shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wanda aka fi sani da hausa novel wanda ni Muhammad abba gana nake rubutawa dan wayar tare da fadakarwa ga mutane a yanayin da muke ciki.

Sunday 19 July 2015

WACE CE****ITA? 48

computerimages1.jpg

a252520novels-1.jpg

WACE CE ITA..?? 48
Na ABBA-GANA




Tayi ajiyar xuciya Ta juyo ta kallesu sunyi cirko
cirko dasu, da kunburarren bakinta take musu
magana, kiyi haquri Dan Allah wallahi bansan
lokacinda na daki qawarkiba, sukace ba komai
kema kiyi haquri, nan dai suka yafi juna suka
qulla qawance da ita da alqawarin zasu
taimakamata da duk abinda sukasan zasu iya.
Haka suka zauna Kowa shiru har aka tashi
makaranta..
*
iffaat na zuwa gida mama ta fara tambayar ta
lafiya kike kunbura haka kamar jabo tayi kuka??
Wallahi mama anyo korane, zasu shiga class tayi
karo da wata frnd dinta sai kuma ta fadi qasa
shine bakinta ya kunbura, Subhanallahi. Kinga
yanda kika kunbura kuwa? Allah ya tsare gaba
ta amsa da amin ta wuce dakinta.
Bayan ta shiga daki ta cire uniform, ta zauna ta
fara tunanin abinda yan matannan suka fada
tabbas kuwa idan har abinda suka fada shine
kaji kanason mutum to wallahi tanason Yaya
farhaaan, aiki jaa wanda zai zama mijin yayarta
takeso??
Dole ta dauki mataki wa zuciyarta.! Tayi
murmushi Kai amma so shegene shine ya hanata
sukuni shekara da shekaru! Amma so ya
wanketa! Waima miyasa bata ganeba? Tayi tsaki
ni ko zan mutu zan auri Yy farhaan ne gashi da
shegen son mata! Duk maganar da takeyi aranta
takeyinta amma Sam zuciyarta bata aminta da
ko kalma daya tataba, kawai tana fadane amma
tasan yanda takeji da gudu idan yace yana so
zata amince,...
Hmmmm dole zuciya taso Yy farhaan ta saba
dashi, yy farhaan duk inda namiji mai lfy zai
shiga yana shiga haka tayita karanto siffarsa da
maganar sa da tafiyarsa da murmushinsa tana
murmushi, lallai ta yarda tanasonsa but miye
mafita???
Dole ne ta ijiye sonsa taci gaba da danneshi har
Allah ya bata mijinta tayi aure??
Anya zata iya kuwa??
Zaki iya mana dayar zuciyarta ta bata amsa aiki
ja gabanta..
Suhaila ce ta shigo tana waya ta gane da
farhaan take wayar kuma taji yanayinda ta saba
ji amma ta basar.....
Share:

0 comments:

Post a Comment

pls drop down your comment......
dan Allah ku ajiye comment.

Tallata Kayanka

Guide Tricks Blog

Be With Me Technology

Popular Posts

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Blog Archive