shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wanda aka fi sani da hausa novel wanda ni Muhammad abba gana nake rubutawa dan wayar tare da fadakarwa ga mutane a yanayin da muke ciki.

Monday 23 November 2015

KAUNA CE SILA***16----20

kauna-ce-sila.jpg

[11/22, 2:34 PM] Ábbä~Gåñā: KAUNA CE SILA 16






MUHD-ABBA~GANA





da muka saba sai naje gurin ummanmu na zauna nace umma kin san meye? tace sai kin fada sai kuma na kwashe da dariya sai tace amma kin fiye shirme to ki fada min mana meye sai nace mata ina zuwa sai na nufi daki ba dan nayi komai a daki ba sai akuma na fito nace mata hmm! umma waka zan fara tace ban gane ba nace mata waka dai irin wadda kike ji a radio sai tace haba mamaa sai kace wasan yara kin san kuwa me kike cewa? nace Allah umma ba wasa nake ba nan dai na bata labarin komai tun daga ranar dana fara fadawa maryam har zuwa yau tace to ni dai ba abinda zance sai nace Allah ya zaba abinda yafi alkairi Allah shi kadai yasan dai dai.naji dadin bayanin umma kuma gaskiya ta kara min karfin gwiwa sosai hudu da minti goma daidai ina gidan su maryam muna ta hira ina ta duba lokaci dan a kule nake da doki biyar daidai ifan ya kira maryam gashi a kofar gida tace to tare muka fita muka gaisheshi ya amsa maryam ta kawo kujeru muka zauna aka kawo wa ifan lemwo sai yace min da gaske kike kina so kiyi waka sai nace dashi eh har zuciyata ina so sai yace amna fa kin san waka dalilin yinta suna da yawa zaki iya fada min daya daga ciki sai nace masa ra'ayi sai yayi dariya yace har da wannan ma amma kara tuno wani nayi shuru alamar tunani can nace masa eh fadakarwa sai yace yawwa kinga yanzu kika dauki hanya to amma kina ganin zaki iya fadakar da mutane ta hanyar waka"






MUHD-ABBA~GANA






www.abbagana.pun.bz
[11/22, 7:43 PM] Ábbä~Gåñā: KAUNA CE SILA 17






MUHD-ABBA~GANA







sai nace masa eh zan iya sai yace to shikenan yanzu bani number ki sannan kiyi min kwatancen gidan ku nace masa toh yace yanzu yamma tayi amma zan kira ki na zo gidanku kamar jibi haka nace masa na gode ina jira dana koma gida sai na bawa umma labarin duk abin da ya faru yau sai naga kawai ta yid ariya da alamun dai umma bata gamsu ba tana ganin kawai shirme nakeyi bayan kwana uku da rabuwar mu da ifan sai ga kiranshi bayan magariba wai aina fita na tarar dashi har ya samarwa kanshi gurin zama a dakalin makwabtanmu nayi sallama sai ya amsa tare da fara'a yace yauwaa yau fa zaki fara daukan karatu nace masa kai yace da fatan kin shirya nace masa eh sai naga ya zaro farar takarda da biro daga aljuhunsa ni abin ma sai ya bani dariya sai kawai na basar kar ya gane nace masa lallai kuwa kamar karatu yace aike wasa kika dauka nace a'a ni din wa ai kuwa kamar karatu haka muke yi ni da ifan don yana biyawa ina yi nima har yaji na rike yace kin yi kokari ya kuma ce kin san sunar wakan nace a'a yace sunansa (langar fasi) sai nace me kenan ban taba jiba sai yace yana nufin langar da ake yayi nace oh na nage sai naga ya mike yace bara na tashi na tafi sai da safe ki tafi da takardar nan kiyi tayi kafin na dawo ki iya sosai nace masa toh Insha Allah dana shiga na bawa umma labari na kuma nuna mata sai naga ta kalleni....








MUHD-ABBA~GANA








www.abbagana.pun.bz
[11/23, 8:09 AM]abbä~Gåñā: KAUNA CE SILA 18







MUHD-ABBA~GANA




kawai da alamu dai har yanzu umma bata gamsu da abin da nake yi ba ta dauki abun wasa ko yaushe ka gannni da takarda a hannu na ni a dole na samu abun yi in har ba aiki nake yi ba to kuwa zaka ganni da takarda ta a hannu ko idan zan yi sallah,dan abinci ma baya hanani nazarin waka ta kuma wani ikon Allah sai gashi na iya sosai har na rike ko ba takar da zan iya yi maka bayan kamar sati daya ifan ya dawo gidan mu ya tambayeni na iya nace masa eh yace to na rerra masa yaji nnan na hau rere waka kamar karatu yace excellent gaskiya kin yi kokkari amma yanzu tunda a n rubuta ta gaba daya zan je studio ayi kidan ta sai nayi tare da wata mawakiya idan muka yi sai na kawo miki kiyi taji idan kika iya sai muje kiyi irin yanda tayi nace masa toh yace dan kar ki sha wahala ne nace masa to na gode yace ba dammuwa a wannan watan ne kumma aka kafe sunayen mu nasamu amisssion a makaranta zamu fara registration na gama cikin sauki aka bani printing technologgy zan fara daga pre nd na yiwa Allah godiya duk da ban san cos din ba sai da naga an kafe ni a can amma nace zan yi don ina zaton hakan shine alkahairi da nake roko na samu rabuwar mu da ifan zai yi kamar sati daya sai gashi a gidanmu da wata yamma duk da garin ana zafi amma garin ba kowa ba kuma hayaniya a yanzu ifan ya zama dan gida dan har ciki yake shiga ya zama kamar dan uwan mu na jini bayan an gaigaisa ne sai ya ce min ga CD plate din wakar ki mun rera tare da murja baba sai nace au waka tace ma? sai yace r
eh mana na karba ina ta murna sai yace shi zakiyi taji har sai kin iya duk yanda tayi"



MUHD-ABBA~GANA




www.abbagana.pun.bz
[11/23, 8:17 AM] Ábbä~Gåñā: KAUNA CE SILA 19





MUHD-ABBA~GANA





nace masa toh da zai tafine naji umma nace masa abin nan kuwa da gaske ne yaushe mamaa zata iya waka yace umma zata iya dan gaskiya tana da kokari da sa kai kiyi mata addu a kawai tace to mun gode washegari na nufi gidan su maryam ina ta murna na nuna matw CD tace ai kuwa yanzu zamu ji muka kunna cd muka fara ji nan na nutsu burina kawai naji duk yanda take karyar da muryar ta nima na yi irin haka sai dab da magariba na baro gidan su maryam haka dai na ci gaba da jin wakar nan dan kullum ina aiki ma aina ji har na haddace bayan kamar sati guda na kira ifan nace to na haddace yace to shi kenan yau wace rana nace masa yau litinin
yace to ranar laraba da yamma ki zo tare da maryam sai ki doro wakarki ki fadawa umma sai ku zo zoo road idan ku kazo sai kiyi kuna fitowa zaku yi min waya ina wani studio local sound studio yana kallon junction din cort road nace masa kace naxo nayi waka cikin wata irin rudewa yace eh nan na daka wani tsalle na ce masa Allah ya kaimu na fadawa umma sannan na kira maryam na fada mata. 27/02/.... wannan ranar ta laraba ta kasance mai dinbin tarihi a tattare da ni domin a ranar ne na fara waka kuma tana daga cikin ranakun da bazan taba mantawa ba har abada.




MUHD-ABBA~GANA




www.abbagana.pun.bz
[11/23, 8:18 AM] Ábbä~Gåñā KAUNA CE SILA 20





MUHD-ABBA~GANA





karfe hudu na shiga gudan su maryam na same ta har ta shirya nace mata to taho mu tafi sai tace min mama zata je sharada tace zata ajiye mu a zoo road din idain ta dawo sai ta dauko mu nace kai amma naji dadi muna haka sai naji muryar mama tana kwalawa maryam kira na bita nima dan na gaisheta ta amsa tace a'a mawaka har kin kararo nace eh tace to zo muje muka fito ina rike da jakar mama,maryam ta shiga gaba na zauna a baya mama tace min mamaa ta ya zance karatunki fah sai nace sai wani sati zan fara zuwa na gama komai tace to ai yafi kar kice kuma karatun ba za ki ba shi mahimmanci ba nace tab! ai ba zan soma ba mama muna hawa kan titi zok road nayi wa ifan waya yace bara ya fito bakin gurin a daidai gurin mama ta ajiye mu amma ba ta tafi basai da ta ga ifan ya sauko daga beben har suka gaisa sannan ta tafi da muka shiga studio sai ya fara nuna mana yan gurin inda ya fara nuna mana mai gurin sunansa muhammad bello muka gaishe shi yace ku kannen ifan ne kuma ifan dan uwana ne shi yasa ba zan matsa da bincike ba nan dai yayi ta nuna mu yana gabatar da mu har muka isa dakin da ake wakar annan na sha kallo na kuma zama yar kauye dan ban taba zata haka zanga abin ba gaskiya da mutum ya ga irin kayan aikin su yasan abin ba na wasa bane banda inda muka fara zama nan ma da wani studio na farko kuma duk iri daya ne amma muna biyun muka wuce fasalin dakin ne kamar ciki da falo anan na farko wato engineering room akwai kujera kamar uku har da ta wanda zaka zauna a kan computer wanda shine zai dauki recording.




MUHD-ABBA~GANA



www.abbagana.pun.bz
Share:

0 comments:

Post a Comment

pls drop down your comment......
dan Allah ku ajiye comment.

Tallata Kayanka

Guide Tricks Blog

Be With Me Technology

Popular Posts

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Blog Archive