shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wanda aka fi sani da hausa novel wanda ni Muhammad abba gana nake rubutawa dan wayar tare da fadakarwa ga mutane a yanayin da muke ciki.

Tuesday 4 October 2016

WAYE SANADI? 31---35

waye-sanadi.jpg

[10/3, 9:00 AM] Äbbå-Gãñâ: WAYE SANADI? 31 MUH'D*ABBA*GANA 09039016969

www.abbagana.pun.bz

Allah mallam ba zan tafi ba sai de karasa ganin na kafe bazan tafi ba yasa yace duka mu tafi aji. muna shiga na dauko sunayen Allah ina dubawa naji an kira sunana nayi saurin dago kai kizo inji mal ahmad yana office dinsa kan nayi magana ta fita maida kaina nayi ina duba littafi har sai da ya kara turo wato jin nayi mata shiru ta hau masifa ,dan wulakanci a nayi miki magana kinyi shiru me kika dau kanki me kike ji dashi sai kace yar gidan uban wani gidam ma da ake takama dashi ai mun san komai zan agolanci aka zo ake anaso ana kaiwa kasuwa..." saukar mari da taji shi ya hanata karasawa ba kiyi karya ba zaman agolanci nazo gidansu aminiyarki maryam sai kuma nazo nafisu iko da isa har ma da samun matsayi shi kuma wanda kike haukan a kansa baya gabana hasalima ni din nafi karfinsa dan ko ta gefen zuciyarta bai taba giftawa ba ke da kawarki kuke hauka akansa duk malaman makarantar nan nafi karfinsu babu tsoron maganata karatu nazo nema ba hauka a kan namiji ba, kiyi hankali dani kadan nayi miki kinyi sa,a bana hada jiki da kowa bare ke kazama ga sako ki gaya masa ba zan zo ba, in yana da karfi yazo ya dauken ko ya koren a makarantan mari na kara zabga mata sai ki hada ki gaya masa ya rama miki banza me kishi kan abinda bai san kina yi ba. baki daya ajin suka rude da ihu suna cikin ihu ya shigo fuskar nan babu imani nan da nan suka gigice tsawa ya dakawa nadiya meya kawoki wato kun mai da ajin kasuwa koh? dukkan ku ku fita daga ajin juyowa yayi ya dakan tsawa ba zaki fito ba? banyi kifi ba akan me zan fita ke rashin kunyar daki kewa sauran malamai zaki min duk wanda na yiwa rashin kunya shiyaja nikam babu inda zani tashi ki fita wallahi babu inda zan fita zakici ubanki zanyi maganin taurin kanki ya juya ya fita a fusace ya dawo na kalli hannunsa bulala har hudu tashi ki fita na dago kaina ina malam mun gama magana nace banyi laifi ba dan haka babu inda zan.... kan na karasa ya daga iya karfinsa ya zabgan a kaina wata irin azaba nayi nayi saurin rintse ido ban kuma motsa daga inda nake ba haka yayi ta zabgana duk inda ya duken sauri wajen ya dauke duk yan ajin sun shigo suna bashi hakuri wata irin kara nayi na mike nayo kansa da hannu daya na dakeshi ya fadi kan ya mike na karbe bulakar na hau dukansa da gudu suka fita kiran malamai dakyar mal. ahmad ya karbe bulalar hannuna a hankali na bude idona nayi saurin mikewa umma na gani da daddy sannu safiyya lafiyata klau umma yaushe na dawo ji nayi duk jikina ciwo yake, safiyya ki tashi kici abinci gani nayi duk jikina shedar bulala nan take na tuna da mal. umar to ya akai naxo gida khalifa ne ya shigo dake, ki tashi safiyya na daga masa kai daddy ana kira a fusace waye yake kirana wanda yaxo Allah daddy duk hakurin da zasu baka kar ka hakura sai an koya masa hankali shegen malamai bai san aikinsa ba.

Abbagana hausa novels @ facebook. [10/3, 9:03 AM] Äbbå-Gãñâ: WAYE SANADI? 32 MUH'D*ABBA*GANA www.abbagana.pun.bz

mikewa yayi ya fita umma ta juyo tana kallon khalifa kai da zaka bashi hakuri shine kake kara tunzura shi? haba umma ba kya ganin yadda yayi mata kice ayi hakuri gara a koya masa hankali na juyo ina kallon umma me akayi wa mal. umar? Alhaji ne yasa a kamashi kwana biyu bana zuwa ko ina kullum sai mal ahmad ya turo a a kirani na aika masa cewa bazan fito ba. momy dan Allah meyasa baki leka kin gaida nana ba, momy ko maryam bata je ba hab..... yi min shiru ba za muje din ba mara kunya kaja mu ka kaimu momy kiyi hakuri gani nayi ya kamata kije ai kasan ni din ban san ya kamata ba, saboda kai baka da kishina yariny ta mari uwarka amma kake tunanin naje dubata to ba zanje ba kuma wallahi ka kara zuwa kamin maganarta sai na saba maka shashasha mara hankali. daka bakin kofa taji muryarsa wallahi zahra khalifa ya fiki hankali kuma in har kina so mu shirya ki tashi kije ki dubata ya shiga kiran maryam da sauri ta fito. gani daddy jiya dana tambayeki kinje kin duba safiyya me kika ce? shiru tayi ya daka mata tsawa fice waza kije ki mata sannu, yana fita sukaci karo da abba "daddy sann....." yi min shiru wato ban isa na saka abu kayi ba ko daddy yanzu nake shirin shiga to wuce muje tare suka shigo fuskarsa a hade yace ya jikin? ban ko kalleshi ba na amsa na wuce cikin dakina. karfe tara na shirya umma zan tafi karatu to kin karya? zanyi break a makaranta yau zamu fara jarabawa to Allah ya bada sa,a dakinsa na shiga yau zan koma makaranta har kinji sauki safiyya? naji sauki kasa asaki mal. umar saboda me? bazan kara zuwa islamiyyan ba kaga ko rike shi bashi da wata fa'ida. ina shiga na hangi momy tayi parking tare muka shiga class baby ya jikin ki naji sauki jiya ina ta kiran wayanki ba,a daga ba momy na ma mance da ita in na koma zan duba. ina koma gida na dauko wayar miss call yafi hamsin nayi saurin dubawa wannan number ceta min miss call 45, na duba account din naga akwai raguwar kudi na kira number ana dauk wa suratul iklas naki shiru nayi ina saurara har aka gama sai kiran ya katse. wajen wata daya kullum sai an kirani da number ina dauka wa karatu kawai nake ji wanda hakan ba karamin farin ciki yake sani ba, har yau ban san waye yake da number ba kuma ban samu nasan waye bane. yau tun da safe nake jiran waya shiru bayan na idar da sallah na dago wayata na duba saina ga da raguwar kudi kadan sai na fara rubuta sako kamar haka *dan Allah waye ne me wannan number nayi sending ban fi minti biyar da turawa ba ga reply kamar haka "muhammad. i .salis

Abbagana hausa novels @ facebook. [10/3, 8:12 PM] Äbbå-Gãñâ: WAYE SANADI? 33 MUH'D*ABBA*GANA www.abbagana.pun.bz

abun ya bani mamaki kira ne ya shigo kamar kar na daga can na daga muryar sudeis ta duka kunnena cikin suratul ma,ida shiru nayi ina saurara har ta kare nayi sauein cewa dan Allah waye ne? cikin wata zazzakar murya aka furta muhammad ne ana fadar hak aka katse na ajiye wayan na wuce cikin toilet, ina toilet naji kara wayata bayan na fito na daga hello suppy kin shirya shirin me kuma? kin mance bikin zulaih oh nina mance kuje kawai bazan samu zuwa ba haba suppy karki mana haka kin san motar rukayya ta samu matsala, ni ai bam sani ba to yanzu kin sani dan Allah ki shirya gamu nan zuwa ke sadiya bafa inda zani kinga ga mominki zata miki magana kan nayi magana naji muryarta safiyya mekike cewa ? ba magana nayi ba cewa nayi sai kun karaso okey mu same ki a ciki? zan fito kafin ki iso ma tunda muka shiga mota babu wanda yayi wa wani magana ba har muka karasa wajen party yan mata ne kowa yana harkarsa , parking nayi momy in kun fito ina jiranku ba zaki fito ku gaisa ba Allah momy babu inda zani toh shikenan wayata ce tayi kara nayi saurin dagawa naje angwa in na koma gida zan kira ka ina fadar haka na katse. fitowa nayi ina kiran su sadiya mu tafi mutum na gani tsungune bayan mota ta na kunna touching waya na na haskashi da sauri na koma cikin motana ina zaune har na fara barci naji karar waya na tashi na dauko yau dai na kira mu gaisa abunda aka furta kenan dan Allah waye kai kai tsaye aka ban amsa kiyi hakuri na takura miki koh? ni dai kawai ka gaya min kai waye ne ya akayi ka samu numberta? zan gaya miki gaskiya numberki a jikin kudi na ganta nasai credit an ban canji to ban duba ba kum lokacin muna hanyar zuwa filin jirgi zan taho karatu kasar waje bayan na sauka na duba kayana sai naga canji ina budewa sai naga number an kum rubuta suppy tawa ni kuma sai naji ina son jin muryar me number da fatan kin gamsu da bayanina.

Abbagana hausa novels @ facebook. [10/3, 9:58 PM] Äbbå-Gãñâ: WAYE SANADI? 34 MUH'D*ABBA*GANA www.abbagana.pun.bz

tabbas na tuno ranar da sadiya ta rubuta number ta a jikin kudi kawar kice? school din mu daya to baki gaya min sunanki ba? meye ruwanka da sunana, ina son kawai naji "safiyya mukhtar shine kawayenki suke kiranki da suppy an ce maka kawaye ne dani? zan kwanta okey safiyya na gode sai da safe. ya rage saura sati uku umma su tafi tun da naje makaranta nake ta ware ido inda zan hango sadiy ko momy naji an rufe min ido momy ko sadiya ta bude tana dariya kallon me kike ku nake nema littafi ta zaro take karantawa, momy kema kina karatun littafi?? baby labarinsa aka ban momy meye a cikin littafin uhumm baby bazan iya baki labari ba zan so ki karanta baby ban taba ganin rayuwa irin wannan ba zan baki ki karanta momy ya sunansa? bayan ta juyo tace da ita "sireenah"baby so nake kawai na karanta na 3 naji karshen matar da yayanta. ya rage saura kwana uku su umma su tafi ina daki umma ta shigo nana kizo alhaji yana kiranki tare muka fita muka tarar dashi yana zaune a falon umma, safiyya kinga saura kwana uku mu tashi shine nace zaki zauna ko zaki tafi gidan kaka kan mu dawo? zan zauna sai a dauko kaka ta tayani zama kuma muma sauran sati hudu mu tafi lagos, Allah ya kaimu karatu yazo karshe kudi ya zaro gashi ki rike a hannunki na karba ranar da suka tafi ina school ban samu damar raka su ba ina dawowa na tadda kakz a,a yar tsohuwa kin sha A/C har kin fara mulmulewa zaki fara halin naki koh kinga abar magana yanzu ina abinci na ba wani musu ta nuna min. khalifa ya shigo muna cikin hira maryam ta shigo yaya kazo inji momy okey ina zuwa. muka ci gaba da hira ji mukayi an banko kofar kai dan wulakanci ana kiranka shine kake zaune wajen wannan kwadayyayun tare suka fice aiko ranar kaka ta rantse ba zata kara kwana gidan ba babu irin magiyar da khalifa bai mata ba amma taki haka dole ya kaita gida, ina daki naji sallamarsa har ka dawo daga kai tsohuwa yar rigima babu wani rigima sai gaskiya kuma wallahi in daddy ya dawo sai na gaya masa yanzu nana zaki iya kwana ke kadai to me zai sameni? shikenan safiyya zanje nayi sallah yana fita momy su ta shigo kina ina makira? nayi saurin fitowa ta cigaba da cewa to wallahi abinda zan gaya miki ki fita daga harkar dan in kina ganin uwarki ta cinye zuciyar alhaji toke kinyi kadan ki cinye tasa...........

Abbagana hausa novels @ facebook. [10/3, 9:59 PM] Äbbå-Gãñâ: WAYE SANADI? 35 MUH'D*ABBA*GANA www.abbagana.pun.bz

murmushi na saka zahra'u ni safiyya a golar gida nafi karfin danki kece kike kishi akan danki har kike tunanin ko auransa zanyi umma kuma da kike maganar ta cinye zuciyar mijinki ladabi da biyayya ta fiki ina fadar haka nayi daki. tun da ga ranar ban kara ganin khalifa ba yau ina kwance naji shigowar message dagawa nayi tare da budewa 'please safiyya kin ban dama na kiraki mu gaisa na rasa ya zanyi bana so na kira ba tare da amince warki ba. naku muhammad I salis. muhammad na kara mai mai ta sunan kwata kwata na manta dashi filashin nayi masa ba,ayi mintu biyu ba ya kira "Assalamu alaikum naji sansanyar muryarsa ta doki kunne na safiyya kin amince na dinga kira muna gaisawa kau nifa na mance da kai sai ka tuna min waye kai bakin ciki ne ya tunkare zuciyarsa da kyar ya iya hadiyewa tare da cewa ni kam kinga bazan taba iya mancewa dake ba koh? sosai ma kuwa kina lafiya ya karatu? lafiya klau karatu mun godewa Allah safiyya ni baki tambayeni ya karatuna ba, meye ruwana sa karatunka kaga maganar ta isa haka zan kwanta, bai kamata ki kwanta haka ba cikin mamaki nace saboda me? ki tashi ki roki ubangiji bukatunki ko ki daura alwala ki kwanta.' okey na gode ina cikin sallah naji wayana na kara bayan na idar nayi addu'o'ina na dauko littafin da momy ta ban na karanta "MASOYINA HAR ABADA" na mrs umar. ina cikin karantawa wayata tayi kara na daga, na zata kinyi barci ga karatu nan zan sa miki, to na gode ina saurara muryar sudeis naji cikin suratul rahman tun ina bi har barci ya dauke ni muryarsa naji safiyya iya nan kika iya? firgit na bude idona cikin wata rikitacciyar murya nace ka kashe kar kudinka ya kare wata irin ajiyar zuciya ya sauke kiyi addua sai na kashe kan ya kara wata magana na katse wayar. washe gari umma ta kirani mun jima muna hira muna cikin waya naji sallama juyawa na momy ne tare da farida na hango tare muke karatu da ita yar katsina ce da gudu na taro su. yanzu baby ke kadai kike kwana momy ya zanyi umma ta tafi ta barni na juyo wajen farida yaushe kika dawo ina kuma tsarabata uhum suppy kin fiya ban haushi kudi kawai na karbo kin san saura sati daya mutafi. sai bayan isha suka tafi na gama shirya tsaf zan kwanta naji karar wayat sai da ta kusa katsewa sannan na daga' na zata kinyi barci yanzu nake shirin yi dai okey safiyy wai me kike karantawa ne?? da sauri nace meye ruwanka da abinda nake karantawa, laifi ne dan na tambaya?? to ba zan fada ba".

Abbagana hausa novels @ facebook.

Share:

10 comments:

pls drop down your comment......
dan Allah ku ajiye comment.

Tallata Kayanka

Guide Tricks Blog

Be With Me Technology

Popular Posts

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).