shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wanda aka fi sani da hausa novel wanda ni Muhammad abba gana nake rubutawa dan wayar tare da fadakarwa ga mutane a yanayin da muke ciki.

Monday 20 July 2015

WACE CE******ITA? 61

computerimages1.jpg

WACE CE ITA..??61
Na ABBA-GANA
Suna tsaka da labarin su saiga farhaan ya shigo
ya gaida surukansa yama ummanshi ya jiki ya
shige dakin abbansa,
Bayan ya wuce ne maman Suhaila take cewa
Allah sarki yaronnan har yanxu bai nemi
mataba? Umma tace kedai bari gashinan
Bansan mi yake jiraba, niko ga shawara, mizai
hana a hada farhaan da iffaat aure. Mama tayi
dariya kai hajiya kulu ina kika taba ganin rigima
da rigima sun hadu duk sukasa dariya umma
tace lallai kam Dan farhaan da iffaat basa zama
guri daya. Mama tace koda yake shi aure daban
ne wata qila sai kiga sun zauna lfy.
Gaskiyar magana dukansu sunyi na'am da
shawarar hajiya kulu maman Suhaila sun tsaya
akan zasu shawarci mazajensu suji,
Suna zaune suna tadi saiga iffaat da ta ciki
kyale da su mangoro da gwaiba umma tace um
um mai hali baya barin halinsa..! duk suka saka
dariya, taje ta wanko ta kawo musu suka
farasha, dama ita qa'idarta idan zatasha
mangoro saita mulmulashi yayi laushi yayi ruwa
sannan tasha. Ta kuwa miqe qafafu ta saka
basket dinda ta saka kayan a ciki ta fara shan
mangoronta tana zaune saiga farhaan ya shigo
ya kalleta, xaman da tayi ya bashi dariya ya
tuna mai da lokacin da take qarama sai yaji bari
ya tsokaneta komai ta fanjama fanjam.!!
Wai umma wannan Yar taki ba university take
xuwaba? Umma tace eh chan take kaga yata an
zama yan mata ko..!! Inafa yan mata har yanxu
bata wayeba! Kalli Dan Allah yanda take shan
mangoro kamar wata Yar ruga,! ruwan
mangoromangoro suna bin hannu, ya kwashe da
dariya hadda buga qafa ya gama quleta ya kalli
umma anya kuwa zata sami miji a haka??
Umma tace ka sakawa yata ido dayawafa miji
kam sai ta xaba Dan ma bakaga yanda ake
layiba dukansu suka dara nima dai jabo na dara
kuma Masu karatu sai Ku dara.!!
Iffaat tace umma ki barshi, ta dago ta kalleshi
ido cikin ido tace mijina sai ka Ganshi wayayye
na gaske ba irin wayewarkaba, ba Wanda yagane
habaicin da ta masa sai shi damu Masu karatu.
Yadan Sosa kai yayi murmushi qarfin hali mama
bari na tafi tunda kun hanani mangoro, umma
tace sai kace wacce da debo ta sammaka, yace
waa ai wannan tafi dijee rowa.! da zai fita ya
hada da gefen chinyarta ya take saida tayi qara
ta jefeshi da qallon mangoro......
Share:

0 comments:

Post a Comment

pls drop down your comment......
dan Allah ku ajiye comment.

Tallata Kayanka

Guide Tricks Blog

Be With Me Technology

Popular Posts

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Blog Archive