shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wanda aka fi sani da hausa novel wanda ni Muhammad abba gana nake rubutawa dan wayar tare da fadakarwa ga mutane a yanayin da muke ciki.

Monday 20 July 2015

WACE CE******ITA? 57

computerimages1.jpg

WACE CE ITA..?? 57
Na ABBA-GANA
Bata tsaya ba taci gaba da chin uban hafsa
farhaan ya kasa aikata komai kunya ta isheshe
dagyar hafsa ta samu ta miqe tayi bayan
farhaan da gudu tana kuka, tabbas hafsa ta
gane iffaat Dan kuwa itace ta qona mata qafa
shekara wajen Shida da suka wuce, iffaat ji take
kamar ta hada da farhaan din ta musu lilis
amma bazata iya dukan farhaan ba, tsanar sa ta
rufe mata ido ta tausayawa yayarta da take
tareda fasiqi irin sa tagodewa Allah da bata
aureshiba, da saidai suyi kashin kai a gidan Dan
bazata dauki wannan iskancinba ta dakawa
hafsa tsawa tabar gidannan hafsa ta kasa fitowa
bayan farhaan ta qara mata tsawa wallahi idan
naxo sai na kakkaryaki, inbanda hafsa batada
gaskiya ai ko qanwar hafsa iffaat bazata iya
fada da itaba bare hafsa mai Shekara wajen 30,
zata kakkarya iffaat. amma tunda batada
gaskiya dole ta boye farhaan kuwa ya rungume
hannuwa yana kallon ikon Allah kunya ta isheshi
da nadamar abinda ya aikata, tayi cikin hafsa
da qarfi hafsa ta riqe farhaan da qarfi wani baqin
cikine ya qara tasomata yanda taga tana
rungume farhaan ta baya uhum su kishi manya
tayi cikinta da qarfi ta janyo gashin da tayi qara
da qarfi ta wurgata a kan fridge farhaan ya
dakawa iffaat tsawa akan miye haka ta juyo
tamai kallo keep quiet ina zuwa gunka kaima..!!!
tama hafsa gargadi kamin ta lissafa biyar tabar
gidannan hafsa dagyar ta miqe ta kwashi
kayanta a hannu taji jiki tana gudu tana tunanin
wai wannan WACE CE ITA?? House girl ce haka
kyakyawa kuma ta mata haka gaban farhaan.
Anya kuwa?? Bayan ta kori hafsa ta juyo ta kalli
farhaan ido cikin ido tana tunanin balbala masa
masifa ji take kamar zuciyarta ta fito Dan baqin
ciki aranta tace wai ita kenan inaga matarsa da
sukasan juna idan taga haka sai hade rai ta
mutu.! Ya dago ido ya mata wani kallo ta
mayataccun sexy eyes dinsa tuni ta manta
abinda takeson ta masa sai ya bata tausayi tayi
tsaki.....
Har zata fita dakin sai kuma ta daure ta dawo ta
gyara ko ina ta tattara sauran kayan hafsa data
bari ta miqa masa tace ga kanan tsohuwar
karuwarka nan idan ka bita ka kai mata.. ta juyo
kenan ya janyo mata gashi da qarfin bala'ee
saida tayi wata qara....
Share:

0 comments:

Post a Comment

pls drop down your comment......
dan Allah ku ajiye comment.

Tallata Kayanka

Guide Tricks Blog

Be With Me Technology

Popular Posts

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Blog Archive