besamu daman k’arisa maganan ba dan yanayin daya tsince ta ciki kamar kuka take, daya gama k’arisowa kusa da ita kuwa seya tabbatar da hakan zama yayi a gefenta.
   Cike da tashin hankali yake maganar. “Omg! Flower why are you crying?” Kasa amsa shi tayi kawai tayi hugging nasa a yayinda kukanta ya tsananta. Bayanta yake bubbugawa a hankali, “shhh! Kibar kuka kinji I’m here stop crying Flower” seda ya tabbata tayi shiru ya d’agota. “Meya faru?”
    “Habeebi promise me baraka tab’a barina ba, promise me please.” Ta sake matsesa ajikinta tana meh cigaba da kuka.
    “Shhh! I will never leave you Fannah, never ki kwantar da hankalinki _INA TARE DA KE_ forever.” Hannu yasa ya share mata hawayen ”meya kawo wannan zance? Kinyi mafarki ne?” Kai ta gyad’a masa. “You want to talk about it?” Nan kuma ta kad’a mai kai “I’m afraid Habeebi.”
    “Toh shikenan is okay, tashi kiyi wanka yanzu.” Ba musu ta miqe ta amshi towel dayake miqa mata bayan ta cire kayan jikinta ta d’aura towel d’in “Habeebi ka rakani bathroom d’in wallahi tsoro nake wai Ya Farouq na ciki.”
     “Mafarkin Farouq kikayi dama?” Cike da tsoro ta gyad’a kai. “Karki damu Farouq is gone foever.”
   “Nasani Habeebi still ina tsoro ka rakani please” hannunta ya riqe yakaita har bathroom d’in tabarsa yafito tak’i labule taja ta tare kanta shiko yana zaune akan hand basin bayan data gama suka fito tare man shafawanta ta nema kap kan mirron babu. “Habeebi kaga lotion d’ina?” Se ayanzu ya tuna ya had’a cikin akwati d’azu. “Bangani ba Flower, babu akan mirron?” yayi qarya.
   “Babu” tayi maganar tana nufan wardrobe dan ciro sabo.
   “Wait wait!” yayi sauri ya dakatar da ita, “babu achan ga vaseline chan ki shafa.”
  “Habeebi wai me kake b’oyewa cikin wardrobe d’innan ne?”
   “Kan Farouq ne aciki kika kuskura kik-” be samu daman k’arisa maganan ba sanadiyar tsallen da Fannah ta daka se a jikinsa ta tsaya chak! hannu yasa ya tare ta kafin ta fad’i. “Na tuba wallahi barin bud’e ba, dan Allah kabari ina vaseline d’in zan shafa.” Dariya sosai ya tsaya yi “toh muje mu shafa miki amman sauk’a tukuna.” ya gwada cire hannyenta dake rataye a wuyansa, kafad’a ta buga nufin barata sauk’a ba tare da sake kankamesa, haka tana zaune kan cinyarsa ta shafa manta. Kayan ta daya cire mata wani baqin abaya ya miqa mata, “gashi sa.”

     “Habeebi abaya nefah.”
   “Ina sane ai” ya gyad’a mata kai.
   “Toh ina zamuje da zan sa abaya?”
  “Ikon Allah! Mom Hanan ko d’an bincike seya baki hanya wani irin bincike ne haka?! Allah kika sake questioning d’ina zan bud’e wardrobe d’in Farouq yafito.”
   “Nabari nabari please kabar fad’in sunansa Hanan zatayi kuka.”
   “Toh Mom Hanan na dena” yayi managar hannunsa na akan cikinta. “Flower yaushe Hanan zata soma motsi I want to feel her.”
    “Dr tace se pregnancy’n yakai zuwa 16 weeks and Hanan is just 8 weeks yanzu kaga da saura.”
    “Ohh kice min se cikin ki yayi k’aaaatoo Hanan zata fara motsi.” Hannunsa ta d’aga daga kan cikin nata “nifa na fad’a maka bawai wasan nan na sani dariya bane banaso.”
    “Toh I’m sorry yi sauri kisa kayanki.”
  “In nasa ina zam-” bata k’arisa maganan ba tayi tsit dan ta tuna da abinda Anas yace mata akan ta sake masa tambaya ze ciro kan Ya Farouq cikin wardrobe. Kamar baby ya riqota a hannu zuwa dining table yasan ta da kewaye kewaye kar idanunta sukai kan akwatinan nasu.

    “Habeebi harda breakfast kamana yau wow!” Yana bud’e flask d’in k’amshin abincin ya mamaye wajen gabad’aya se shaqa Fannah ke tana d’igan miyau. “Baby hurry up and serve me yunwa nakeji.”
   “Kwad’ayi kike ji de.” K’aramar tsuka taja ta bugesa gefe ta amshi flask d’in taja gabanta ta soma chi. Tsayuwa yayi yana kallon ta cike da mamaki ganin takusa cinyewa ba shi yayi magana “Flower nifa ban chiba karki cinye duka.”
    “Ayyah Habeebi, Hanan kuma fah? Kayi hak’uri kabarmu mu cinye mana.”
    “Bawani Hanan d’innan glutton (meh shegen cin abinci) kawai.”
   “Kafad’i koma meh mu cinye?” Kai ya gyad’a mata yana murmushi yadda takecin abinci na bala’in kashesa. Bayan da ta gama yaje yayi frying sausages ya karya dashi shima. Bayan da suka gama ya tattara dining table d’in “Flower jekisa mayafin abayan naki we are going somewhere.”
   
     “Ina kenan Habeebi?”
   “Aww! inje inciro kan Farouq ko?”
   “A’a please nayi shiru.”
  “Better jeki shirya ina jiranki and karki bud’e wardrobe d’in ni na fad’a miki.”
   “Toh Habeebi kazo muje tare wallahi tsoro nakeji” seda yayi ta mata tsiya sannan ya rakata yana ganinta tana shiryawa har tagama tayi arabian rolling mekyau me amsarta sannan ta feffesehe da turare d’ayan da kad’ai tagani kan mirron ta tambayi Anas ina sauran turarukanta kuma tana tsoron kar yaciro kan Farouq daga cikin wardrobe. “Kingama?” Ya k’are maganar hannunsa k’ark’ashin hab’anta yana kallon fuskarta datasha light makeup.
    “Eh nagama semeh kuma yanzu?”
  “Se...” Yakai bakinsa kan nata “Habeeb-” be sake mata baki ba seda ya tand’e maroon strawberry flavor jan bakin data shafa tas.
    “Haba! Habeebi” tayi maganar lokacin da ta juyo tana kallon bakin nata a mirror. “Mena sharemin jan bakin yanzu?” Tayi pouting lips nata.
   “Saboda yamiki kyau sosai and banason in mun fita mutane suna kalla min ke, because you are mine Flower, as from today banason ki sake yin makeup in zamu fita okay?”
   “Nikam wannan Habeebin” tayi maganar chan k’asa k’asa tana zumbure zumbure.
   “Yes Flower kajol da nude lipstick kawai na yarda kina sawa kinji?” Shiruu “nace kinji?”
   “Naji-” katsesa yayi “good, agida kawai na yarda kina kwalya.”
   “Habeebi gaskia akwai ka da son kai amma kaika iya d’aukan wanka kamar me zuwa gidan biki idan zaka fita.”
    “Toh mijinki neni ai” be jira ta sake magana ba yajata waje zuwa mota sannan ya dawo ya kai boxes nasu mota dake se game nata take ta  bugawa ko kad’an bata ga me yake ba seda ya shigo mota ya tambayeta “Mom Hanan are you ready?”
   “Do I have a choice bayan baka sanar dani ina zaka kaini ba.”
   “Karki damu you’ll find out soon.” Seda ta bari sukayi nisa da tafiya ta yadda barasu iya komawa gida ba, balle yace ze ciro kan Farouq tasoma jero masa tambayoyi wanda duk ciki ba wanda ya bata straight answer.

     Wani tambayan ma seda ta ga sun dosa hanyan airport “Habeebi wai me zamuyi anan?†
    “Flower inda zaki d’an k’ara hak’uri everything will turn out cool.” Badan tanaso ba tayi shiru waje yanema yayi parking sannan ya fito da ita a yayinda wani security ya cicciro musu luggages nasu “Habeebi wannan fa akwatina ne a hannun mutumin nan” tayi maganar tana bin mutimin da kallo.
  “Yes ina sane Flower” ya jawota jikinsa.
   “Toh a ina ya samu?”
   “Acikin booth kayakin mune aciki.” Cike da mamaki da rashin yarda tsantsan mamaki ta d’ago kai tana kallonsa. “Kayan mu aciki? Kana nufin tafiya zamuyi?” Gira ya d’aga mata.
    “What?! Habeebi-” yatsansa ya aza a lips nata “shhhh! Nasan me zakice ban fad’a miki ba you are not ready barakije ba but please don’t say so kinji? Don’t ruin this I’ve worked hard for it.”

    Hugging nashi tayi abinda beyi tsammani ba a tunaninsa she will freak out tace masa barata jeba. Cikin sauti cike da jin dad’i tayi maganar, “Taya zance barinje ba Habeebi bayan nasan you worked hard for it I just hope we will enjoy inda zaka kaimu. Me, you and our Hanan Habeebi.” Dad’in kalamunta yaji sosai yayi hugging nata back “we will in shaa Allah Flower, I love you dearly.” Bayan tayi breaking hug d’in ta ciro wayarta daga jakarta “me zakiyi Mom Hanan?”
   “Zan kira Mami in sanar da ita.” Wayar ya amsa “don’t worry na riga na sanar da ita lets just go, hope you are ready to go fly to Abuja?”
   “Abuja? Okay I am ready.” Wajen private jet nasa wanda be tab’a tafiya dashi ba yau ne karo na farko suka nufa se admiring jirgin Fannah ke bata tab’a ganin kalan jirgin ba se a TV.
    “Habeebi mu kad’ai zamuyi tafiyan ne?”
    “Yes Flower this is my private jet ba public jirgi bane.”
   “Ohhh wow! Its amazing baka tab’a fad’a min ba.”
   “Sorry nima ban tab’a using nashi ba seyau tun kafin muyi aure na saya I mean tun lokacin dana fara sonki Flower I was hoping Allah ze kawo min ranan da zan shiga ciki dake that is when we’ve accept each others love just as we did a very long time ago now, I love you Flower” Kyakkyawar fuskarsa ta shafa “I love you too Abu Hanan.” Hannunta ya riqe suka shiga ciki bayan angama komai da komai sauran tashiwar jirgi Fannah tasa suka karanto add’o’in kariya. Tun anan Anas yagano ta soma jin tsoro dan kuwa this is her first time shiga jirgi.

    Seatbelts Anas yamusu tighting aiko ta riqo hannunsa gagam “Habeebi na fasa tafiyan ina jin tsoro please su tsaya.” Dariya yakeson yi amman ya b’ata rai. “Flower just keep calm muna tashi everything will be normal.”
    “No Habeebi ni kawai kace musu su tsaya” a hankali jirgin ya fara tafiya bata wani ji tsoro ba seda jirgin ya fara tashi anan ta fara kuka harda hawaye hannunta Anas ya matse cikin nasa yana fad’a mata dad’ad’d’un kalamu ahaka har suka tashi da suka fara flying kuwa seta bar jin tsoron. A hankali ta bud’e idonta d’aya sannan d’ayan. “Kin dena jin tsoron?” Kai ta gyad’a a hankali “are we flying already?”
   “Yes Flower we are kiduba window kiga.”
   “A’a tsoro nakeji.”
   “Ki leqa ba abinda ze sameki am here.” Cike da tsoro ta leqa kad’an da wuri ta dawo da kanta ciki “calm down Mom Hanan ki kwanatar da hanakalinki ko kinason Hanan ma taji tsoro ne?” Kai ta kad’a masa “good” yace tare da pecking nata, headphone ya ciro yasamata akai tare da kunna mata qira’a. Cikin ‘yan mintuna suka iso Abuja nan ma da suka zo landing kad’an ya rage Fannah batayi kuka ba.

   Transcorp Hilton Hotel Abuja suka sauk’a zuwa Azahar bayan sunchi abinci sun sake wanka suka wuce embassy’n USA  kasancewar a New York Anas yakeson suyi rainon Baby Hanan. Dad’i sosai Fannah taji daya sanar da ita plans nasa, sun gaji iya gajiya wai haka ma dan da sanin ido kenan aka samu aka gama musu abubuwan on time zuwa jibi everything will be ready seya rage sauran tafiya. Koda suka dawo gida Fannah takasa fitowa daga mota dan gajiya Anas ne ya cirota da kansa yakaita har zuwa d’akinsu. Akan gado ya direta kafin ya juya ta riqo kolan rigarsa tajasa jikinta kafin yayi wani k’wararren motsi ta kifa bayansa da gadon ita kuma ta haye kansa. “Habeebi bacci nakeji.”
    “Flower bamuyi Sallan isha bafa.”
   “I know Habeebi mubari zuwa 10-11 haka se muyi please.” Shiru yayi tare da aza hannunsa kan bayanta yana shafawa a hankali. In the next 5 minites Fannah tayi bacci. “Flower!” ya kira ta shiru ba amsa.
    “Flower har kinyi bacci?”
   “Uhmm” tayi groaning cikin baccin. D’an murmushi ya saki tare da pecking kanta. A haka shima ya samu yayi bacci se 11:27PM Anas ya tashi anan sukayi Sallah suka chi abinci sannan suka watsa ruwa suka sake komawa bacci.

     Kwanan su biyu a Abuja Anas ya sama masu visa. Washegari around 8:00AM suka d’au flight zuwa New York kamar sabon shiga haka tata jin tsoro ma yau.

     _10 hours later... Exactly 6:00PM a Nigeria 1:00PM a kuma New York_
 
     Su Anas suka shigo NY gajiya kam ansha sosai, musamman Fannah kusan duk a kwance kan gadon dake jet d’in ta yini amman hakan be hana k’afafunta kumbura dam ba.
    A MANDERIAN ORIENTAL HOTEL NY suka sauk’a. Fannah de takasa b’oye k’auyancinta inwhich Anas found so adorable and cute komai tagani seta tambaya. Warming jikinsu sukayi cikin had’ad’d’en jacuzzin dake bathroom d’in sannan suka yi ordering abinci sukaci.

     Baccin sauk’e gajiya suka yini sunayi ranan da daddare bayan sun idar da Sallan isha sunci dinner Anas yahau massaging wa Fannah k’afafunta da suka kumbura bayan daya gama mata kuma suka kwanta.
     Washegari basu fita ko inaba a d’akinsu suka wuni ba abinda suka tsinana wa kansu banda romancing juna da suka yini sunayi se the next day suka fita ganin gari leisure points da dama erinsu 911 Memorial Guided Tour with Museum, Disney on Broadway Exclusive, Magic Walking Tour, NBC studio, central park, Brooklyn bridge, 9/11 Memorial and Museum, da sauran su suka jejje se killing selfies suke Fannah nawa Afrah da kishi kamar ya kasheta sending. They had alot of fun se Maghrib suka dawo masauk’insu all tired. Sallah kawai sukayi suka miqe kan gado se bacci.

      Haka fa rayuwa ta cigaba da kasancewa Mr. And Mrs. Fauzi cikin so da k’aunan juna, zamansu a New York ba shiyasa Anas hana Fannah sa hijabi ba dukda kuwa in aka gansu se an tsaya ana kallonta amman kamar yaddda bata damu ba haka shima Anas d’in, sosai yake kishin Flowersa. Baby Hanan nasu kuwa se girma take a yanzu haka cikin Fannah nada 5 months da anganta anga me ciki dan ko har ya b’ullo kai tun anan Anas ya fara neman tsokananta dan haka tama bar zama da vest inya nan se baggi kayakin da zasu b’oye mata‘yar cikin nata, ga yadda taciko dam iya cikowa Anas baya iya hak’ura da ita yanzu aduk lokacin da ya kalleta se sha’awan ta ya taso masa kullum suna cikin yin abu d’aya.

   ****
      Yau ranar ta kasance Tuesday ayau ne Mr. and Mrs Fauzi zasuje duban gender’n Baby’nsu tunda cikin yayi k’wari, dukansu bugawa zuqatansu ke barin ma Anas dakeson ‘ya mace kamar hauka.

**
     Murna gun Anas da Fannah baya misantuwa da aka tabbatar musu mace ce baby’nsu. Sabon siyayya Anas yace zasu soma yiwa Baby Hanan yanzu da aka tabbata Hanan d’ince a hanya, inbawani ikon Allah ba.
     Ta ward d’in karb’an haihuwa suka fito aiko Fannah na ganin yadda mata masu ciki ke nak’uda yadda suke shan azaba ta rushe wa Anas da kuka. Kuka na sosai seda suka nemi waje suka zauna hankalinsa duk yabi ya tashi ya rasa meya sata kuka haka, just a while ago she was happy jin sex na baby’nta yanzu kuma tana kuka to meh dalili? Ko ta dena san ‘ya mace sena miji ne?

    “Flower is okay kinji stop crying please ya isa” ya cusa ta ajikinsa yana bubbuga bayanta har izuwa lokacin da tayi shiru.

© MIEMIEBEE

TANA TARE DA NI...

TANA TARE DA NI... PAGE 90
BY MIEMIEBEE








 
     
       “Flower mesa kike kuka? Do you want to talk about it?” A nitse ta d’ago kanta daga k’irjinsa ta share hawayenta sannan ta masa nuni da ward d’in. Cike da rashin fahimta yace, “what about it Flower?”
    “Habeebi baka ga yadda matan suke kuka bane? Yadda haihuwan ke basu wahala Habeebi I’m afraid” tasake rushewa da kuka. Kallonta ya tsaya yi Fannah barata ishesa da kallo ba. Sake kwanto da ita yayi a jikinsa yana bubbuga bayanta “is okay kinji bar kukan ya isa, you will have a safe and easy delivery in shaa Allah zamu cigaba da miki addu’a bar kukan haka ya isa.”
    “Habeebi ina tsoro kasan wasu matan daga labour room se lahira suke wucewa Habeebi banason in mutu ban rik’e Hanan ba.”
    “Flower kibar magana haka wayace zaki mutu baraki riqe Hanan ba? In shaa Allah zaki shiga labour room kuma kifito fine and good banason irin maganan nan kinji? Stop crying ya isa.” D’agota yayi sannan ya share mata hawaye “lets go and eat.”

    Ba musu ta miqe tana manne a jikinsa har suka isa gun motansu. Yana cikin driving ya juyo ya kalleta tayi lamo jikin kujeran tana kallon window.
    “Flower kinsan you are funny koh.” Ba tare da ra juyo ba ta amsa shi, “menayi kuma yanzu?”
   “Kukan da kikayi mana, gaskiya banason Hanan ta d’auko kukanki abu kad’an kuka.”
    “Sekayi ai kai dama in baka nemi tsokana naba bakajin dad’i.”
   “Oh common Mom Hanan chill please wasa nake miki.” daga nan bata sake che masa k’ala ba.
    A Restaurant Manhattan Anas yayi parking bayan ya fito da ita daga motan sukayi ciki, table dake kusa da bakin k’ofar ya zaunar da ita a yayinda ya yi ciki dan yimusu order kasancewar traditional restaurant ne. Fannah na zaune ita kad’ai kan kujerar tayi jugum har a yanzu hankalinta be kwanta ba regarding mata masu nak’uda data gani d’azu daga bisani ta d’ago kai tana kallon k’ofar seji take kamar ana binta da kallo data dudduba kuwa se bataga kowa ba.

     Kamar daga sama taji hannu dafe kan kafad’ar ta a razane ta d’ago kai acewarta ma kidnapping nata za’ayi harta bud’e baki zata sa ihu setaga mace ce ‘yar uwarta anan ne hankalinta yad’an kwanta. Bata tab’a sa matan a ido ba amman kuma she is sure ba a yau ta fara ganinta ba zuciyarta se rad’a mata take she’ve met this woman before amman ta rasa a ina.
    “Sannu Sister yi hak’uri in na razanar dake please.” matar tayi magana cikin muryarta wanda sosai yayi kama da wata wanda Fannah tasani amman ta rasa gane a ina, no matter how tayi ta tuna a’ina tasan muryar ta kasa.
   “A’ah ba komai Aunty” cewar Fannah har a yanzu se kallon wannan babbar mace me k’imanin shekaru 45 take tana me tunanin a’ina ta tab’a ganinta.
    “Toh nagode nace dan Allah wancan da kuka shigo dashi just a while ago mijnki ne?” Shiru Fannah tayi tana  nazarin ko ta bata amsa kokuwa kar ta bata saboda question d’in is too private. Shirunta ya sake bawa matar damar magana. “I’m sorry please karkiji tsoro ba abinda zan miki suna na AYSHA kuma ‘yar Nigeria ce nima kamar ku kawai I want to know ne please ki fad’amin.”
    “Eh mijina ne.” tayi maganan idanunta cikin na Aysha, hawaye ne suka soma gangarowa kan kumatun Aysha wanda yamugun bawa Fannah mamaki toh kode son Anas nata wannan Aysha ke da har zatayi kuka da ga jin ance yanada aure.

    “Aunty Aysha mesa kike kuka?”
  “Babu, babu ba komai sunan mijin naki A... A... Anas koh?” cike da mamaki Fannah ke kallonta har taya tasan sunan Anas? Ta bud’e baki zatayi magana kenan Anas yakira ta from far behind.
   “Flower!” Da sauri ta juya izuwa direction nasa, drinks biyu ne riqe a hannunsa “wannan ko wannan kikeso.” Murmushi ta saki sannan tayi nuni dana hannun daman nasa, ido ya kashe mata sannan ya koma anan ta juyo dan cigaba da magana da Aysha sede ta duba gabas da yamma kudu da arewa bataga Aysha ba. A nitse ta miqe ta fito waje tana kewaye kewaye ko zata ganta amman ko alamarta babu, badan tanaso ba ta dawo ciki ta zauna shima Anas bada dad’ewa ba yadawo da plates nasu a hannunsa nata ya ajiye mata a gabanta. “Thank you Habeebi amman basu da waiters ne sekai zaka kawo mana da kanka?”
    “Ninaso Flower, kinsan white people d’innan da shegen son mata banason su kalla min ke.” Dariya sosai take “over possessive ba” tace cikin dariya.
    “Na yarda whatever lets eat.” Cike da jin dad’i suka soma chin abincin daga bisani Fannah tace, “yauwa Habeebi bakasan meba.”
  “Meneh?” Ya tambayeta tare da kai spoon baki yanacin abincin.
   “Shiganka ciki wata mata ‘yar babba haka tazo ta sameni take tambayana wai ko kai miji na ne dana tabbatar mata mijina ne kai sekuma tasoma min kuka wai sunan ta Aysha kuma abinda yafi ban mamaki ma yadda tasan sunanka, nayi nayi intuna a ina na tab’a ganin ta amman na kasa ‘cause her face seems familiar.”

    Spoon daya kai bakinsa ya maido shi plate d’in tare da d’ago blue eyes nasa yana kallon Fannah. Anan data kuma k’are masa kallo itama se ta tuna a ina tasan kamannin fuskan Aysha, anan tagane a’ina ta tab’a ganin fuskar Aysha ashe cikin family photon su Anas ne wanda ya goge fuskarta, anan ta gane Anas nata ke kama da Aysha, muryar Amal kuwa sak na Aysha ce. Aysha itace Ummimin su Anas. Ummimi na raye bata mutu ba.

    “Kikace meh?” Cewar Anas alokaci d’aya yaji lisafin k’wak’walwarsa na gushewa jin an ambaci Aysha sunan mahaifiyarsa da ya tsaneta fiye da komai a duniya.
    “Habeebi Ummimi nagani, wallahi ita nagani just a while ago.”
    “Whaattt?!” Ya tambayeta cike da k’in yarda.
   “Habeebi itace wallahi itace, Ummimi ce tana raye tashi mu neme ta I know she is somewhere close to us” kafin ta miqe Anas ya zaunar da ita har a yanzu besan meyake ciki ba tunaninsa duk ya jagule kayinsa na juyawa. K’arfin hali yayi yace, “ba ita bace Flower, Ummimi ta mutu inma bata mutu ba tana chan bangon duniya da mijinta da yaranta saboda haka ba ita kika gani ba lets eat and leave this place.”
   “Hab-” katse ta yayi a tsawace “I said enough ba ita bace!” Ta mugun firgita barata iya tuna when last Anas ya mata tsawa haka ba ‘yar k’ollan dake ciko mata a ido tayi sauri ta shanyesu bata sake ce masa komai ba.
    Sunfi minti biyu zaune ahaka ba tare da sunce da juna ko uffan ba, abincin gabansu ma duk sun kasa chi as Fannah ta zura wa Anas daya zurfafa cikin tunani ido.

      _What if abinda Fannah ke fad’i gaskia ne dan kuwa be tab’a fad’a mata asalin sunan Ummimi ba how comes zata sani inhar bawai taga Ummimin bane dagaske. Amman kuma is it possible? Meze kawo Ummimi New York? Dakansa ya amsa wannan tambaya._
     _Ai koda tazo tafiya ce mana tayi wanda ze aureta yace ze kaita k’asar waje meaning k’asar waje nan New York ya kawota kenan?_

    Kai ya girgiza a sauri “No it can’t be!” yayi maganar a fili. Hankalin Fannah yayi matuqar tashi ganin hankalin Habeebinta ba’a kwance ba.
     “Habeebi is okay kaji? Ya isa haka Abu Hanan.” tasa hanky ta share masa zafaffun gumin dake k’eto masa. “Lets go” yace da ita tare da miqewa ya riqo hannunta suka fito suka kama hanyan lot kamar ance Fannah juya ta juya idanunta basu sauk’a ako ina ba sekan Ummimi dake tsaye daga bakin k’ofan Restor d’in, sanye take da hijabi bak’i iyaka guiwa fuskarta duk alamun hawaye, kallo d’aya za’a mata agano tsantsan rashin kwanciyan hankali da wahala tattare da ita amman duk da hakan kyawun halittan fuskarta wanda su Anas suka d’auko be gushe ba.

     “Habeebi” Fannah takira sunansa tare da dakatar da tafiyarta badan yanaso ba yatsaya shima batare da ya raba hannayensu ba. “What is it Flower? Lets go!” Yayi maganar cikin wani erin murya. “Habeebi ka juya ka ganta gata chan” a hankali yake karkato da kansa har ya juya gabad’aya sannan ya d’ogo blue eyes nasa ya miqar basu sauqa ko ina ba se akan Ummimi. Kallonta yake cike da rashin yarda, sam yakasa yarda Ummimi ce yau a gabansa shekaru nawa rabuwansa da yasata a ido? 15 good years, memories na incident daya faru lokacin tafiyar Ummimi ne suka soma masa yawo a k’wak’walwa.

      “Anas” yaji muryar Ummimi dake nan kamar na Amal na tsamo sa daga duniyar tunanin daya wula, a gabanshi yaga Ummimi tsaye idanunta cike dam da hawaye tana kallon cikin idanunsa. “Anas... My.. My... My son... Anas my son” tasa hannu akan kumatunsa tana shafawa a hankali ayayinda k’arfin kukanta ya dad’u, shi kansa Anas idanuwansa sun kad’a sunyi jazir, he don’t even know what he is feeling fatansa kad’ai Allah sa dukkannin wannan mafarki ne.
     “Anas my son kamin magana dan Allah.” Hannunta ya sauk’e daga fuskarsa cike da k’in yardan itance a gabansa. “Ummimi?” Ya kira sunanta. “Kece?”
    “Nice Anas, Ummimi ce mahaifiyarka, Ummimi ce your own very real mother, Anas nice.” Duk yadda yayi dan shanye kukan yakasa besan a lokacinda yasoma zubar da hawaye ba, Fannah dake tsaye a gefensu tayi shiru ta k’ure musu ido tana kallon yadda suke zubar da hawaye.
     “Anas kayi min magana please” yunk’urin hugging nasa tayi wanda sakamakon haka yaja baya da wuri. Hannun Fannah ya rik’o “lets go Flower” nan ya juya.
   
    “Anas!... Anas! dan Allah ka tsaya.” Cewar Ummimi cikin sautin kuka. “Habeebi please ka tsaya ka saurareta kaji please” Fannah tayi maganar tana k’ok’arin tsayar dashi amman sam yak’i saurarenta. Murfin motan ya bud’e mata “get in!”
   “No Habeebi I’m not getting in, taya zaka bar mahaifiyarka haka?”
    “Fannah kinga banason abinda ze had’ani dake just get in” zata sake magana ya daka mata tsawa “I said get in!” Shi da kansa yasata cikin motar sannan ya zagaya ya shiga shima ya kunna motar. Ta window Fannah ke kallon Ummimi dake kuka sosai tana bin motar nasu da kallo amman Anas kota kanta beyi ba.

  ** Some hours later...
     Zaune Anas ke akan wresting chair yayi shiru, tun dawowansu bema Fannah magana ba itama haka bata huce da masifan daya mata ba d’azu ba, zaune take kan gado tana kallon sa a nitse ta miqe taje ta samesa tana tsaye akansa amman ko kewayowa ya kalleta beyi ba. “Habeebi” ta kira sunansa tare da zama kan cinyansa.
    “Yes Flower” yayi maganar not paying attention to her, hannunsa ta d’aga ta had’a da nata. “Habeebi I’m sorry for crossing you earlier.”
   “Is okay Flower ni yakamata in baki hak’uri for shouting at you I’m sorry kinji?”
    “Ba komai ya wuce muje mu huta.” Kai ya kad’a mata “banajin bacci just go, nap well Baby Hanan” yayi maganar hannunsa kan cikin Fannah.
   “Mesa baraka kwanta ba Habeebi ba haka na sanka ba tunanin Ummimi kake?”
    “I don’t want to talk about her Flower jeki huta.”
   “Habeebi yakamata ka cire son zuciya kayi facing reality, duk abinda Ummimi ta maka kamata yayi kayi hak’uri ka yafe mata, uwa uwa ce yanzu zakaso ace Hanan ta min kalan abinda ka ma Ummimi?”
    “For God’s sake Flower kidena kwatanta Hanan da Ummimi, Allah raba Hanan da halin Ummimi banason maganan ta karki sake d’auko min maganar ta.” Zata sake magana ya katse ta “am I clear?” Badan tanaso ba ta gyad’a masa kai ta sauk’a kan cinyansa ta koma gado ta miqe. Batasan a lokacin da bacci yayi awon gaba da ita ba.

     A hankali ya miqe ya nufa wardrobe tare da ciro wallet nasa family picture’nsu ya bud’e yana kallon fuskar Ummimi. “Why do you have to show up Ummimi? Why? Bayan duk mun mance dake munyi moving on mesa zaki dawo ki sake hargitsa mana rayuwa as you did before, why? Mesa bakida tausayi ne?” Ganin bayida amsoshi ga wannan tambayoyi ya haye gadon ya kwanta a gefen Fannah tare da kwantar da ita jikinsa hannunsa na akan cikinta.

   “Hanan in shaa Allah baraki d’au halin Ummimi ba, baraki ma yaranki abinda Ummimi tama Daddy’nki ba.” Daidai nan Hanan dake ciki tayi kicking take Fannah ta tashi “Habeebi Hanan ta motsa yanzu” murmushi ya k’irk’iro mata “yes Flower nima naji” hannunsu duka suka kai kan cikin nan Hanan tasake motsawa. Dad’i kamar ya cinyesu both suna feeling baby Hanan insu.

    **
     _Washegari 1:30PM_
   Anas na tsaye a gaban mirror a bathroom fuskansa shaving cream ne da alama shaving zeyi danko riqe yake da shaving stick a hannu amman sam ya kasa yi, gabad’aya hankalinsa bayya a jikinsa ko bacci yakasa jiya se tunanin Ummimi yake, duk yadda yasan ze iyabi dan hana tunaninta yayi amman ya kasa the more yana hana kansa the more yake tunanin nata, Fannah ma takasa bacci ta zauna awake with him ko kad’an bayason maganan Ummimi koda Fannah ta taso da maganar masifa yake mata sosai wanda shima ba a son ransa yakeyi ba, he just can’t take it.

    Ya zurfafa cikin tunaninsa next abinda yaji shine hannun Fannah akan nasa tana amsar shaving stick d’in kwata kwata besan lokacin da ta shigo ba. Sanye take dawani silky dogon riga me spaghetti hands. “Habeebi take it easy please banason ina ganinka cikin damuwa.” Juyo da fuskarsa tayi ta soma yimasa shaving d’in lightly kamar yadda take ganin yanayi. Bece mata komai ba har seda ta gama masa ta wanke mai fuskar tare da share ruwan da towel. Kallon kansa yayi a mirron, sosai shaving d’in yamasa kyau saboda bata kwashe gashin duka ba, tabar sajen da kuma beard nasa wanda suka had’e kad’an very light irin na larabawan nan sosai yayi kyau.
   “Flower kin ma fini iya shaving d’in ban tab’a leveling haka ba” yayi maganar yana shafa kan gashin fuskar nasan. “Thank you sweetheart.”
   “No big deal Habeebi” Hannayenta ya had’a gu d’aya tare da pecking nasu, “Flower ko baki fad’a ba nasani you are mad at me saboda abubuwan dana riga miki jiya, I’m sorry kinji? I’m sorry for shouting at you and Hanan”
     “Na sani Abu Hanan you don’t have to be sorry komi ya wuce muje muci abinci amman yau ba anan nakeson chin abinci ba.”

    “Fad’i duk inda ke da Hanan kukeso muje muchi.”
  “A Restaurant Manhattan mukeso” (inda sukaga Ummimi jiya) kai ya girgiza mata “no Flower baramu je chan ba choose any other place amman banda chan.”
    “Ayya Habeebi chan nakeso.”
   “Flower NO! And that stays that bara muje chan ba.” Ba tare da tace komai ba ta k’wace hannayenta daga nasa ta fice zuwa d’akinsu tare da kwanciya kan gado tana jin footsteps nasa ta soma rera kukan qarya.
    “Flower yanzu kuka kike saboda nace bara muje chan ba?” Yayi maganar yana k’ok’arin d’agota. Shuresa ta shiga yi “ka sakeni nikam bana so stop touching me.”
    “Haba Mom Hanan I’m sorry kinji?”
  “Banji ba ni ka sakeni.” Kunnuwansa ya riqe both “Flower I’m sorry kiyi hak’uri.” Da hanzari ta suk’e hannayen nasa “ni bance kabani hak’uri ka ka kaini Restaurant Manhattan kokuma karka sake min ko Hanan magana.”

   “Flower kiyi hak’uri mana ki zab’i wani restor daban.” Banza dashi tayi tare da juya masa baya. “Mom Hanan magana fa nake miki...” Nanma shiru “Mom Hanan” still shiru “toh naji tashi muje Restaurant Manhattan d’in” a ransa yana me addu’an Allah yasa kada su had’u da Ummimi. Cike da ji dad’i ta miqe tare da brushing masa ligjt kiss a lips “thats my Abu Hanan! Lets go” kallonta kawai yake cike da adoration.


© MIEMIEBEE

Share:

18 comments:

  1. ummu amaturrahaman29 September 2016 at 10:04

    muna tare da kai abba allah ya ka basira

    ReplyDelete
  2. sannu da kokari dan allah kayi ading dina a whatsapp group dinka my no.07064465879

    ReplyDelete
  3. allah ya kara basira

    ReplyDelete
  4. tnk our elbow,allah sakada alkhairee, allah barmana kai

    ReplyDelete
  5. Mungode Dan Allah add me a whatsapp ga Numba na 09059350189

    ReplyDelete
  6. Muna go diya da labarinnan maidadi da kike bamu allah ya karamiki lafiya

    ReplyDelete
  7. Muna godiya sosai allah ya karamiki lafiya

    ReplyDelete
  8. Muna godiya sosai Allah ya qara basira

    ReplyDelete
  9. Allah yasaka pls more

    ReplyDelete
  10. Acigaba don allah

    ReplyDelete
  11. ummu amaturrahaman3 October 2016 at 01:39

    allah yasa lafia dan allah kadoramana

    ReplyDelete
  12. tnx we really enjoyed nd appreciate tana tare dani need 91 to and end pls tnx once more

    ReplyDelete
  13. Allah ya saka ya kara basira, pls continue

    ReplyDelete
  14. Allah ya saka ya kara basira, pls continue

    ReplyDelete
  15. muhammad abba gana4 October 2016 at 03:02

    ameen @Rahma ,

    ReplyDelete

pls drop down your comment......
dan Allah ku ajiye comment.

Tallata Kayanka

Guide Tricks Blog

Be With Me Technology

Popular Posts

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).