shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wanda aka fi sani da hausa novel wanda ni Muhammad abba gana nake rubutawa dan wayar tare da fadakarwa ga mutane a yanayin da muke ciki.

Wednesday 7 September 2016

TANA TARE DA NI...1---5

tana-tare-dani.jpg


TANA TARE DA NI... PAGE 01
BY MIEMIEBEE


ANAS
     K’auyen Bama dake jihar Maiduguri, Borno.

            Da yammacin ranan Asabar misalin k’arfe biyar da mintuna aka. Ruwan sama akeyi me ni’iman gaske, ga wani iskan dake hurawa me kad’a bishiyoyi da flawoyi, ko ina ya d’au sanyi. Tsit kukeji a garin, yara da manya, maza da mata kowa na cikin gdajensu, masu tafiya akan hanya kuwa sun faka gu d'aya, motoci dabasu fi a k’irga ba ke wucewa time-to-time. Can k’ark’ashin wata bishiyar ’yim na hango wasu samaruka guda hud’u wanda barasu gaza kuma barasu fi shekaru 17-18 ba.

        Daga nesa nake, amman hakan be hana ni tantance kyakkyawan cikin wad’annan samarukan ba. Wani kyansan ma sanda na gama k’arisowa, fari ne yellow shar da gashi kwance a duk sassan jikin d'an Adam da akasan na tsirar da gashi. Gashin kansa nada yawa saidai bawai afro tayi ba saboda tsantsin gashin bai tsayuwa, luf-luf yake kwance a kansa, bak’i k’irin yana yalk’i wane yasha mai.

      Saje ne kwance akan farar fatar fuskarsa wanda da ace yanada gemu da sun had’e. Gashin girarsa ba a cike take erin thick dinnan ba, silky yake a kwance d’an siriri wane yayi carving nasu. Dogayen eyelashes nasa wanda suke kallon k’asa santsi ne dasu. Bashida dara-daran idanunu, idanun nasa suna nan madaidaci da k’wayoyin idan nasa light blue wane na bature.

          Nasha jin ana cewa a Africans akoi masu blue eyes ban tab’a yarda ba sanda naga wannan saurayi. Hancinsa ma ba dogo har bakan nan bane, daidai yake cikin 'yar fuskarsa wanda yakasance shi ba dogo ba bakuma gajere ba. Bakinsa light red yake d’an madaidaici cikin fuskar tasa. Dukda cewar ya d’aure fuska hakan be hana dimple na kumatun damarsa lotsewa ba wanda babu hakan a na hagun.

   A zaune yake amman hakan be hanani tantace tsawonsa ba, dogon na miji ne, yanada faffad’ar k’irji duk da cewar siriri ne. Ofcourse ana cewa d’an Adam bai cika goma but za’a iya kiran wannan saurayi hallitar data cike goma bansani ba halan ya gaza ta hali amman inde ta hallita ne kam masha Allah, Allah yabasa, ban tsammanin akoi macen da zata ga wannan saurayi bata kuma kallonsa ba. I mean ba mace kad’ai bama kowa in all.

      Sanye yake da mint blue T shirt wanda ya mugun amsar farar fatarsa, jeans na jikinsa kuwa tad’an kod’e alaman tasha ruwa. Rik’e yake da kara a hannunsa yana wasa dashi da siraran yatsunsa wanda suke nan kan ba na miji ba.

      Gefensa saurayi ne me kama da shi sak, saidai komi na wannan kyakkyawan yafi nasa, kuma shid’in be kai kyakkywan fari da k’war jini ba, duk yadda akayi wansa ne na jini saidai na kasa tantance wane babba cikinsu. Sauran biyun k’arshen kuwa chocolate skinned suke, saidai still d’aya yafi d’aya haske.

     “ANAS na mata kenan!” Cewar d’an bak’i na k’arshen tare da kewayo da kallonsa kan kyakkyawan cikin nasun wanda nake da tabbacin shine ANAS d’in yana mai murmushi wanda hakan ya bayyano da brown teeth nasa, tabbacin kanuri ne shi kenan. “Uhm uhm fa BAANA!” cewar me haske na gefen d’an bak’in da yayi magana yanzun kenan. BAANA yace, “ah’ah barni in tsokanosa de.” Shide kyakkywan nasu da ake kira da ANAS be tanka saba, hasali, yi ma yayi kamar besan ana magana a gefensa ba se b’antare karan dake hannunsa yakeyi yana kallon yadda ruwan saman ke sauk’owa.

        Wanda nake kyautata zaton wan Anas d’in ne yace da d’an bak’in gefen nasa “barsa de KASHIM, neman magana yake yau gun ANAS.” KASHIM ya karkato da kallonsa kan BAANA “aikam naga alama rad’au a fuskarka, kuma wallahi kasan inya shak’ure ka bame k’wato ka, kasan halin mazan namu. Ko mata ma bai ragar masu ba bale kai,” ya d’an yi shiru sannan ya k’arisa “gardi” Yafad'a cike da gatsine.

     BAANA yace, “hummm zagen dai, naga kap nan gardawa ne har Shettima k’anin mun ma(k’anin Anas knan)” Duk suka k’yalk’yale da dariya illa shi wannan kyakkywa da suke kira da Anas wanda yayi burning face sekace besan me kalmar dariya ba.

        Niko miemie na matsu injiyo muryan wannan kyakkyawan da suke kira da Anas. Yawancin anacewa wanda yafiye kyan fuska bai fiye zaqin murya ba kuma hakan ne sanda na jiyo muryan Anas na k’aryata wannan batu.

        “You see, ruwan nan na tsayawa barama kuganni anan ba to talk more of kumin tsiya mtschww.” Cewar Anas tare da watso musu harara sekace mace.

      Lallai! Allah yayi murya anan, muryar Anas sautin na miji ne da anji amman saidai ba tattausar murya bace, zaqi ce ga me sauroro, bakuma zaqi erin ta mata ba saboda yadda muryar ke cracking a hankali in yana magana.

       “Toh Anas meyayi zafi daga fad’in gaskiya? Ai gaskiya ce wallahi kap ‘yan matan garin nan basu san wani na miji sekai, narasa menene kake dashi bamuda, ni da bansanka bama se ince asircesu kayi.” Cewar Baana yana nuna yadda abin ke damunsa.

      “Ahhh lallai Baana ka soma zarewa” cewar Kashim cike da mamaki. “Yanzu har seka tambayi ko mesa matan garin nan basu kula kowa se Anas? Bakada ido ne?” Shettima ya karb’esa “gaskia da alama.” Kashim ya cigaba, “k’warank’wasa ace yau ni mace ce nima sena so Anas wanga blue eyes sekace bature, ko ka manta teacher'n English namu da ke sansa.” Suka sake sheqewa da dariya at once kuma sukayi shiru suna jiran tsiwar Anas to thier suprise be ce masu ko uffan ba miqewa yayi da niyar tafiya dukda cewar ruwa akeyi fuskarsa a tamqe kwata kwata abin be basa dariya ba.

        “Haba maza yi hak’uri mana karka fad’a min cikin ruwan nan zaka tafi!” Cewar Shettima wansa tare da rik’o shirt na Anas. Harara Anas ya galla masa da nufin ya sake masa kaya, kafin ace me k’arfin ruwan saman ya dad’a k’aruwa ba yadda ya iya dole ya koma ya zauna. “Wai zanso inga Anas yayi aure wataran, muga ya zena controlling wannan uban temper'n nasa da matarsa.” Cewar Baana. Take Shettima ya juya ya kallesa tare da zaro masa ido yana me masa warning.

         Dukda cewar Anas be tanka sa ba amman fuakarsa takoma ja alokaci d’aya ya had’e girarsa gu d’aya kallo d’aya za’a masa asan ransa ya b’aci ko dan meh oho? Kodan kiran kalmar ‘aure’ da abokin nasa yayi ne?

      Cikin tsiwa yake maganar ba alamar walwala a tattare dashi. “Baana don't push it, nasha fad’a maka time without number bana san kana min maganan aure ko kuma ‘yan mata in muna tare, that goes to both of you” ya nuna Kashim da Shettima. “Banaso! Banaso! Inhar kuna sona yaci ace kundena for goodness sake!” Shettima ya dafe kafad’arsa “toh maza we are sorry.” kallonsa yayi ba tare da yace masa komi ba sannan ya kau da kai. Baana ya numfasa sannan yace, “toh ka fad’a mana why mana, kullum se kace bakasan kalmar aure ko budurwa amman baka tab’a gaya mana mesa ba, as friends we have to know ko bahaka ba Kashim?”

      Kashim ya giad’a kai “sosai mah kayi gaskiya.” Shettima kuwa dayasan mesa wan nasa bayasan wannan kalmomi guda biyu kawai ya kad’a kansa cike da nadama, yayi yayi ya ganar da d’an uwansa gaskia yakuma sa ya yafe wa mahaifiyar su amman ina abin ya gagara sam saboda abinda tayi ta sa Anas ya kariya, zuciyarsa a toshe take da bak'ar kiyayya is hardly aga Anas yana dariya, murmushin ma se in abu yakai ya kawo ne yakeyi.

      “I can't tell you guys, I'm sorry saboda talking about it makes me sick kawai ni kudena tareraya ta da wannan magana banaso give me a break please.” Baana ze sake magana Shettima ya dakatar dashi ta aza yatsa kan lips nasa. In akoi abinda yafi damun wannan abokai guda biyu, (Baana da Kashim) befi wannan halin abokin nasu ba, ace da an kira kalmar aure se mutum ya b'ata rai, aure da ta kasance sunnah me k’arfi wanda kowani d’an Adam keda burin cikata. Gaskiya da abun duba.

     Kashim yakasa hakura shikam sanda ya kuma tambaya “Anas munsan baka san maganan nan amman ka dage ka fad’a mana, who knows! we might be of help.”

     Juyowa Anas yayi ya kalle sa tare da wata murmushin takaici ta gefen lips nasa wanda a sakamakon hakan ya bayyano da fararan hak’waransa da suke kamar an daidaita tsawonsu “help? Hmmm, k’arshen k’ok’arin da zaku iyayi shine ku dawo da ita kuma koda kunyi hakan ma barinyi appreciating ba saboda tafita a raina, bana san sake sata cikin idanu na, ta cuceni ta cuci two siblings d’ina Shettima da Amal, and most of all ta cuci Abuu (mahaifinsu). I don't want her ever in my life.”

      Cike da mamaki Baana yace, “subhanallah wa kenan?” “Bade mahaifiyarku ba?” Kashim ya tambaya. Anas bece dasu komai ba Shettima ne ya giad’a masu kai da nufin eh mahaifiyar su Anas ke nufi. “Subhanallah! Subhanallah! Anas be kamata kana maganar mahaifiyar ka da ta kawo ka duniya haka ba, uwa uwa ce. Kome tayi maka ka tuna ita ta kawo ka duniyah.”

   “Thats my point!” Anas ya fad’a a masifanche. “Ita ta haifeni, ita ta kawo ni duniyah abin dayafi ban haushi fiye da komai kenan. Taya matar da ta kawo ni duniyah zata tafi ta bi wani na mijin daban ta bar family’nta a baya, How? Why? Mesa mata basuda tausayi? Mesa Allah yayi su mugaye masu san kai da abin duniyah mesa? Mesa basuda Imani? Mesa tayi breaking heart na Abuu haka? Har yau yakasa trusting wata ‘ya mace a duniya. Why does it have to be this way? Why? Mstchww!” yaja tsaki cike da haushi.

       “We are sorry” Kashim yafad'a cike da tausayi, so wannan grudge d’in Anas ke holding a zuciyarsa har yanzu saboda abinda mahaifiyarsa da Shettima tayi musu. Yau shekaru kusan bakwai kenan da sanin junansu amman be tab’a sanin mesa Anas ke cikin k’unci ba, kullum ba walwala a tattare dashi se yau. Tun ba yau ba yakeson jin me tarihin Anas amman Anas ko kad’an baisan maganar haka zalika ya hana wansa Shettima fad’a ma kowa. Yau d’inma halan saboda sun tak’ura masa ne yasa ya fad’a.

         Tun da suke a secondary school haka Anas yake, ko erin secondary school dating da akeyi d’innan Anas be tab’ayi ba hasali betab’a showing koda slightest interest akai ba ma. Unlike his brother Shettima daya d’au komi as k’addara yake living life nasa peacefully cikin walwala da dariya.

       Tunanin ya zeyi ya karkato da hankalin friend nasan kan gaskiya yake. Gyaran murya yayi sannan a hankalche yace “Anas we are all here for you, we are like brothers yanzu. Nasan how hard this must be for you amman dole kayi haquri ka rungumi qaddara kamar yadda Shettima yayi.”

       “No Kashim, I can’t baran iya ba. Karka had’ani da Shettima, Shettima was a small kid back then time da abin yafaru, definately ya manta komai bare iya tuna koda abu ba, but me? Da wayona da komai na wannan matar ta tattara kayakinta, we were all begging on our knees muna roqarta karta tafi... Mschww I don't want to talk about it banasan ciwon kai, you two have heard enough.” Anas ya fad’a tare da miqewa daga mazauninsa. “Finally ruwan ya tsaya” yayi qoqari canza topic d’in, yana miqa wanda a sakamakon haka joints na jikinsa suke sakar k’ara. “Shettima lets get going, yakamata mud’an taya Ummee da aiki kafin Maghrib yayi” (Ummee; k’anwar mahaifinsu wacce takasance tamkar uwa a garesu tunda mahaifiyarsu ta tafi ta barsu take kula dasu).

        Shettima ya mik'e shima suka d’anyi manly shake da juna, “alright! Se mun had’u a masjid” Anas yace da Baana da Kashim da suke zaune har yanzu sannan ya juya shida Shettima suka soma tafiya.

     “Huh!” Kashim ya numfasa, “ina tausaya wa abokin nan namu, like sosai. Zuciyarsa ta riga ta toshe da tsantsan k’iyayya.”  “Sosai fa Kashim, but tsaya kaga wani abu yanzun nan ze dawo” cewar Baana yana murmushin jin dad’i. “Bade ya manta blessing d’inba?” (Yaren da masu shaye shaye ke amfani dashi wajen kiran ‘wiwi’). Baana yace, “Yup!” Tare da d’aga girarsa sama yana murmushi.

© miemiebee

TANA TARE DA NI... PAGE 02
BY MIEMIEBEE


Tafiya suke a sahu d’aya, tsayin nan nasu na nan d'ai da kad’an Anas ya d’ara Shettima inba wai ance ya da k’ani bane za’a zata agemates ne. Daidai lokacin da suka yanko wata corner kenan Anas yasa hannu a aljihu yaji wayam ba komai, cak ya tsaya hakan yasa Shettima tsayawa shima. “Ya maza lafiya?” “Ba lafiya ba, go ahead I'll catch up nayi mantuwa.” cewar Anas. Shettima ya tsaya ya k’are ma d’an uwan nasa kallo sannan yace, “bade blessing d’in ba.”

      Anas ya kallesa da gira d’aya d’age sannan yace, “toh meh? Kadega yadda su Kashim suka sani tono maganan chan definately nasan ciwon kai ze kamani and despite that, yadda akayi ruwan saman nan I'm gonna enjoy sleeping.” tare da d’anyin murmushi wanda ya sake bayyano da kyansa tare da lotsar da dimple nasa dake kumatun dama. “Kona yau baraka hak’ura ba?” Shettima yasake tambaya. “Se in na amso karka sha” cewar Anas.

       Dariya kad’an Shettima yayi “zan d’an tab’a mana, naji ance da akoi dad’i cikin tea.” Anas ya dafe kafad’arsa “lets go?” Da d’aga kan da Shettima yayi suka juya suka dawo gun Kashim da Baana. Suna iso wurin nasu, Anas yace, “maza bani!” Baana yaci fuska “ban gane baka ba, mezan baka?”  “Wai me ka maidani ne? Give me!” Anas ya fad’a a little bit pissed. Dariya Kashim yayi “basa please kaga har yafara losing temper.”

     Nan Baana yasa hannu a aljihu yaciro wata leda ya raba into two saidai d’aya yafi d’aya yawa sannan ya mik’a wa Anas kad’an din. “Are you serious? Naga fa wannan abu ni nasaya da kud’ina so kabani me yawan ko in hanaka duka.” Baana yace, “haba! Anas namu na kanmu, kap qauyen nan fa kai kad’aine me blue eyes yi hakuri mana. Aikasan da inada kud’i dana siya nima.”  “Toh ni na hanaka yin noma ka samu kud’i? Abeg give me and stop wasting my time.”  “Dan Allah fa nace” Baana yafad’a pleadingly. “Okay naji talaka kawai semun had’u a masjid then.”

      Daidai sunkai ga shiga corner'n gdansu kenan wata budurwa tafito daga wani gida, sanye take da hijabi iya guiwarta, dududu barata fi shekaru 15-16 ba. Idanunta suna sauk’a kan Anas ta sakar dawata murmushi. Tsuka Anas yaja yasa qaninsa a gaba yana tunkud’esa dan suyi sauri subar gun shiko Shettima daya gano haka tuni ya rage saurin tafiyarsa dukda tunkud’in da Anas kemasa.

     Se k’arisowa wajen nasu wannan budurwa ke. “Anas kamar kayi bak’uwa ko? Wannan ba Aisha bace? Ka tsaya kaji me zatace mana.” Cewar Shettima yana murmushi. “Wallahi in bakayi shiru ba zan mareka, kuma barakayi tafiya bane?” Daya wani tunkud’a gaba Shettima besan sanda yasoma matching dasauri sauri suka bar wurin ba.

     Isarsu gidah keda wuya suka tarar da Ummee a tsakar gidah tana tsince shinkafa. Da sallama suka shiga ta amsa da fara'arta. ‘yar dattijuwa ce wacce barata fi shekaru 45 a duniya ba, tanada haske sosai amman bara’a kirata da fara ba, ga kyau daidan gwargwado masha Allah!. “Ohhh mazan nawa sun iso ne? Sekuma ruwa ya tareku a hanya ko?”  “Eh Ummee” cewar Anas yana k’arisowa wajen da take. “Me kikeyi haka?”

     “Tsince nake baba na, tuwon shinkafa Abuu keson ci gashi har ruwan ya tafasa ban gama ba.”  “Toh Amal fa mesa bata tayaki ba? Anyways kawo in tayaki Ummee.”  “Kai Baba na kaide Allah shi maka albarka” ta d'ago kai tana kallon Shettima dayayi kamar besan ma me suke fad’i ba. “Kai yanzu Shettima koda aiki ze taru ya kasheni ba ruwanka da bari ka tayani ko? Baka ganin wanka ne?”

    “Toh Ummee fisbailillahi ina aka san maza da tsintar shinkafa.” Baki wangalau ta bud’e tana kallon Shettima dududu shekarunsa sha shida ne fa da abu aka yake wannan tsiyar bayan ga wansa Anas me shekaru sha takwas bece komi ba. “Ehh hakane, sannu fa” tafad’i cike da gatsine. “Oyoyo Ya Anas” cewar wata kyakkyawar yarinyar da baratafi 8years ba fitowarta daga wata d’aki, ba shakka itace sistersu da suke kira da Amal, kyakkyawace sosai kamar sauran yayun nata bata gama kai Anas fari ba amman tafi Shettima. Su uku kap kamanninsu d’aya.

          (Bayan tafiyar mahaifiyarsu daga gdansu da wata takwas ta turo da Amal da wasiqa na cewa tabar gidan da cikin Amal ga ’yarsu nan ta haifota, kwanan ta d’aya a duniya kenan) sanadin haka Anas yake mutuwar san Amal duk rashin kunyarta bata masa saboda duk fitar da zeyi seya siyo mata abun k’walama unlike Shettima da cikinsa kawai ya sani thats the reason why basu shiri da Amal kullum cikin fad’a sukeyi duk sanda Anas yazo kuma seya bata gaskiya, wani sa’in har taran dangi suke masa.

     “Oyoyo my angel” yafad’i tare da bud’e hannunsa tazo da gudu tayi hugging nasa. “Ina sweet d’ina ya Anas?” kafin ya amsa mata ta zira hannu cikin aljuhunsa taciro ’ya’yan wiwin da Anas ya amso gun Baana sekuwa idan Ummee yakai kai. “Baba na meh wannan!?” Ta tambaya tare da zaro idanu waje. Nanfa Anas yasoma kame-kame can yace, “laaa Shettima kalli wannan abin da abokin Baanan can yace na rik’e masa” yama Shettima ido. Shettima yace, “ohh yamanta be karb’a ba kenan?”

      “Gashi anan kuwa!” Cewar Anas. “Anyways meh abun nema?” ya amshi daga hannun Amal. Ummee tace, “maza ka mayar masa wannan abu shaye shaye akeyi dashi, mayar masa maza!”  “Toh Ummee amman bansan ina gdansu ke ba, agidansu Baana muka had’u.”  “Nide koma me ka mayar masa.”  “Toh Ummee bari in muka fita Maghrib zan bawa Baana ya mayar masa.” Anas yafad’i a hankali
“Toh” tace tare da numfasa. “Ya Anas to ina sweet d’ina toh?” Cewar Amal.

      “Angel bansamu na saya miki ba, shops d’in duka a rufe I promise gobe kinji?” A hankali ta giad’a kai tare da turo baki. “Tsaya kiji wani batu” nan ya daidaita tsawonsa yakamo nata tare da rad’a mata wata magana a kunne aikuwa tahau tsalle suna ido hud’u da Shettima ta galla masa harara. “Wallahi Amal niba sa’anki bane wa kke harara? Maras kunya kawai.” Kafin Ummee ta masa magana Anas yace “ah’ah karka zagarmin k’anwa now go inside okay? Anyi ruwa kar mura ya kama ki.” Tana tsalle takoma ciki.

     Ba tare da b’ata lokaci ba Anas yataya Ummee suka gama tsince shinkafar banda Shettima daya tsaya kansu yana kallonsu cike da mamaki yarasa meke burge Anas a aikin kitchen bama aikin kitchen kad’ai ba. Bayasan ganin abinda ze tab’a Ummee ko Amal, he is so protective of them, duk abinda zeyi zeyi inhar it will keep them save and happy.

   *****

        Bayan sunfito daga masallaci iyayensu sukayi gaba a yayinda Shettima, Anas, Baana da Kashim suke tafiya a bayansu suna tattauna warsu ta maza. Wata budurwa ce ta b’ullo gabansu, dakatar dasu. “Ina wuni?” ta gaishesu duk suka amsa illah Anas dake neman any chance yabar wajen. “Anas ina wuni?” tasake fad’i cikin wata anniyar murya ganin shine be amsa ba. Shiru yamata, “Shettima ko nama Anas wani abu ne baimin magana?”

      Murmushi k’adan Shettima yayi sannan yayi k’arya “ko kad’an Hafsah mura yake saisa bai iya magana.” Wani kallo Anasa ya watsa masa wanda shi Shettima yamayar da murmushi. Kafin yace wani abu Hafsah tace, “dama zuwa nayi na tayaka murna ne kan scholarahip daka samu cewa nanda ‘yan kwanaki zaka London shine na had’o ma wannan pepper soup sekuma gashi kana mura I'm sure ze d’an wassakar maka da muran ma. Gashi please ka amshi”

        Ganin Anas baida niyan karb’a Shettima yasa hannu ya amsa “kai sannu Hafsah kamar kinsan mura na damunsa kika kawo wannan.” Shettima ka tabatta Anas yasha please ze taimaka masa sosai.”  “Aii karki damu” cewar Kashim “consider it done, zamu tabbata yasha.”

      Da murmushi a fuskarta tace, “toh nagode seda safenku.” Sanda ta sake kallon Anas sannan ta fice. Nan Anas ya finciko Shettima tare da kama masa kunne ya murd’a da iya k’arfin da Allah ya basa. “Awchhhh!” Shettima ya sakar da k’ara. Karb’e kulan abincin Anas yayi ya soma tafiya. Baana yace, “ya haka kuma? Nad’au ai baraka ci ba.” Duk suka k’yalk’yale da dariya. Bece dasu komi ba yacigaba da tafiya, “anji kunya” cewar Shettima nan ma be tankasu ba. Yana isa gida ya tarar da Ummee tana ‘yan wanke-wanke kafin ya b’oye flask d’in har ta riga ta gani.

       “Baba na me wancan kake k’ok’arin b’oyewa?” Cewar Ummee da murmushi fal a fuskarta. “Oh wannan!” Ya d’ago flask d’in sama “erm... Erm... Na-”

      “Iyye baba na manya har ‘yan matan naka sun soma kawo maka abinci ne, to yayi kyau. Me aciki?”

    Kamar ya mata k’arya sekuma ya fasa, “pepper soup ne nakawo wa Amal ko kema zaki tab’a?”  “Noo haba! Budurwa takawo wa Baba na kaji kuma se inci je kaci abinka.”  “Kai Ummee da Allah bafa budurwata bace.”  “Hehe!” tayi dariya sosai “yanzu uwar taka kake jin kunya?”  Rashin sanin me zece mata yasa ya wuce ta kawai ya kira Amal suka wuce d’akinsu ya bud’e masu suka sha pepper soup nasu. Ni miemie nace Anas ba kunya yanzu sha yake!? Lol

       Sun ci kusan rabin kazan Shettima yashigo senishi yake da alama gudu yayi ya iso nan. “Yanzu Anas cinye kazan nan zakayi da wannan maras kunyan baraka d’an bani ba nima?”  “Eh bara'a bayar ba” cewar Amal “Ya Shettiman nan shegen kwad’ayi wallahi ko Ya Anas?” Ta sake p’antarar kazar ta kai baki. “Sosai ma Angel” Anas ya amsata. “Wallahi Amal ki kiyaye ni” gwalo ta masa sanin in Anas na gefe da ita ba abinda Shettima ya isa ya mata.

          “Ka kwantar da hankalinka bari mu fita sallan Isha har gidansu Hafsah zanje in fad’a mata ka cinye kazan kap ko k’ashi baka bari ba.” Murmushi kad’an Anas yayi “to ai ko ka fad’a mata ba yadda zatayi ba saboda ban bata fuska ba.” Haka ya dake sanda suka cinye kazan tas shida Amal, pippike da wuya suka ragar sannan Anas ya ceda Amal ta mik’a ma Shettima da yawunsa ke d’iga k’asa.

      Itako ta d’aga ta ajiye mai “gashi Ya Shettima.” Hannunta ya rik’e tare da danna mata nank’washi aiko tasaki kuka harda na munafirci take Anas ya k’ariso ya rama mata.

     ***

     Haka ma da suka dawo sallan Isha Aishar d’azu ta tsaresu tare da masu sallama kap suka amsa illa Anas. Sak batun da Hafsah tayi haka Aisha ma tayi sede nata chips da omalet ne, itama na taya Anas murnan samun scholarship da yayi. Anas na jiran Shettima ya amsa kamar na d’azu aikuwa yak’i. “Dan Allah kayi hak’uri ka karb’i Anas ni badan kasoni na kawo ma ka ba, consider it as a friendship gift please.”

      D’ago blue eyes nasa yayi ya kalleta ciki ciki wanda tuni ta soma shaking tare da kawar da kanta. Ajiye flask d’in tayi a k’asa “dan Allah ka d’auka se da safenku.” Aiko tana shigewa cikin gdansu ba kunya Anas ya d’aga yakama tafiya. Baana yace “andeji kunya” haka suka ta masa tsiya amman ko a kolan rigarsa, duk yasan so suke suci kuma bayarwan ne bareyi ba. Nanma dashi da Amal ne suka cinye wannan karan ko ragowar ma ba’a baiwa Shettima ba.

    **

        Da misalin k’arfe goman dare bayan kowa ya kwanta a gdan. Anas da Shettima suna kwance kan seperate gadonsu bayan sun gama shan wiwinsu cikin tea. Shettima daya zura wa Anas kallo na kusan mintuna yace, “tunanin me kake haka?”

      “Anas?” Nanne ya dawo hankalinsa “yes! kace me?” Shettima ya kuma nanata kansa “nace tunanin me kake?”

     Murmushi sosai Anas yayi wanda yasa dimple nasa lotsewa sosai, kad’an daga cikin fararen hakwaransa suka bayyano. “My dreams are about coming true.”  “Wani dream kenan?” Shettima ya tambaya tare da tasowa ya zauna kan gadonsa tare da jingina bayansa a jikin kan gadon.

      “Don't tell me bakasan dreams d’ina ba! Ofcourse to be a billonaire se in samu inyi breaking hearts na thousand of women by then kaga na ramawa Abuu abinda mamarku ta masa.”

    “Wai wace erin magana kakeyi Anas? Wai yanzu kana ganin in Abuu yaji wad’annan munanan kalamu daga bakinka zeji dad’i? Haba mana kai baka yafiya ne?”

      “Yafiya! Har yau bansami defination na word d’in a dictionary ba plus in wa’azi kakeson yi kaje masallaci kayi, kagannin nan? Banasan jin wannan wa'azi allow me to get some sleep yadda nasha ’ya’yan wiwin nan.” Nan yaja bargo tare da rufe kansa ciki a hankali bacci me nauyi ya daukesa.

© miemiebee

 TANA TARE DA NI...

TANA TARE DA NI... PAGE 03
BY MIEMIEBEE


FANNAH

      ‘kauyen Bama dake jihar Maiduguri, Borno.

       Kyakkyawar budurwa ce zaune cikin wata ‘yar k’aramar d’aki bisa gaban wata ‘yar madubin da aka mak’ala a jikin bango. Ba komai bane a d’akin illa katifan dake shimfid’e a k’asa seda bakunan sa kaya da leather carpet ciki. Ba shakka basu da arziki. Dududu wannan ‘yar budurwa baratafi 15 years old ba. Tanada haske sosai, da sirirn hanci dakuma plumpy lips, idanunta ba laifi ‘yan manya ne dadai. Gashin girarta acike yake mekyawun gaske ba ruwanta da zana artificial gira [ba erinsu ni ba;( ] in kuwa aka k’are mata kallo sosai za’a ga alamar had’ewar girar ta guda biyu gu d’aya sede be munanta taba hasali kyau ma yak’ara mata. Gashin idanunta a cike suke kuma dogaye, saje ne a fuskarta kwance luf-luf wane na miji (kaman nawa, lol) gashin kanta dana girarta sun had’e dan yawansu. Hannunta gashi ne a kwance dogaye masu mugun kyau.

           Siririya ce de tanada tsawo daidan shekarunta, tana sanye da wata atamfa maroon da torches na white and green, se murza wata ‘yar jan baki pink take a lips nata hankalinta kwance da anganta ansan batada matsala. A lokacin da wayarta k’irar Nokia Asha dake kan cinyarta tayi k‘ara, a hanzarce ta duba tana ganin sunan daya bayyana kai Ya Ahmad tayi murmushin jin dad’i sannan ta bud’o sakon ta karanta kamar haka;

    my Fannah I'm outside waiting for you yanzu shigowa na gari ko gida ban lek’a ba just wanted to see you
            “yeyy!!” Ta fad’a a fili tana murna. Data gama sa jan bakin ta shafa powder tareda sa kwalli a fararen idanunta take ta dawo wata balarabiya. A garin mike’wa d’an kwalinta ya since ya fad’i k’asa tare da ribbons data k’ukk’ula gashin nata dashi. Fans ko kunsan ya gashin buzayen Maiduguri yake? Erin bak’i k’irin me santsi da tsawo kamar haukan nan? Haka gashin wannan ‘yar budurwa yake.

     Ni kaina miemie dana gani sanda na tsorata dukda cewar ita kad’ai ce a d’akin hakan be hanata yin saurin tattara ribbons d’in gu d’aya da sauri ba tasoma k’ok’arin faka gashin nata gu d’aya saidai dan cikar gashin ta kasa, hannun nata suna nan sirara ba fad’i ga uwa uba gashi har tsakiyar bayanta. Kamar wacce zatayi kuka tafito d’akin “Mami! Mami!” Shiru kukeji wani mutum ne wanda bara’a kirasa da dattijo ba danko befi shekaru irin 44-45 dinnan ba ya lek’o daga wata d’aki wanda ya kasance opposite daga d’akin da Fannah tafito da alama mahaifinta ne dukda cewar basu kama kuwa. “Fannah uwata ya akayi? Tsaya mesa kike yawo da kanki a bud’e haka?”

     Kamar wacce zatayi kuka tace, “Baba ribbon d’in ne yafita kuma nakasa d’aure gashin, Mami nake nema ta tayani.”
         “Shine zakiyi kuka uwata?” Cewar mahaifin nata “Mami batanan tashiga mak’ota.”
          “To baba Ya Ahmad fa yazo yana jirana a waje ko gida be wuce ba ya zosa nan.”

      “Oh! Keda Ahmad d’inkin nan se Allah. Ina Afrah da Aiman toh?”
         “Sun tafi islamiya Baba.”
     “Yoh! Kekuma fah?”

         “Kai Baba wai yanzu so kake kace ka manta sauk’an nawa? Abinda har Hajji kaje da kujerar da aka bani danayi na biyu.”  “Haka fah, taho to in kama miki kan.”
         “ Yawwa Baba na.” Da gudu taje ta zauna gabansa shima sanda yayi dagaske sannan ya kama uban gashin nata gu d’aya. Banda tsawon gashin gu d’aya. Wawan cika ne dashi saisa Fannah batta iya kamawa. “Toh nagode Baba.”  “Yawwa ‘yar akbarka se ganin Ahmad ko?” Ta giad’a masa kai. “Ki sa hijabi fa tukun kuma kice ya gaishe min da mahaifinsa naji wai ya d’anyi rashin lafiya kwana biyu kuma ban samu na lek’a sa ba.”  “Toh Baba zan fad’a masa in shaa Allah.”

      D’akinta takoma tad’au wata maroon hijabi wanda ya sake ciro da hasken ta tasa, tare da d’aukar wayarta sannan tafito waje idanunta suna sauk’a kan Ahmad nata ta sakar dawata murmushin jin dad’i. Ahmad saurayi ne me k’imanin shekaru 23. Chocolate skinned yake, yana da kyau dadai gwargwado gasan murmushi. Tsayyayen na miji ne masha Allah!

     “Ga sarauniyata ta fito.” Ya fad’a yana mai murmushi. “Gaskiya wankan nan yayi kyau sosai Fannah, kin ganki kuwa? Looking so take away.”
           “Ya Ahmad kaide kullum seka riga zolayata. Ina wuni? Ya hanya? Gashi ko ruwa ban samu na d’auko maka ba duk na k’osa in ganka.”
          “Laaa ai sarauniyata bata laifi ae, karki damu ni ganinki kad’ai ya kashe min k’ishi.” Hannu tasa ta tare fuskarta a kunyance. “To ya Ahmad mu zauna anan mana kar ka kaji a tsaye.” ta nuna wat benchi.
        “Haka sarauniyar tawa tace? “Haka to za'ayi.” Bayan sun zauna Fannah tace, “ya hanya toh? Ya makarantar?” Hannu yasa ya dafe goshi sannan yace, “so hectic fa Queen, biochemistry akoi wahala. Ga Maiduguri zafi like hell”

       “In shaa Allah ka kusa gamawa, Allah baka sa’a yaya na.”  “Ameen sarauniyata.” Kefa ya school ‘yan matan ss2 koh?”
          “Kai yaya! School alhamdulillah” Ta fad’a tana murmushi. Hira suka d’an tab’a na ‘yan mintuna. Shi Ahmad ba abinda yake sake jan ransa kan Fannah kamar san addininta dakuma yawan yarintar ta dakuma sa sa dariya da takeyi in suna tare. Fannah batta magana d’aya biyu seta sa alhamdulillah, subhanallah, masha Allah ko jazakallahu bikhair ciki. Yarinyace me tarbiyan gaske, ga hankali da girmama na gaba da ita koda wasa bata tab’a kiransa da sunansa gatsau ba dole seta sa yayan nan kuma bawai they are related bane tsantsan girmamawa ne kawai.

     “Toh yaya na kar na ta jan ka da surutu nasan su Mama duk suna jiran ganinka, kaje gida ka huta.”
            “Toh sarauniyata” hannu yasa cikin jakarsa yaciro wata leather sannan ya mik’a mata.
       “Me wannan kuma yaya na?” ta tambaya suprisingly.
        “ ‘yar tsarabar Maiduguri ne nace barin kawo wa sarauniyata, yi hak’uri ba wani abu me tsada bane.”
         “Yanzu yaya karatu kakeyi amman seka rik’a kashe kud’inka a kaina? Ni gaskia kadena banso nafison kana kula da kanka a school.”
       “Ko kad’an Fannah baran iya zuwa nan ba tare da na kawo miki komi ba. I prmise you this duk sanda na fara earning salary’n kaina I will spend it on you, ina sonki sosai Fannah ta.”
             “Nima ina sonka yaya na. Nagode sosai, jazakalllahu bikhair Allah taimaka ya baka sa’a yaya.” nan ta mik’e.

     Mik’ewan yayi shima “ameen my Fannah inasan addu’o’in ki agareni, ba k’aramin taimaka min suke ba.”
         Ai saisa kullum nake including d’inka cikin prayers d’ina. Baba na naka sannu dazuwa also, yace ka mim’a gaisuwan sa gun Abba da jiki”
          Toh my Fannah, I'll tell him so se munyi waya ko?” kai ta giad’a a hankali. Wai! Ai na manta kun kusa fara exams ma, barinso jn hana Queen d’ina karatu ba”
        “Haba mana yaya ko wayan minti ishirin baramuyi ba?”
     Da murmushi a fuskarsa yace ai baki tab’a neman abu kirasa guna. Allah kaimu daren toh”
     “Yawwa yaya bo-bye” tamasa murmushi. Murmushin ya mayar mata “bo-bye Queen.” Ahaka tashigo ciki.

      Tun kafin ta yo d’aki ta soma bud’o ledar, abaya ce me kyan gaske ga stones kota ina. “Wowww!” kukeji tana fad’i kamar Ya Ahmad yasan yadda nakeson abayah. Nan ta hau gwada wa kan kayarta bayan ta cire hijabin nata. Aiko daidanta tazo gwada yafa gyalen se kud’i ya fad’i daga ciki tana irgawa taga dubu biyar. “Yanzu Ya Ahmad wannan d’inne zece ba yawa. Baba! Baba!” Ta k’olla masa kira tana nufo d’akin nasa.

     “Ya akayi uwata ta kaina?” Ya tambayeta a kishingid’e tare da kashe radio’n dayake ji. “Wannan kaya fa daga ina?”
       “Masha Allah Ya Ahmad ne yakawo min yanzu kaga harda dubu biyar kuma.”
        “Kai Allah shi mashi albarka, shi kullum cikin wahala yake miki? Gashi ko kayan yamiki kyau kika fito kamar balarabiya.”
      “Kai! Baba dagaske?” Ta tambaya tana tsalle. “Sosai ma kuwa uwata.” ya amsata. Nan ta irga dubu biyu ta mik’a masa “gashi Baba ka rik’e wannan, Mama ma dubu biyu nida Afrah da Aiman kuma semu raba wannan.”
       “A’a uwata rik’e abinki kinji? Ki saya abubuwan da bakida dashi” ya mik’a mata.
        “Baba ni komai danake buk’ata inadashi ka karb’a kaji? Ko cafani sekayi dashi.”
     “Toh nagode uwata, Allah miki albarka ya cigaba da kare min ke.” “Ameen Baba zan koma d’aki.” Nan ta fice, isarta d’aki bada jimawa ba k’annenta Afrah da Aiman suka dawo.

     Atare suka shigo d’akin d’ayan tana nan kamar Fannah baratafi 13 years old ba whereas d’ayan kuma dududu intayi shekaru shine 3. “Ke wai Aiman kullum ne sekin tsaida mu akan hanya da sunan fitsari?” cewar 'yar babban (Afrah) kenan. “Anyin!” cewar Aiman yarinya ‘yar shekara uku se uban baki.

    “Ni kike ma rashin kunya? Iyye?”
       Fannah dake kwance kan katifa tana karatun History ta d’ago ta zauna “wai ke Afrah me damuwarki? Shikenan yarinya bara  tayi fitsari ba?”

        “Ya Fannah ni ban tsoma bakinki ba, nida Aiman nake magana.”
     “Aww rashin kunya zakimin? Dama d’azu Ya Ahmad yazo ya bani kud’i nayi niyan baki kad’an daga ciki amman tunda rashin kunya zakimin na fas-”
      Afrah ta katse ta, “a’a yi hak’uri Ya Fannah ta.” Da gudu ta haura kan katifar “yaushe Ya Ahmad d’in yadawo?”
      “D’azu bakiga abayan daya kawo min ba!” Nan ta mik’a hannu taciro daga cikin wata bako take Afrah data kusan kamota tsayi ta amshi zata soma gwadawa Fannah ta k’wace “kefa bakida seti, akawo min kaya kiwani ce zaki gwada?”

        “Su Ya Fannah manya masu samari.”
          “Samari? Ai Ya Ahmad ba saurayi na bane miji na ne, kinga yana level 5 yanzu ina ss2 ina ss3 yana neman aiki ina gamawa se muyi aure by then yasamu aiki in shaa Allah”

     “Ahh lallai fa soyayya ruwan zuma. I'm envious.” Cewar Afrah.
      “Don't be, kema lokaci ne beyi ba Allah ze had’aki da mijin dayafi Ya Ahmad sona.”  “Allah sa!” Afrah tafad’a da sauri “Ameen habibti” cewar Fannah.

       ****
     “Fannah! Fannah! Zo da sauri da Allah” kirar Mami. “Na’am Mami gani zuwa.” Sunnah take da niyar yi kafin tayi nafilar Maghrib kasancewar lokaci ya kusa yi amman dan kirar Maminta ta fasa tajeta. “Gani Mami”
        “Fannah yi hak’uri ki siyo min maggi ashago nan kusa wallahi bansan ya akayi ba har ya k’are ban sani ba yi hak’uri kinji mamana?”

      “Yanzu Mami aike zakiyi shine sekin had’ani da Allah harda bani hak’uri. Ina kud’in?”
       Nan Mami taciro hamsin ta mik’a mata. “Kinga ai kece babba Afrah yakamata in aika amman shegen yawonta tashiga nan mak’ota ganin jaririyar da Ameenatu ta haifa.”

       “Ayya ba komai Mami barin yi sauri kafin su rufe shagon.”
      “Toh Allah kare.”  “Ameen” ta amsa sannan ta fice.

ANAS

    “So Anas sauran ka 3 days kafire London kenan?” Cewar Shettima suna zaune a kan wata benchi a bak’in k’ofar gidansu. “Gonna miss me?” Anas yafad’a yana d’aga gira.
      “Eh mana I will miss you, nide Anas wallahi ka canza tsoron zuwanka London d’innan nake nan da Bama ma kana shaye shayenka a b’oye bale ace kaje can inda ba idan kowa.”

      “Toh yau kuma wa’azi zaka min? Kagannin nan yanzu haka akoi inda mukayi appointment da su Baana I will have my last drink a Bama yau kasan gobe zamu wuce Maiduguri, so kaga dole in sha in bugu tunda na k’arshe ne.”

     “Amman kasan Abuu nagari ko? In ya ganka a buge fah?”
      “Make up stories for me then, kamar yadda ka saba kace masa fad’a mukayi da wani. I'm going now.”
     “Toh masallaci fah?” Cewar Shettima.
      “Sena dawo zanyi sallar.” Daga nan ya fice inda suka saba had’uwa in zasuyi shaye shayensu ya je chan suka bugu like never, ko sanin ina suke in aka tambayesu ba sani zasuyi ba.

         Daidai Anas ya tashi ze tafi gida kenan aka soma wani erin masifaffen ruwa ba yadda Baana basuyi dashi yajira ruwan yad’an tsaya kafinnan ma hankalinsa yad’an dawo jikinsa ba amman sam yak’i jinsu ana ruwan yasoma tafiya, yazo ma besan ina yake dosa ba dan yadda ya bugu.

    **
FANNAH

     “Oh No! Shagon Ya Wakil a rufe gashi Mami battada maggin da zata yi amfani dashi dole in k’ara gaba” haka tatayin gaba duk shagunan a rufe amman still bata hak’ura ba. Bada jimawa ba aka soma ruwa me k’arfin bala’i gashi daga can tana hango wata shago a bud’e ta koma gida ba maggin kuma battaso. Cikin ruwan ta cigaba da tafiya daidai ta shiga wata lungu taga wani na miji daga gani a buge yake, duda acikin duhu ne hakan be hanata tantance kyansa da blue eyes nasa daya d’ago yana  kallonta ba. Take ta soma b’ari Allah sa ba gamo tayi ba. Mutum da blue eyes.

      Addu’o’in kariya tasoma yi jikinta se rawa yake gu d’aya ta tsaya jiran yazo ya wuce tayi gaba itama. Daidai yazo kusa da ita seya tsaya hannu ya d’aga yakai kan fuskarta tuni Fannah ta soma kuka tunda take ba d’a na mijin daya tab’a tab’ata inba Babanta ba. Ga k’arfin ruwan saman koda tayi ihu bame jinta shagon data gani a bud’en ma har sun rufe.

©miemiebee

 TANA TARE DA NI...

TANA TARE DA NI... PAGE 04
BY MIEMIEBEE


Cikin kuka tace, “dan girman Allah bawan Allah kayi hak’uri I beg of you please.” Jikinta se rawa yake tana hawaye. “Bawan Allah dan Allah kayi hak’uri I'm just 15 ba abinda zan iya baka have mercy on me please dan Allah.” Ko k’adan be saurareta ba hijabin jikinta yasoma k’ok’arin cirewa. “Wayyo Allah Mami na! Baba! dan Allah kuzo ku taimakeni! ihu take sosai.”

     Hannu yasa ya rufe bakinta. “Duk mata haka kuke, mesa zanji tausayinki? Data gudu tabarmu ta tausaya mana neh? Why will I have mercy on you? I hope you tell her abinda zan miki yanzu saboda itama ta d’and’ana little daga cikin bak’in cikin data sanyamu time da ta tafi ta barmu” Yana d’aga hannu daga bakin nata ya yaga hijabin nata into two. Ihu ta sake sakarwa “bawan Allah dan Allah kayi hak’uri karka lalatani dan girman Allah, kaji tausayi na I'm just 15 years dan Allah ka rufa min asiri karka b’ata min future”

     “Data tafi ita taji tausayin mu ne?”

       A rikice bakin ta na rawa tace, “ww..wa ce? Ni bansan wacce kake fad’a ba bawan Allah ban tab’a ganinka ba seyau kayi hak’uri dan Allah, karka lalata ni.” Be saurareta ba ya yaga kayanta. Nan ta shiga tare k’irjinta kuka sosai Fannah takeyi tana rok’an wannan bawan Allah'n haka ba tausayi ba inani yayi raping (fyad’e) nata.

     Tun tana iya jure zafin har ta sume wajen, kaca-kaca yayi da ita sannan ya fice yabarta ruwan sama ma dukan sumemmiyar jikinta. Shi kansa besan ya akayi ya isa gida ba a daren, kawai ganin kansa yayi bisa kan gado.
 
             A hankali ya bud’e blue eyes nasa wansa Shettima yagani a kansa. Tunanin meya faru yakuma yake nan ya soma lokacin da aka soma ruwa yace dasu Baana ze tafi sukayi k’ok’arin hanasa amman ya k’i jinsu ya hau tafiya can cikin wata lungu.. Wata lungu... Daga.. Can kwata kwata seya kasa tuna meya sake faruwa.

         “Anas how are you feeling? Sanda na fad’a maka karka bi su Baana kak’i kasan yadda ruwan saman nan yamaka duka kuwa? In akayi wasa seka kamu da mura.” cewar Shettima fuskarsa a d’aure

     “Ina Abuu?” Anas ya tambaya. “Ka gode wa Allah be ganka ba sanda nashigo dakai nan. Anas fisabilillahi mesa baraka rungumi k’addara ka manta da zancen Ummimi (mahaifiyarsu) a rayauwarka ka yafe mata ba? You're blaming yourself for her mistakes, misleading your life in the process. Haba mana Anas. Saboda Ummimi kasoma shaye shaye me haka please? Yanzu saboda ita ka kusan kashe kanka, abinda tayi ya riga ya wuce se mu rungumi k’addara mu barta da halin ta.”

        “No Shettima I can never do that, tariga ta juya min rayuwa, my life can never be normal kamar yadda kakeso, I can never move on barni haka kawai inta misleading rayuwar nawa har zuwa sanda zan mutu. Images of yadda ta tafi ta barmu will never leave my head, they are stuck in it forver”

       “Anas wai kai mesa bakajin magana ne ko dan ni k’aninka ne kafisan babba ya maka magana? Bari Abuu ya dawo I think is about time yasan gaskia shima, I've been keeping your secret for how many years now? A ganina with time zaka mance komai amman tunda you are not ready to change, tunda baka iya rungumar k’addara ba zan fad’a wa Abuu komi idan ya dawo.”
             Sede daya juyo ya kalli Anas yaga ko k’adan ma hankalin sa ba a gunsa yake ba, yayi nisa cikin duniyar tunani.

     “Anas?” Ya kira sunansa. Shiru Anas yayi be amsa ba dan haka ya d’an jijjik’a sa. “Yarinyar...” Anas yace fuskarsa cike da damuwa. Se yanzu ya tuna yaga wata yarinya acikin lungun. Amma sam ya kasa tuna ya fuskarta take ko fara ce ko bak’a ko kyakkyawa ko munana, ko doguwa ko gajeriya shide yasan yaga yarinya cikin lungun.

         “Wata yarinya kuma Anas? Yau kai ke kirar mace cikin gidan nan?”

     “Yarinyar Shettima ina take?”

    “Wai wace yarinya Anas, me kake fad’i?” Shettima ya fad’i fuskarsa cike da mamaki

           “Yarinyar Shettima, ina take? Ina ka tsince ni?” Cewar Anas.
             “Can gaba da gidan gona and also meya sami kayanka duk jini na duba ka banga ciwo ba.”

     “Jini fa kace? Ina kayan nawa?” Anas ya fad’a a rikice.
    “Na wanke already.”
     “Innalillahi wa inna ilaihi raji’un.” Abinda Anas keta nanatawa kenan duk yasa Shettima kid’imewa.

    “Wai meke faruwa ne Anas? Wani abu ne?”  “A’a nothing thanks please in baraka damu ba I want to be alone in d’an huta thanks.” Shettima na fita Anas ya rufe ido so yake ya tuna fuskar wannan yarinya amman ya kasa, “ina take? Mena mata? Mesa Shettima yace yaga jini ajikin kayana. Oh no! Nayi blaming yarinyar da batasan komi ba akan laifin da Ummimi tayi. Oh no! Nayi raping d’inta subhanallah shikenan nazama mazinaci, Ummimi baran tab’a yafe miki ba abinda kika min, kin cuceni” Dakyar bacci yayi gaba dashi...

**
FANNAH

       “Malam wallahi aiken maggi nan shagon bakin titi nace taje mun kuma har yanzu bata dawo ba, wayyo Allah inaji a jikina abu yasamu Fannah tah.”

      “Maman Aiman ki kwantar da hankalinki Fanmah yarinya ce me hankali tasan abinda takeyi barata tab’ayin abinda zesa mu cikin damuwa ba.”

     “Abin da nake nufi kenan Malam” Mami ta fad’a cike da tashin hankali.
          “Fannah bara ta tab’a yin abinda ze samu cikin damuwa ba saidai in za’a tilasta mata.”

    “Me kike nufi kenan Maman Aiman?”
         “Malam wallahi ji nake a jikina Fannah ba lafiya ba wayyo Allah tun kafin Maghrib fa na aiketa yanzu har Isha bata dawo ba, Allah ba lafiya ba nashiga uku!”

    “Maman Aiman ki kwantar da hankalinki yanzu d’auko hijabinki ga lema anan muje mu duba nan mak’ota ko halan tashiga tana jiran ruwan saman ya d’an saurara.” Nan ta d’auko hijabi sunzo fita kenan Aiman ta fito daga d’aki “Mami ina zakuje?”

         Idan Mami cike da hawaye tace, “nemo Ya Fannah zamuyi Aiman, bata dawo gida ba tun d’azu” daidai lokacin Afrah ma tafito “zan biku Mami.” tace idanta cike da hawaye tunda take bata tab’a shiga tashin hankali kamar na yau. Fannah ba mutumiyar yawo bace, ba inda take zuwa banda boko tunda ta kammala haddan Al~Qur’aninta. Dole ne wani abu yasameta a hanya, fatansu Allah sa ba sharri bane.

       “A’a Afrah ki zauna da Aiman a gida in shaa Allah yanzu zamu dawo.”

      “Mami what if something bad ya samu Ya Fannah fa? Please kibarni inje” tafad’a hawaye na tsiyaya a idanunta cike da tausayi da tsoro.

       “In shaa Allah ba abinda ze sameta” cewar Baba “ku zauna yanzu zamu dawo.”  “Toh Allah kare” Afrah tace. “Ameen” Mami da Baba suka amsa a tare sannan suka fice cikin ruwan sama. Aiman ce ta rik’o hannun Afrah, “Ya Afrah me ze samu Ya Fannah?”
        Murmushin dole ta k’irk’iro “in shaa Allah ba komai karki damu kinji? Ya Fannah will be alright.”

          *
         “Malam suka ce Fannah bata shigo nan ba innalillahi malam dan Allah ina zataje? Ina aka kaimin ‘yata?!”
          “Maman Aiman panicking is never a solution kizo mu dudduba kusa ko zamu ganta cikin shagu nan bakin titi” Haka fa iyayen Fannah suka ta duba sak’o sak’on unguwar tasu ba Fannah ba alamarta har sun fidda rai se Mami ta tuna shagon dake gaba da wata lungu a sabuwar unguwa tace suje su duba, sunayin wajen kuwa sega Fannah kwance a k’asa half naked ruwan sama yamata tsinannen duka ko numfashi battayi.

          “Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!” kawai ke tashi gun both Baba da Mami were shocked hawaye gangara suke daga kumatunsu suna kallon yadda aka walak’antar masu ‘yarsu. Mutuwan tsaye Mami tayi Baba ne yayi k’arfin hali yaja zanin ta dake gefenta ya rufe mata jikinta dashi tare da rungumota yana kiran sunanta sam bata amsa ba dake ko numfashi battayi. Alokacin Mami ta sakar dawata erin k’ara    
              “FANNAAAHHHHH!!! WAYYO ALLAH!” Da gudu tayo kansu tare da jefar da leman ta karb’e Fannah tareda rungumota tana kiran sunanta “FANNAH! FANNAH! Dan Allah karki tafi kibarmu dan Allah kitashi wayyo Allah!” Kuka kenan!

         Mota Baba yasamu da k’yar aka sa Fannah ciki suka wuce babban asibitin dake hukumar Bama. Nan take akayi emergency da ita sam Mami ta kasa daina kuka shikansa Abba kuka yakeyi duk yadda yayi ya hana kan sa kuka ya kasa. Hannun Mami ya rik’e yana bata hak’uri tana kuka tace, “mesa Malam? Mesa se Fannah ta za'ai wa haka? Hankalinta yayi yawa ace an mata wannan tsiya. Malam shikenan an rusa wa ‘yata future Allah ya isa ma duk wanda ya mata wannan d’anyen aiki barin tab’a yafe wa ba...” ta fashe cikin wata erin matsanancin kuka.

       Rungumota Baba yayi yana bata hak’uri shima yana kukan. “Nima kaina abinda ke d’aure min kai kenan, wani azzalimi ne kawai yayi taking advantage na innocence nata saboda Fannah bawai tana mu’amala bane da maza bale ace saurayi ne yamata wannan abu, Ahmad ne kawai ke zuwa wajenta kuma nasan Ahmad bare tab’a aikata mumunar abu kamar haka ba.”

**
3 hours later
   K’ofar d’akin da Fannah ke ciki ya bud’u likita ya bayyana daga bayansa. Da sauri su Mami suka taresa. “Ya ‘yar tamu likita ya jikin nata?” cewar Mami da Baba a tare. Kai ya k’ada a hankali fuskarsa cike da tausayi. “Likita dan Allah karka fad’a min ta rasu, dan girman Allah” Mami ta fashe da kuka Baba yana bata hak’uri.

      “Iyayen Fannah kuyi hak’uri amman munyi duk iya abinda zamu iya dan ceto ran ‘yarku, mun kasa, ya gagare mu, mun kasa at all ruwan saman ya mata duka sosai har na fitan hankali, yabi ta kunnenta da hanci har baki, bayan haka kuma ga raping nata da akayi wanda aka mugun ji mata ciwo. Zafin datayi witnessing yafi k’arfin jikinta yafi k’arfin shekarunta. Yarinya ce sosai. Kuyi hak’uri dan Allah amman kar kuyi losing hope anyi waya dawani likita daga Maiduguri Teaching Hospital gobe da sassafe ze iso ya dubata inhar da abinda ze iya toh se mu godewa Allah.”

        Mami dake kuka kamar zata cire ranta tayi k’arfin halin fad’in “likita me kake nufi kenan? har yanzu ban fahimce ka ba ‘yar tawan tana raye ne kokuwa ta mutu?”
 
           “Maman Fannah ni kaina banda amsar wannan tambaya zuciyarta na bugawa yana aiki amman kuma bata numfashi, mun samata oxygen munyi komi still ba progress, kwata kwata bata responding to stimuli.”
              “Innalillahi wa inna ilaihi raji’un. Malam sun kashe min ‘ya shikenan Fannah ta tafi ta barni, ta barmu Malam” takuma fashewa da wata masifaffiyar kuka Baba na bata hak’uri, shikansa hawaye yake zubdawa shar shar.

   “Baban Fannah ‘yarku bata gama mutuwa ba tunda tana numfashi, duk me numfashi aikuwa nada rai kenan.  Addu’a kawai zaku sata ciki sosai, Allah sa tayi making it through the night in shaa Allah in gobe likitan yazo seya duba ta. Allah bata lafiya ya k’ara maku hak’uri. Excuse me please.” Nan ya fice. Har k’asa Mami ta sauk’a tana kuka.

     In ta rasa Fannah ta rasa komai a duniya cikin yaranta uku ba wacce takai Fannah hankali, ‘yar da zaka aiketa sau d’ari a rana barata b’ata rai ba bara kuma tayi fushi ba. ‘yar da kana ce mata bari ta bari kace yi kuma tayi. ‘yar da is ready to sacrfice the last kobo she have just to make her parents happy. Barata iya rayuwa ba Fannah ba. If only zata iya bada ranta asawa Fannah da tayi.

      Kuka take sosai, abin tausayi, tanayi Baba nayi tabbas shima kap cikin ‘ya‘yan sa babu kamar Fannah. Kalmar son kai ko k’adan Fannah bata sani ba, she can give up her own happiness for others...

©miemiebee

 TANA TARE DA NI...

TANA TARE DA NI... PAGE 05
BY MIEMIEBEE


       “Malam baran iya shiga ganin Fannah ba, if only zan iya bata raina wallahi zanyi.”
           “Addu’a zamu mata Maman Aiman kinsan dole ke zaki kwana da ita.”
     “Yanzu Malam kud’in asibitin fa? Taya zamu biya? Wallahi duk d’an iskan da yama Fannah wannan abu be kyauta ba.” Ta kuma fashewa da kuka hak’uri Baba ke ta bata. “Karki damu da wannan, zan sayar da shanu na in shaa Allah zamu biya bills nata dashi, fatan mu Allah bata lafiya”

               “Shikenan yanzu dama shanun nan kad’ai muka mallaka, Allah ya isa wallahi.” A sanyaye suka mik’e zuwa d’akin Fannah, Baba na bud’e k’ofa suka hango Fannah kwance kan gado ba alaman nishi a tattare da ita.

        Da gudu Mami tayi kanta ta tsuguna tare da rik’o hannunta se kuka take zubawa. “Maman Aiman addu’a zamu mata kuka baida amfani barin koma gida in d’ibo muku abubuwan da zaku buk’ata, kiyi hak’uri” ahaka ya fice isarsa keda wuya ya tarar da Afrah se safa da marwah take a parlour tana ganinsa tayo kansa. “Baba ya kun sami Ya Fannah?” Kallon daya mata yasa jikinta yayi sanyi take idanunta suka cike da hawaye “Baba dan Allah meya sami Ya Fannah?” ta tambaya tana kuka.

           “Afrah da rungumar k’addara aka san musulmi, mun samu Fannah amman yanzu haka tana asibiti.”
          “Innalillahi wa inna ilaihi raji’un Baba me kake nufi? Meya samu Ya Fannah?”
          “Bata da lafiya Afrah, mun... Mun...” Sekuma yayi shiru hawaye na cika a idanunsa sakamakon hakan ya sake tada ma Afrah hankali. Tana kuka tace, “Baba dan Allah ka fad’a min meya samu Ya Afrah.” Zaunar da ita yayi ya bata labarin komai kuka Afrah keyi sosai kamar zata cire ranta sam tace seta bisa asibitin taga yarta.

        Ba yadda Baba beyi ba dan hanata amman ta dage setaje. Aiman kuwa ta jima da bacci, bayan sun gama had’a abubuwan da zasu buk’ata Baba ya rakata ya tsara mata abin hawa sanda suka b’ace ya dawo ciki. Tafiyar minti 15 ya isar da Afrah asibitin, bayan ta biya sa kud’insa tashigo ciki direct d’akin Fannah ta wuce.

      Tana bud’o k’ofar taga Mami tsugune gefen Fannah se kuka takeyi take itama wani kukan ya faso mata da gudu taje ta rungumi Mamninsu suna kuka sosai. Sunjima suna abu d’aya sannan Mami ta tambayeta “Afrah me kkeyi anan ina Babanku?”
       “Mami yana gida na zo ne in tayaki kwana.”

       “Afrah bekamata kiga yarki a wannan yanayi ba da kin koma gida.”
      “Haba Mami! Ya Fannah fa yayata ce taya zakice haka?” Nan ta jiyo tana kallon Fannah wacce take kamar gawa. Wani sabon kukan tasoma ta rungumeta, tana kuka “Ya Fannah dan Allah karki mutu ki barmu, Allah ze sak’a miki in shaa Allah.” Da kyar Mami ta lalasheta tayi shiru.

       Mami ko kayan tean da Afrah ta had’o musu susha tea ma takasa sha hankalinta duk yabi ya tashi. Afrah bata tab’a ganin Maminsu cikin tashin hankali irin wannan ba.

     Kwana Mami tayi tana nafilfilu tana rok’an Allah haka itama Afrah bawanda yayi bacci cikinsu.

     ****

     Washegary da safe misalin k’arfe 8:00AM babban likita daga TH na Maiduguri ya iso. Aikin kusan awa uku akayi kan Fannah sannan likitan yafito. Baba, Mami, Afrah da Aiman dake rik’e a hannun Afrah duk sukayi kansa “likita ya jikin ‘yar tawa?” Cewar Mami jikinta se b’ari yake.

       “Ku kwantar da hankalinku in shaa Allah ‘yarku zata samu sauk’i tana cikin state of coma ne yanzu within 5-7 days in shaa Allah zata farfad’o.”

     “Alhamdulillah!” kukeji a wajen. “Likita amman har kwana biyar? Kana nufin barata san inda take ba har nan da tsawon kwana biyar ko bakwai?”

     “Eh Hajiya, she've been through alot, raping at this tender age ba k’aramin abu bane, tamugun jin jiki, gakuma ruwan daya mata duka again yasa ta kamu da pneaumonia but in shaa Allah inta farfad’o everything will be alright za’a bata magani karku damu.”
     “Toh likita mungode sosai Allah biya.”
       “Ba komai” ya fad’i sannan ya fice.

       A hankali Umma ta soma kuka “Malam yanzu har kwana biyar ko sati ‘yata zatayi batasan inda take ba? Innalillahi wa inna ilaihi raji’un.”
      “Maman Aiman godiya yakamata muyi tunda Allah yabar mana ita be karb’i abinsa ba, mu cigaba da addu’a in shaa Allah zata samu sauk’i.”

   
       *ANAS*

    _Bawan Allah dan Allah kayi hak’uri kar ka lalata min future, wallahi baran iya baka abinda kake nema ba I'm just 15 dan Allah karka lalata ni kayi hak’uri ka rufa min asiri_

    Firgit Anas ya farka daga bacci yana numfashi da k’arfi sosai wanda hakan yasa Shettima tashi shima daga bacci tun jiya yaga yanayin wansa ya canza koda ya tambayesa meh kuwa ce masa yake ba komai, wannan karan ne na farko da Anas ya soma b’oye masa abu. Gadonsa ya bari yaje yasamu Anas tare da dafe kafad’arsa. “Anas lafiya? Ka jima fa bakai mafarkin Ummimi ba, meya faru kuma yau?”

    “Ba mafarkin Ummimi nayi ba.” cewar Anas yana raba ido.
      “Mafarkin me kayi toh?”
      “I don't want to talk about it karka damu its okay.” Anas yayi k’ok’arin calming kansa.
      “Its not okay Anas, tun jiya nake lura da kai, something is bothering you and you’re keeping it to yourself. Tell me.”
      “Nace maka ba komai” Anas yayi insisting. A hankali ya mik’e ya wuce bayi. Tun shigarsa bayin ba abinda yakeyi se tunanin mafarkin dayayi akan yarinyar jiya, ko kad’an besamu yaga fuskarta ba a mafarkin. Ruwa ya riga watsa wa a kansa sannan yayi wanka yafito ya shirya kayakinsa da komai dake yau ze tafi Maiduguri, gobe ya wuce Abuja daga can kuma se London.

      Yana fitowa daga d’akin nasu ya rufo k’ofar yana juyawa sega Amal idanunta sunyi ja “my Angel waya tab’aki?”
      “Ya Anas wai yau zaka tafi baraka sake dawowa ba se nan da 5 years?”
      “Waya fad’a miki haka?” Ya fad’a yana wasa da gashin kanta.
     “Ya Shettima ne kuma wai kana barin gidan nan ze dakeni wai dama tarani yake, Ya Anas dan Allah kar ka tafi” ta rungumesa da tsayinta daidai kunkuminsa. Sama ya d'agata “stop crying kinji Angel? very soon zan dawo kuma duk sanda Shettima ya tab’aki ki d’au wayan Ummie ki kirani I promise in na dawo zamu rufesa a d’aki mumasa dukan tsiya.”

     “Dagaske Ya Anas? Zamu masa duka?”
     “Sosai ma bulala zan baki ki zanesa se yayi kuka.”
   “Yeyyy!” Hugging nasa tayi “I love you Ya Anas.”  “I love you too Angel. Sauk’o to muje wajen Abuu.”
     “O’o ni muje a haka ka d’aukeni for the last time.”  “Okay Angel” ya manna mata kiss a goshi sannan yaja akwatinsa suka fice. Suna isa parlour ya sauk’eta tare da gaishe da Abuu sannan Ummie.

     Breakfast suka ci bayan sungama Abuu ya zaunar da Anas.
       “Anas kaga karatu zakajeyi ba hutu ba kuma kafi kowa sanin wahalar da mukayi kafin muka samo maka wannan scholarship I'll be very angry inhar baka je kacika mana burinka na zama architecture ba.”

     “In shaa Allah Abuu” cewar Anas dake kallon kan carpet.

       “Kasani kuma duk abinda kakeyi Allah na kallonka, kowa yasan ya rayuwar London yake, inbanda iskanci ba abinda sukeyi, ba ruwanka da zuwa beach bale kaje kaga abinda ze hana ka d’aukan karatu. Qur’ani shine guidance naka, karka kuskura kabari rana ya wuce ka baka d’au Qur’ani ka karanta ba. Ba ruwanka da ‘yan mata ko friends na banza. Ba ruwanka da shaye-shaye Anas. Kajini ko bakaji ba?” ya gargad’i Anas tare da rik’e kunnensa.

    “Naji Abuu na gode in shaa Allah zan kiyaye duk wannan abubuwan daka lisafo, nagode.”

    “Toh Baba na nikam nasan ko ban ja maka kunne ba kasan what is right and wrong, ban tab’a doubting tarbiyarka ba. Allah baka sa’a ya kareka daga kowani irin sharri Baba na.” Cewar Ummie.

    “Ameen Ummie nagode.”

**

         “Amal kukan me ne kuma haka sekace mutuwa yayan naki zeyi? Makaranta fa zasa in shaa Allah ze dawo.” Cewar Ummie tana lalashin Amal dake ta kuka.
      “Bar shakwab’a de Ummie ke kike biye mata ma ai, tayi kukan jini tagadama ta mutu.” Shettima ya fad’i yana ma Amal dariyan mugunta. Harara ta watsa masa me rai da lafiya “toh nak’i kukan” tasa hannu ta share hawayerta “kaine zaka mutu mugu kawai.”

      “Ke! Rashin kunya kike min?” Ya mik’a hannu ze finciko ta daga jikin Ummie, hannu Ummie tasa ta make hannun nasa da k’arfi “okay dan Amas yatafi zaka soma cin zalin Amal ko? Toh kasani Anas yace duk sanda ka tab’a ta in kira sa a waya in fad’a masa dan haka ka mayar da hankalinka. Kai kullum kata biye wa ‘yar yarinya duk kabi kasa ta raina ka.”

      Gwalo Amal tamasa harda sa hannu kan kunnenta. “Ni shikenan Ummie kullum ma wannan maras kunyan zaku na ba wa gaskiya wallahi kicigaba Allah kawo rananda za’a barni dake gidan nan.” ya cize yatsa.

     “Karki kula sa Amal taho muje mu siya miki sweet ga kud’i nan dayawa Anas ya ajiye miki.” Juyawa tayi tasake ma Shettima gwalo sannan suka fice da Ummie.

***
Da misalin k’arfe 1:00pm Ummie ta kira wayar Anas ringing kad’an yayi ya d’aga “hello Ummie” yafad’a cikin muryarsa me dad’in gaske.
   “Baba na ya gajiyan hanya?”
      “Alhamdulillah Ummie tun d’azu muka iso ai, ina gidan chairman ahaka.”
       “Toh yayi kyau, Babana kaji abinda Abuu ya fad’a maka ai? Nasan kanada hankali kuma kasan abinda ya kamata kar kayi abinda ze haddisa mana matsala kaji ko Babana?”
     “In shaa Allah Ummie karki damu, ina Angel d’ina?”   “Tana parlour tana kallo barin kai mata.” Nan ta mik’e takai wa Amal “ga Ya Anas nasan yanason ku gaisa.”

     “Ya Anas ina wuni?”
   “My angel ya kike?”
     “Lafiya, har kun isa London d’inne?”
    Murmushi kad’an yayi wanda hakan yasake bayyano da kyansa. “A’a Angel da saura sosai ina Maiduguri ne yanzu se gobe zamu wuce London.”
     “Okay! Nagane. Ya Anas kaga d’azu Ya Shettima ya nank’washeni akai dan yaga baka nan.”
       “Shettiman? Bari ki riga irgamin duk mugunta daya miki ina dawowa zamu masa duka.”
    “Yeyy! Ya Anas I love you ina kallon frozen se anjima.”
      “Yawwa Angel d’ina bo-bye.”


  FANNAH
    6 days later...

       “Mami kukan ya isa mana dan Allah, ki dubi yadda kika rame dan Allah.” Cewar Afrah dake rik’e da Mami itama tana hawaye.

      “Afrah kiyi hak’uri ba san ra’ayi na bane nima, yau kwanan ‘yar uwarki shida bata san inda take ba taya baranyi kuka ba. Gani nake kamar zata tafi tabarmu. Allah ya isa, haka kawai Fannah bata masa komai ba ya zab’i ya wulak’an ta ta. Allah ze sak’a mata.”
       “Shhh Mami dan Allah karkiyi magana haka, in shaa Allah Ya Fannah zata farfad’o lets not lose hope Mami.”

*
     Da azahar misalin k’arfe 1:30PM wani dattijo yashigo cikin asibitin, kallo d’aya za’a masa asan wan Baban su Fannah ne. Zekai shekaru irin 50 a duniya. Baba dake zaune a bakin k’ofar d’akin Fannah ne ya hango wan nasa nan ya mik’e “sannu da zuwa Ya Khaleel.”
        “Sannu dazuwa fa kace? Ashe iskancin da ‘yarkan tayi kenan shine ka b’oye min kak’i gaya mun, toh Allah ya sanar dani gaskia.”
     “Haba ya Khaleel ya kake magana haka? Kafi kowa fa sanin halin Fannah ba halinta bane tarayya da d’a na miji.”
Share:

3 comments:

  1. Thanks alot our elbow

    ReplyDelete
  2. keep it up kana kukari

    ReplyDelete
  3. Surayya abdullahi13 October 2016 at 10:32

    Good Allah yakara basira

    ReplyDelete

pls drop down your comment......
dan Allah ku ajiye comment.

Tallata Kayanka

Guide Tricks Blog

Be With Me Technology

Popular Posts

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).