shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wanda aka fi sani da hausa novel wanda ni Muhammad abba gana nake rubutawa dan wayar tare da fadakarwa ga mutane a yanayin da muke ciki.

Sunday 22 November 2015

KAUNA CE SILA***6--7

kauna-ce-sila.jpg

KAUNA CE SILA 6










MUHD-ABBA~GANA








yafa mayafi purple na sake bakin takalmi dama ni bana saka plat sai mai tudu ko don bani da tsayi ne sosai amma dai irin takalma na kenan dana fito nacewa umma ni zan tafi tace to ki gaida mama marayam da maryam din amma kar ki kai magariba don Allah gidan su maryam na nufa na shiga da sallama na ganta a tsakar gida tana karatun littafin hausa nace mata har an fara ta tareni da dariya muka shiga falon su muka zauna t kawo min ruwa na sha muka fara hira tace bari ta zubo min abinci nace mata ai a koshe nake don yau ko abincin dare ma bana jin zanci tayi dariya nace mata yana ji gidan shiru tace min duk sun tafi kamu wata yar uwarmu ni suka bari da girkin dare nace ai gara da na sameki na mika mata wayata ta fara daddannawa tana murna tace yauwa ai yanzu kin zama babba ta dauko wayarta ta saka number ta ta kira naga tana yin sarving anan ne nake bata labarin yanda muka yi da jibrin tace toko shi ya sai miki nace a'a ubana ne tayi dariya tace iyye ashe mun kusa shan biki nace dawa din? nifa bana sonshi tace meyasa? nace nifa kinsan nafi son dan gayu kuma mai ilimi tace au shi ba gaye bane? nace gaskiya ba sosai ba muka tafa tare muna dariya munyi hira sosai da maryam wadda rabi ta samarice har take cemin ina fa wallahi duk tafi son wanda yake wasan hausa nace mata to Allah ya taimaka










MUHD-ABBA~GANA

09039016969





www.abbagana.pun.bz





KAUNA CE SILA 7









MUHD-ABBA~GANA




bayan ta rako min nake fada mata cewa zanje jos gurin yayar ummanmu amma kafin na tafi zanzo muyi sallama tace to zata kira nima nace mata to tace dan Allah ki gaida min umma sosai kafin nazo tace to ranar ne da daddare ummi take fada min babnmu yace na shirya ranar lahadi na tafi jos din nace mata to ina murna,bayan sallar ishai yaro ya shigo yace wai jibrin yana kirana haka naje kmar yanda na saba fuska taba yabo ba fallasa na zauna tare da sallama bayan mun gaisa na dan daure fuska nace jibrin ashe dama kaya ka kawo min har kala uku to gaskiya ni bna so kawai sai ka hau kawo min kayan sakawa yayi yan dariya yace haba mamaa nifa nake fatan zama mijinki idan nayi miki ai kaina nayiwa ko? nace masa eh duk da haka dai yace tro amma fa a min afuwa nace shikenan washegari na fito zanje wanki kawai sai muka hadu da jibrin sai na dan sunkuyar da kai na kasa nace masa ina wuni yace lafiya ina zak haka nace saloon yace muje na rakaki nace a'a ka barshi na gode yace shikenan har ya dan yi gaba sai nace masa au gobe zanyi tafiya zan je jos gurin yayar mamanmu yace amma shine ba ki fada min ba nace kayi hakuri na manta yace ba komai sai nazo da daddare nace to da daddare yazo kamar yanda ya saba haka na karasa na zauna muka gaisa nace masa ga number ta.










MUHD-ABBA~GANA

09039016969






www.abbagana.pun.bz
Share:

0 comments:

Post a Comment

pls drop down your comment......
dan Allah ku ajiye comment.

Tallata Kayanka

Guide Tricks Blog

Be With Me Technology

Popular Posts

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Blog Archive