shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wanda aka fi sani da hausa novel wanda ni Muhammad abba gana nake rubutawa dan wayar tare da fadakarwa ga mutane a yanayin da muke ciki.

Wednesday 9 September 2015

INSIYA****16

insiya.jpg

INSIYA 16



*********NA**********


muhd-Abba~Gana




tuni na saki kara mutanan suna jin kara suka fito jeji da gudu'suna zuwa suka ganni a kwance sai nishi nake.nan suka daukeni sai cikin dakin su.
nan na ji su sama-sama suna wani irin yare idona kuma sai ganin mutane nake bibbiyu uku-uku ga shi nan dai.haka dai sai gani nayi akan gado mai raushin stiya ashe har gari ya waye mutane sun zagaye ni sai fifita ake yi min.ina bude idona na ga sun fara murna nima sai na mayar musu da tawa murnan mai hade da murmushi dan duk wanda ya dauka a cikin wannan halin ai ya wuce masoyinka sai dai mai kaunarka.
maganar su ce ta tsayar da ni daga tunani da nake ciki fulatan ci naji suna yi min ga shi kuma ni ban iya ba,hausa na iya sai suka yi murmushi ashe sun iya hausan kadan amma ba kamar mu ba da muka tashi a cikin hausar sai naji suna ce min"sháññû yaro, ya jiki shin ya warke? sai nace musu da sauki ina yi ina murmushi mai hade da tarin farin ciki mai yawa.nan na zauna da su har na warke sosai san danayi shekara biyu masu kyau har ma na iya fulatancin kuma gashi har na iya kiwo,dan matar dana ke gurin ta ta rike ni tsakaninta da Allah,tamkar ita ta haifeni ga shi Allah bai taba bata haihuwa ba saboda haka ni take so har a fiska sunanta tumba,mijin ta kuma sunan sa jauro,samarin wajen kuma suna sona,dan akwai wani saurayi mai suna bako yana sona sosai dan shi ne yake rakani kiwo.
idan kuma ina tatsar nono sai ya zo mu nayi tare kai zan iya cewa bacci ne yake rabamu.akwai wata rana ina zaune sai tumba tace"yau fa rana ta kusan karewa dan mun kusan tashi domin mu ba mazaunan nan bane.



muhd-Abba~Gana





www.abbagana.pun.bz
Share:

0 comments:

Post a Comment

pls drop down your comment......
dan Allah ku ajiye comment.

Tallata Kayanka

Guide Tricks Blog

Be With Me Technology

Popular Posts

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Blog Archive