shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wanda aka fi sani da hausa novel wanda ni Muhammad abba gana nake rubutawa dan wayar tare da fadakarwa ga mutane a yanayin da muke ciki.

Wednesday 22 July 2015

WACE CE*******ITA? 69

computerimages1.jpg

WACE CE ITA..??

69


.............by........


muhd-Abba~Gana



Tace Idan da kana dukana ada yanxu akwai
banbanci wata qila ada ina gyalewa ko kuma ina
ramawa to ka sani yanxu akwai banbanci, ni
matar aurece inada yanci kuma nasan yancina
so ka kiyaye hannunka daga Taba matar aure.!
Ta sake mai hannu da qarfi Ta wuce abinta ya
bita da kallon Mamaki hadida zargin abinda ya
kawota yi anan ya akayi tasan yana nan ya daki
iska baima jira karuwarshiba ya fito da qarfi
koda ya fito bata ba labarinta ya shiga mota
gudu yake kamar ya ya hira sama koda ya isa
gida bata isoba yayi kusan 30mnt sannan ta iso
da ledojin abinci a hannu.! Tana zuwa ya daka
mata tsawa ina taje? Ta kalleshi dukda taji tsoro
amma bonewa tayi, ta danqaramar uwar harara,
kamar ma bada ita yakeba, tana Neman guri ta
zauna ya fincikota ke badake nake maganaba, ta
kalleshi ido cikin ido tace mai inda yaje chan
taje? Mi kikaje yi achan nanma ta bashi amsa
abinda kajeyi achan shi najeyi.? Idonsa suka
kada sukayi jaaa sun firfito waje iffaat kinsan
abinda kike fada ya qara fincikota ya mannata a
garu kinada auren nawa zakije gurinnan ? Ko kin
manta ke matar aurece. Taji tsoro iya tsoro
amma ta daure ta bashi amsa ta kalleshi idonta
cikin nasa tace, au auren akan mace kadai yake
kenan kaima ai kanada auren nawa kaje gurin
nan ko kaman ta kanada aurenane akanka? Idan
kuma akwai banbanci tsakanin mu let me know.
Yanda idan ka'aikata badaidaiba za'a maka
hukunci haka nima za'amini so miye
banbanci?? Wani baqin cikin kishi ya turnuqeshi.
Muryansa na rawa yace iffaat tell me the Truth
mi kikajeyi a gurin nan ? Ya bata tausayi yanda
ya sassauto, nace abinda kajeyi shi najeyi.
Sakinta yayi ya fuskanceta dakyau iffaat mi
kakajeyi a gurinnan Har kika ganni? Tace abinci
naje siya,
Ya manna mata arniyar harara, daga yau na
soke baki ba fita sayen abinci idan dai ba
makaranta zakijeba baki ba fita, abincin kuma ki
shiga ki girka da kanki!!
Tsaki tayi ta wuce shi,
Farhaan ya tsargu matuqa yauda ta kamashi da
wata ai bai isa ya shigo gidannan ba..by
muhd-Abba~Gana
Share:

0 comments:

Post a Comment

pls drop down your comment......
dan Allah ku ajiye comment.

Tallata Kayanka

Guide Tricks Blog

Be With Me Technology

Popular Posts

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Blog Archive