shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wanda aka fi sani da hausa novel wanda ni Muhammad abba gana nake rubutawa dan wayar tare da fadakarwa ga mutane a yanayin da muke ciki.

Sunday 19 July 2015

Ladabin shiga bandaki (1).

peopleimagessm7.jpg

Ladubban Shiga Bandaki (Fitsari Ko Bayangida):
Akwai tsari na ladubba da musulunci yake dasu a
lokacin da mutum yake niyyar kewayawa.
Wannan zai nuna maka cewa addinin musulunci
ya karade komai:
(1) Anbaton Allah:
Ana bukatar kafin kashiga ka ambaci Allah domin
ba'a anbaton Allah a makewayi, kuma kanemi
Allah ya tsareka daga sharrin aljanu, domin irin
wadannan wurare matattarace tasu.
Sai ya karanta wannan addu'a yace:
ﺑِﺴْﻢِ ﺍَﻟﻠﻪِ، ﺍَﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﺇِﻧِّﻲ ﺃَﻋُﻮﺫُ ﺑِﻚَ ﻣِﻦَ ﺍَﻟْﺨُﺒُﺚِ ﻭَﺍﻟْﺨَﺒَﺎﺋِﺚِ
Ma'ana
Da sunan Allah, Ya Allah lalle ni ina neman
tsarinka (Daka tsareni) daga aljanu maza da
kuma aljanu mata.
Idan kuma zaka fito sai kace:
ﻏُﻔْﺮَﺍﻧَﻚَ، ﺍَﻟْﺤَﻤْﺪُ ﻟﻠﻪِ ﺍَﻟَّﺬِﻱ ﺃَﺫْﻫَﺐَ ﻋَﻨِّﻲ ﺍَﻷَﺫَﻯ ﻭَﻋَﺎﻓَﺎﻧِﻲ
Ma'ana:
Ina neman) gafararka Allah, Dukkan godiya ta
tabbata gareka, wanda ya rabani da wannan
kazantar kuma ya bani lafiya.
Kusani ba'a shiga bayi da dukkan wani abu da
yake dauke da sunan Allah, kamar zobe, ko carbi.
Hakanan kuma ba'a katse bayangida da dukkan
wani abu da yake da sunan Allah.
(2) Fara Gabatar Da Kafar Hagu A Lokacin Shiga.
kafar dama kuma lokacin fitowa.
(3) Ayi A Tsugunne:
kada mutum yayi fitsari ko bayan gida a tsaye,
sai dai idan wurin kangone ko yana tsoron fitsarin
ya fallatso masa, sannan ba wanda zai ganshi.
Darasi mai zuwa zanci gaba daga yadda muka
tsaya.
Insha Allah.
Share:

0 comments:

Post a Comment

pls drop down your comment......
dan Allah ku ajiye comment.

Tallata Kayanka

Guide Tricks Blog

Be With Me Technology

Popular Posts

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Blog Archive