shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wanda aka fi sani da hausa novel wanda ni Muhammad abba gana nake rubutawa dan wayar tare da fadakarwa ga mutane a yanayin da muke ciki.

Wednesday 27 January 2016

BANA KAUNARKA!!! 8

bana-kaunarkajpg.jpg

BANA KAUNAR KA!!!



8




MUHD-ABBA~GANA


ya alamin ya zauna tare da cewa ke naki ba zai zo ba ne ,ni rufa min asiri ni bani da kowa asalima ni yanzu bani da lokacin soyayya yace kamar ni kin gani aure baya gana ni kan ba yanzu zan yi aure ba nima gaskiya nafi so nayi karati sosai gaskiyarki my sister amma naga shahid yana sonki sosai ko ba kya son soja ne? ni dai gaskiya yanzu bazan ce ina son shi ba domin karatu nasa a gabana to Allah ya taimaka mana,da safe kamar kullum na shiga dakin mom nagaishe ta nace mom ya zancan karatunmu? a,a sai dai ki tambayi abbanku na mike da sauri
[10:07AM, 1/27/2016] A.➖GANA: na shiga dakin abbanmu nayi sallama ya amsa min yana zaune kan abin sallah na zauna kusa dashi nace abba ina kwana lafiya lau sister usaina na bata rai gaskiya abba bana so acemin usakina to ya sunanki? ni sunana fa wahida abba ya zancan karatunmu? haba sister wahida wanne irin karatu kuma eh abba to kia min yar uwarki inji raayinta ina shirin fita ta shigo bayan ta gaida abba yace dama yar uwarki ce take so kuci gaba da karatu amma yaya kika gani? ta sunkuyar da kai sannan ta soma magana abba gaskiya ni aure zan........na zabura na mike mahida kina da hankali aure! aure fakikace? kuka ne ya kwace min ni kaina ban san dalilin kukan ba abba ne yai ta lallashina har nai shiru amma zuciyata kamar ta fashe don bakin ciki abba yace mahida menene hujjarki na kin karatun sannan batun aure wakike so? dan waye?aina kuma yake,abba munyi dashi zai barni na cigaba da karatuna nace waye shi? abba ya haidar ne dan anty....da kyau mahida Allah yai muku albarka. kefa wahida wallahi ni ba zan yi aure yanzu ba har nawa nake ni gaskiya karatu zanyi mahida ta katse ni da cewa abba wallahi ya shahid yana tsananin son wahida cikin kuka nace shi ya fada miki yana sona? don ni bamuyi dashi ba in ma ya fada miki to ki bashi hakuri dan bani da lokacin soyyaya a yanzu ina gama magana na fice wata dakinmu na shiga na kulle na fada gado kuka nake sosai me yasa mahida zatai mana haka? menene aibun karatun meyasa zata so aure akan karatu muddin ta tauye mana karatunmu wallahi ta cuce mu tuni wani irin rikitaccen zazzabi ya rufe ni kaina na sara min.maganar abba naji yana kiran sunana na mike jikina n karkarwa na bude ya amin yai saurin rike ni don ganin lokacin kankani na zafge abba yace wahida dama baki da lafiya natsunguna don kafafuna ba zasu iya dauka taba ya amin neya kama ni taso mu tafi asibiti abin ka da yar gatan al'amin tuni ya kaita babban asibiti inda aka bata gado hankalin al'amin bai kwanta ba sai da yaga ta samu bacci bayan azahar ina kwance dakin ni kadai sai ga ya shahid da haidar da yake a asibiti din ya haidar aiki sukai sallama na amsa da sauri bom boy ya karaso sannu sister yauwa ya shahid ina anti?



MUHD-ABBA~GANA

www.abbagana.pun.bz
Share:

0 comments:

Post a Comment

pls drop down your comment......
dan Allah ku ajiye comment.

Tallata Kayanka

Guide Tricks Blog

Be With Me Technology

Popular Posts

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).