shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wanda aka fi sani da hausa novel wanda ni Muhammad abba gana nake rubutawa dan wayar tare da fadakarwa ga mutane a yanayin da muke ciki.

Saturday 18 July 2015

WACE CE ITA? 20

] .: WACE CE ITA..?? 20
Na ABBA GANA
Yaci gaba da wayansa saida ya qare kamar zai
daga kai ya ganta amma hankalinsa na gun
budurwar da yake tsarawa a waya, bata gane mi
yake cewaba Dan da English yake magana, ya
wuce kamar da second 30 ta sauko ta shiga
gidan da sauri ta kulle qofar lanbu taje gurin
zamanta tana addu'a da Allah yasa bai gantaba,
idan ya ganta tunda yace bazai maidata gidaba
ya zatayi, zai kulle qofarne ya hanata fita ko ina
gashi tanason tayi qawance da yar baqar
yarinyar da take gani tana wucewa. Tana nan
zaune Tana Zane a qasa ya kwala mata kira taje
ta turbude fuska, yace taje hafsa na kiranta,
batamai musuba ta wuce shima yayi mamaki
sosai yanda ya wasketa da mari batace
komaiba, aransa yace kodai ya fara nasarar
natsar da itane, hafsa a Palo zaune, wai ta dan
qasa mata qafafuwanta da ruwan xafi, ( inaga ta
kusa fara period ne coz yan chinar skull dinmu
haka sukeyi kuma zakiga sun Dan sami sauqin
ciwon cikin) na watsa mata harara, banganeba,
tamin bayani shiko gogan yana tsaye ya
rungume hannuwansa, nikaina jabo nayi
mamakin iffaat data amince da aikin, ta zauna ta
riqa juya ruwan turinisu suna dukan qasar qafar
hafsa har suka huce ta zubar ta dauko wasu ta
mata daqowar da hafsa zataye ta hanbare iffaat
ta fadi xaune ruwan suka zube a jikinta duk ta
jiqe amma ruwan ba wani zafi sosai, farhaan ya
kallesu baice musu komai ba, yaci gaba da
kallon ball dinsa, karo na uku ta dauko ruwan
zafin da gangan iffaat ta juye matasu a qafafu,
hafsa ta tsallara ihu, iffaat ta miqe tsaye da qarfi
tayi gefe farhaan yazo da sauri yana duba qafar
ba abinda tayi a Zahiri amma tana zugi daga ciki
iffaat tayi tsaye tana jiran hukuncin da farhaan
zai yanke mata da sauri ya kira Dr. hafsa sai
aikin kukatakeyi, yana rungume da ita tanata
ihun, yace iffaahh. Ta watsomai idonta da gani
tadan tsorata ya akayi haka?? Ta fuske kamar
da gaske, naje zan juye ruwan sai kawai tasa
qafa zata shureni saita shure ruwan suka juye
mata a qafa, harga Allah ya yarda cox yaga
yanda ta shureta karo na farko, ya jinjina kai,
duk da baiji dadiba amma yasan iffaat batada
laifi,......
Dr yazo ya dubata ya bata
magunguna, tace zata koma gida kada yar
aikinsa ta kasheta, baiji dadiba cox duk cikin yan
matanshi hafsace kawai take iya jure jarabarshi,
cox ita sonshi takeyi so duk wahalan da zai bata
tana jurewa sauran kuma, kudi kawai sukeso,
Yakaita gida, ya dawo bai kula iffaat ba ya wuce
dakinsa sai yanxu ya kula dakin yayi kacha
kacha ya kwala mata kira, ke zaman me kike a
gidannan?? Kalli dakina kalli toilet dina! Miye
amfanin kine??
Share:

3 comments:

pls drop down your comment......
dan Allah ku ajiye comment.

Tallata Kayanka

Guide Tricks Blog

Be With Me Technology

Popular Posts

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Blog Archive