shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wanda aka fi sani da hausa novel wanda ni Muhammad abba gana nake rubutawa dan wayar tare da fadakarwa ga mutane a yanayin da muke ciki.

Tuesday 15 September 2015

INSIYA*****28

insiya.jpg

INSIYA 28



**********NA*************


muhd-Abba~Gana



wallahi ba haka bane hajiya yau watana biyu bana kasar ina london wajen blesing
ok.na manta ashe kace min zakayi tafiya yasu blesing din?
wallahi lafiyarsu klau
hajiya tace amira ki kirawo min antynki tace toh mama nan tazo takira ni muka fito ni da Amira na durkusa nace hajiya sannu da zuwa yauwa.INSIYA sai naji yace kai hajiya ke ba kya rabo da kwashe-kwashe wannan yar aikin fa?
sai tace kinga INSIYA miko masa ruwa yace a'a hajiya ba zan iya sha ba
saboda me?
wallahi hajiya idan na sha zan iya amai
wai to saboda me? ni haryanzu baka bani cikakkiyar amsa ba hajiya ni dai ba zan iya sha ba kawai to bari in dauko maka kai hajiya kai bar shi ba zan iya sha ba,sai na tashi ina dan murmushin karfin hali hajiya tace INSIYA ina zaki? nace hajiya daki zan shiga saboda karna zauna na sa shi amai.
nayi shigewa ta daki nan hajiya ta girgiza kanta tace amma mujit ban ji dadi ba wallahi ance maka kudi hauka ne ko kuma ance maka mulki hauka ne? sai tayi murmushi sannan ta nisa tace lallai mujit kana bani mamaki idan kayi wata maganar amma wani lokacin baka bani mamaki.
mujit kayi tunani a baya kasan mu talakawa ne kuma ni da babarka uwarmu daya ubanmu daya kuma kasan ba irin wahalar da bamu sha ba saboda talauxi shi yasa idan naga talaka nake tausayinsa dan ni ma na dandana naji babu dadi.by muhd abba gana
a lokacin dana auri baban amira kasan ba shi da kudi dan a lokacin karatu hake sai ya fita yake samo mana abinci sai kuma abin da iyayanka suke bamu dan a lokacin babanka kansila nena rijiyar zaki,alokacin kai kuma kana karami dan ba ka fi shekara shida ba.
ga shi yanzu Allah yaba babanka shugaban kasa ni kuma Allah ya ba mijina dan majalisa to kaga yanzu ne muke da lokacin taimaka wa talakawa.

kuma kaga wannan yarinyar wallahi ba yar talaka ba cè sai dai kawai wahalar da take sha ne yafi wani dan talakan.kuma ni ban dauke ta a yar aiki ba na dauke tane a yata ta cikina kafin Allah ya nuna mata yayan babáñtã"



muhd-Abba~Gana



www.abbagana.pun.bz
Share:

0 comments:

Post a Comment

pls drop down your comment......
dan Allah ku ajiye comment.

Tallata Kayanka

Guide Tricks Blog

Be With Me Technology

Popular Posts

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Blog Archive