shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wanda aka fi sani da hausa novel wanda ni Muhammad abba gana nake rubutawa dan wayar tare da fadakarwa ga mutane a yanayin da muke ciki.

Wednesday 9 September 2015

JININ AL'ADAH

banna.jpg

JININ AL'ADA DA HUKUNCE-HUKUNCENSA
NA
MALAM RABI'U UMAR RIJIYAR LEMO
FITOWA TA 2:
JININ HAILA DA HIKIMAR YIN SA:
Kalmar (Haid) ( ﺍﻟﺤﻴﺾ ) a larabce ta na nufin
"zubowar wani abu da kwararowarsa".
Amma a shar'ance kalmar (Haid) ta na nufin
wani jini da ya ke fita daga gaban Mace, a wani
lokaci sananne, ba don wata cuta ba.
Wannan shi ne ake nufi da jinin haila a
shar'ance. Sai dai duk da cewa jini ne da ya ke
fita ba don wata cuta ba, ko rauni, ko haihuwa
ba, amma ya na da banbamci tsakanin wata
Mace zuwa wata, kowace Mace gwargwadon
yadda Allah Ya halicce ta, ko kuma yanayin
wurin da take rayuwa.
Hikimar yin sa kuwa ita ce: Jaririn da ya ke cikin
ciki, ba zai iya cin abinci, kamar yadda wanda ya
ke wajen ciki zai ci ba, don haka sai Allah Ya sa
Mace take fitar da wannan jinin, yayin da bata
da juna biyu, idan kuwa ta yi ciki sai wannan jini
ya zama shi ne abin da Jaririn zai rika
amfanuwa da shi, ta hanyar cibiyarsa, ta inda
jinin zai shiga jijiyoyinsa ya zamar masa abinci.
Wannan ita ce hikimar samar da wannan jini,
don haka sau da yawa idan mace na da ciki, jinin
haila kan dauke mata, haka ma idan ta na
shayarwa, musamman ma farkon shayarwar.
Wata kila saboda wannan jinin ana mayar da shi
a sarrafa shi wajan samun nonon da yaron zai
sha. Wallahu a'alam.
LOKACIN FARA JININ HAILA DA ADADIN
KWANAKINSA:
A saurari fitowa ta 3 in sha Allahu Ta'ala
Share:

0 comments:

Post a Comment

pls drop down your comment......
dan Allah ku ajiye comment.

Tallata Kayanka

Guide Tricks Blog

Be With Me Technology

Popular Posts

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Blog Archive