shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wanda aka fi sani da hausa novel wanda ni Muhammad abba gana nake rubutawa dan wayar tare da fadakarwa ga mutane a yanayin da muke ciki.

Saturday 18 July 2015

WACE CE ITA? 22

WACE CE ITA..?? 22
Na ABBA GANA
Ya bata magani dagyar tasha ta amaryar ya
qara bata wani, yace ta daure ta saka wannan
abin pad tace bata iyaba, ya kalli bayan ledar
yaga yanda ake sakawa ya hada mata ya bata
ta saka, pant ma a kayan farahnax ya daukoshi,
yace ta kwanta dakinsa dakinta ya harqitse
tunda batada lafiya, tanashan magani tuni tayi
bacci,
Bata farkaba sai bayan la'asar tafito Palo tana
dingishi zata tafi dakinsa ya kirata zonan, ya
jikin ta amsa a kasalance, naji sauqi da gani
hajiya iffaat anji jiki Dan har idonta sun fada, tayi
wani iri da ita, ya kir Dr. ya miqa mata waya Dr
ya mata bayanin yanda xatayi komai kuma kada
ta damu duk mace mai lafiya tana wannan abin
sabida haka ta godewa Allah ya fada mata zata
iyayin kwana bakwai tana xubarwa, likita jinina
bazai qareba?? No wannan ba jini bane ciwone
yake fita idan bai fitaba idan kinyi Aure bazaki
haihuba ko bakyason haihuwa?? inaso mana,
him wayaga iffaat da ciki, yadai mata bayanin
komai sukayi sallama, ta bashi wayarsa, ta wuce
daki koda taje duk an tattara kayanta gabi daya
da zanin gado duk babu, an saka wani, sai
yanzu ta tuna yanda tayi kacha kacha da ko
ina...
Iffaat saida tayi kwana biyar sannan ta
kammala, farhaan ne yasa aka kai mata kayanta
wanki.
Wannan ciwon shine mafarin fara shirin iffaat da
farhaaah..
Tunda ta fara ciwo sai yau ta fita waje kamar
yanda ta saba, tana zaune sai ga black girl
dinnan ta wuce qamshinta ya doki hanchinta
aranta tace anyi yar gayu anan gurin, ta qare
kalle kallenta ta shiga cikin gida bayan ta koma
gida tana dakinta zaune tunaninta daya ya zata
zama yar gayu irin na yar baqar yarinyar nan,
taje bayi ta kalli madubi, sosai ta bude
haqoranta taga yanda sukayi laka laka a qasa ga
wata tsatsa da sukayi tofa bata wankewa fiye da
haka ma sai tayi, batasan yanda zatayi dasuba
suyi haske irin na tsohuwar matar farhaan
ramcyba, cox ramcy akwai wushirya kuma da
fararen haqora Tass dasu, tayi tsaki ta qara
gaba...
Ranar ta fito Palo, karo na farko da ta taba
tsayawa kallon TV tunda tazo gidan nan sabida
farhaan kullum ball yake kallo itako batason ball
a rayuwarta, tafison indiya an qare ball ne Anje
talla sai kawai ga tallar signal, mouth Clean ne
mai kyau, taga yanda ake wanke baki sai ta tuna
ta tabaa ganin farhaan yana wankewa har ta
tsaya kallonsa, taje bayin dakin ta nemi mouth
clean din koda ta duba sai taga exactly irin
Wanda aka nuna a TV ne, tayi murmushi Ashe
haqoranta zasuyi fari irin na matar Tv ta Dan
barashi a brush tana wankewa yana jini duk da
ya mata xafi ta daure cox tanason ta zama yar
gayu irin na yar baqa sunanda ta sanyawa
yarinyar kenan, iffaat dai haka tajuri yi brush
kullum ko nace duk lokacin da abin ya motsa sai
tayi cox.......
Share:

2 comments:

  1. Aishat Abdulkhadir (sweety)14 October 2015 at 13:31

    tanx

    ReplyDelete
  2. Zaidu Ebryheemj jibia zaid2 November 2015 at 13:40

    allah ya kara fahimta

    ReplyDelete

pls drop down your comment......
dan Allah ku ajiye comment.

Tallata Kayanka

Guide Tricks Blog

Be With Me Technology

Popular Posts

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Blog Archive