shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wanda aka fi sani da hausa novel wanda ni Muhammad abba gana nake rubutawa dan wayar tare da fadakarwa ga mutane a yanayin da muke ciki.

Sunday 19 July 2015

NASHA NONON MATATA MENENE MATSAYIN AUREN MU ???

clickmaster20dady-1.gif

MALAM NASHA NONON MATATA MENENE
MATSAYIN AUREN MU ???
Don Allah malam ya matsayin mutumin da yasha
nonon matarsa, ya aurensu yake ?
(Daga Hamza Sa'eed).
AMSA:
======
DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAIJIN QAI.
Allah madaukakin sarki ya halatta maka jin dadi
da dukkkan bangarorin jikin matarka, in banda
dubura ko kuma saduwa da ita lokacin da take
haila.
Saboda haka ya halatta ka tsotsi nononta
mutukar babu ruwa aciki, amma idan akwai ruwa
aciki, to malamai sunyi sabani akan halaccin
hakan zuwa maganganu guda biyu kamar haka:
1. Ya halatta, saboda kasancewar nonon da yake
haramta aure shine wanda aka sha kafin yaro
yacika shakaru biyu, saboda fadin Annabi (S.A.W)
.
“Shayarwar da take haramtawa, itace wacce yaro
yasha saboda yunwa”
Kuduba Sahihul Bukhari hadisi mai lamba ta
:5102.
Ma’ana.
Lokacin da ba zai iya wadatuwa ba daga nono,
saboda shine abincinsa, shi kuma wannan ya
farune bayan mutum ya girma don haka ba zaiyi
tasiri ba wajen haramta aure.
Wannan ita ce maganar mafi yawan malamai.
2. Bai halatta ya shaba, saboda koda yaushe
mutum yasha nonon mace tota haramta a
gareshi, domin Annabi (S.A.W) ya umarci matar
Abu-huzaifa data shayar da Salim, don ta
haramta a gareshi, kamar yadda Muslim ya
rawaito a hadisi mai lamba ta: 2636, tare da
cewa a lokacin Salim yariga ya girma, wannan sai
yake nuna cewa idan babba yasha nono to zai yi
tasiri wajan haramcin aure.
Zancen da ya fi karfi shine ya halatta miji ya sha
nonon matarsa, saidai rashin shan shine yafi,
saboda fita daga sabanin malamai yana da kyau,
don neman Karin bayani kuduba:
Bidayatul-mujtahid mujallady na 2\67.
Allah shine mafi sani.
Share:

1 comment:

pls drop down your comment......
dan Allah ku ajiye comment.

Tallata Kayanka

Guide Tricks Blog

Be With Me Technology

Popular Posts

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Blog Archive