shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wanda aka fi sani da hausa novel wanda ni Muhammad abba gana nake rubutawa dan wayar tare da fadakarwa ga mutane a yanayin da muke ciki.

Saturday 18 July 2015

WACE CE ITA? 21

5] .: WACE CE ITA..?? 21
Na ABBA GANA
Dole kiyi aikinda aka kawoki kiyi idan har
kinason amaidaki gida, so zabi ya rage naki, ko
kiyi aiki a maidaki gida ko kuma kiyi ta zama
anan har qarshen rayuwarki. taga gara tayi
aikin ya maidata gida.
*********************
Yau watan iffaat biyar a gidansu farhaan inda
sabo yaci ace ya saba da halinta ya kawo
budurensa daidai har 8 suna chin uban juna Ita
dasu, kuma ko wacce sai tayi nasarar daukar
fansar abinda suka mata ta hanya kala kala,
kuma farhaaah Sam baya ganewa, ita
Har yau ta kasa gane cewa ba matansa bane
matan banxa ne da taga sunfi hudu sai kawai
aranta tace auri saki yakeyi, irin na wani alhajin
qauyensu da akace auri saki yakeyi, kullum
sukaje Gidansa kallon TV sai suga sabuwar mata
a gidan akace auri saki yakeyi, anan ta gane
halinsu daya da farhaan...
*******
Yau dai iffaat an tashi ba lafiya zazzabi yake
damunta da wani gwauron ciwon ciki, har bacci
ya dauketa tsakar bacci ciwon ya tayar da ita
taji danshi danshi a qasanta dubanwa da zatayi
sai taga jini Habawa ta fashe da kuka koda ta
tashi ya mata kache kace a jiki Ashe ya Dade da
zuwa bata kulaba, tayi Sa'a farhaan yana palo
yana kallon ball ta fito a hargitse tana kuka, ta
nuna mai jininta fa na xuba, ya kalleta habo
kikeyi? aah ta gun fitsarinane, kunya ta
kamashi, shi wace irin yarinyace umma ta sashi
dole zama da ita wai mai aiki gashi ta zame mai
jaraba, yayi tsaki yana kall ball dinsa za'a
katseshi, to kije daki zan siyo miki magani
yanzu, yama Dr waya akawo mai pad da
maganin ciwon cikin na mata bada jimawa ba Dr
ya kawo mai, ya kirata amma ba amsa ya gaji
yayi banxa da ita, sai da ya qare kallon ball
dinsa ya miqe tsaye sai maganin ya fadi sannan
ya tuna da wata iffaat ba lafiya yaje dakinta da
yake yana mura baiji qarnin da dakin yakeyiba,
koda yajee ya ganta ta dunqule a qasa sai juyi
takeyi, duk jikinta ya baci, ya rasa yanda zaiyi
idan ya dauketa zata bata mai jiki ya waya da
Dr waya shiru bai daukaba, ya tsaya gabanta
ganin numfashinta na hawa da sauka kamar
zata mutu yaji tsoron tamutu a gida da zamo
mai aiki, yaqara yima Dr. dinsu waya yace mai
normal ne na farkone ya bata maganin da ya
kawo zata warke kada ya damu, ya dagata
chak ya yakaita bayinsa ya wanke mata jiki ya
rasa yanda zai chire mata tufafi tunda duk sun
jiqe yaje dakinta ba kayan da zai saka mata duk
saman gadonta suke kuma duk ta batasu da jini,
yaje dakin farahnax qanwarshi ya memo wata
jallabiya baqa yazo ya rufe idonsa Dan kada ya
ganta ya chanxa mata kayan jikinta ya....
Share:

0 comments:

Post a Comment

pls drop down your comment......
dan Allah ku ajiye comment.

Tallata Kayanka

Guide Tricks Blog

Be With Me Technology

Popular Posts

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Blog Archive