shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wanda aka fi sani da hausa novel wanda ni Muhammad abba gana nake rubutawa dan wayar tare da fadakarwa ga mutane a yanayin da muke ciki.

Sunday 19 July 2015

INA YA KAMATA NA KALLA A JIKIN BUDURWATA

wpeaceanimated1.gif

INA YA KAMATA NA KALLA A JIKIN
BUDURWATA ?
Tambaya:
Malam koya halatta na kalli gashin macen da
nakeso in aura ???
Ko kuma don Allah malam ka taimaka kaimin
bayanin abunda ya halatta in kalla a jikin macen
dazan aura kafin muyi aure.
Nagode.
Allah ya gafarta maka.
(Daga abba gana)
AMSA.
=====
DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAIJIN QAI.
To dan'uwa ya halatta ka kalli macen da kakeso
ka aura.
Kamar yadda yazo a cikin hadisi, inda Annabi
(s.a.w) yake cewa:
"Idan dayanku yana neman aure, to in yasami
damar kallon abin dazai kira shi zuwa aurenta,
toya aikata hakan"
Abu dawud a hadisi mai lambata: 2082.
Amma malamai sunyi sa6ani akan wurin daya
kamata mutum ya kalla a jikin mace lokacin da
yaje neman aure:
1. Akwai wadanda sukace zai kalli fuska da tafin
hannu ne kawai, saboda tafin hannu yana nuna
ni'imar jikin mace, kamar yadda fuska take nuna
kyau.
Saboda haka sai a takaita akansu, wannan itace
maganar mafi yawan malamai.
2. Nabiyu kuma sukace, zai kalli duk abin yake
bayyana a jikin mace, don haka bayan fuska da
hannu zai iya kallon duga-dugai da wuya.
3. Malamai na uku sun tafi akan cewa:
Zai kalleta a kayan da take sawa a cikin gida, ta
fuskace shi ya kalle ta, sannan ta juya baya ya
kalleta.
Wannan ra'ayin shine yafi dacewa, saboda ta
haka mutum zaisan yanayin matar dazai aura,
yadda ya kamata.
Saidai ba'a son yawaita kallon saboda duk abin
da aka halatta saboda bukata, toya wajaba a
tsaya a gwargwadonta.
Wannan yasa yawaita zuwa zance da yawaita yin
waya, zai iya zama haramun saboda yana iya
tayar da sha'awa, sha'awa kuwa tana iya kaiwa
zuwa barna.
Wal iyazu billa.
Saboda haka matasa ku kula dan kunji ance ya
halatta, kada mutum kuma ya wuce gona da iri a
wajen kallon.
Mai neman Karin bayani, yaduba:
Al'insaf 8\15 da Muhallah 9\161.
Allah shine mafi sani.
Share:

0 comments:

Post a Comment

pls drop down your comment......
dan Allah ku ajiye comment.

Tallata Kayanka

Guide Tricks Blog

Be With Me Technology

Popular Posts

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Blog Archive