shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wanda aka fi sani da hausa novel wanda ni Muhammad abba gana nake rubutawa dan wayar tare da fadakarwa ga mutane a yanayin da muke ciki.

Saturday, 18 July 2015

WACE CE ITA? 30

: WACE CE ITA..?? 30
Na ABBA GANA
***********
Kamin kace kobo duk qauye ya dauka da
dawowar iffaat chikin mota mai kamar jirgin
sama. Ko ina sukasan jirgin sama oho!?? kowa
zuwa yake mata sannu, wasu kuwa gulma ake
zuwayi, bawanda yasan aiki tajeyi birni sabida
goggo bata fadawa kowaba duk wanda ya
tambayeta sai tace ai tana birni gun qanwarta,
Su dijee an tafi biki chan nesa dasu, basu ji
labarin dawowar iffaat ba sai da la'asar bayan
sun dawo, suka zo ganin iffat, ganin ta ya sasu
farin ciki koda batayi wani haskeba amma tadan
chanza suka fara baiwa juna labari, iffaat natajin
haushi anyi shegiya da yawa bata, cox dijee tayi
hatsabibanci bayan tafiyar iffaat, tayi wata qawa
ummulkhairi wacce itama hatsabibiyar gaskece,
bata wasa hakadai take yanda suke, itama iffaat
ta basu labarin ta'addancin da tayi barni, amma
bata fadi cewa qawayen farhaaan bane, sunsha
dariya matuqa, anyi kewar juna,
A tunanina iffaat zata bar abinda takeyi a qauye
koba komai anje birni kuma ta fara Dan wayewa
tanason ta zama Yar gayu, Ashe ni jabo bangane
bane, iffaat iskanci da la'ana sai abinda ya qaru,
bare yanxu da suka zama su hudu, ni kaina ina
tausayawa iyayen yaran, kowa kuka yake dasu a
qauye sun gagari kowa ga iffaat an dawo.
****
Iffaat take tambayar goggo ya akayi aka gyara
gidansu, goggo ta bata labarin cewa ai
yayantane dake birni sukazo ganinta suka tarar
batanan kuma suka tarar da babanku ya rasu, to
su suka gyara gidan suka bata wata takarda wai
duk lokacinda kika dawo ki nemesu, zasuzo su
ganki, sun kawo min alkhairi kala kala daga
birni, ainikan naci arzikin yayan kishiya,
Wannan karon Goggo bata tsangwmawa iffaat
kaman daba, shi yasa suke zaman lafiya, ba
ruwanta da harkarta itama haka,
Ranar suna hira da goggo take cewa Wai ihhatu
a birni bakiyi saurayiba, ta zare ido ta dafe qirji
saurayi goggo!!! nida ko fitabanayi, nan iffaat ta
gayawa goggo aikinta goggo taji tsoro, Allah
yasa dai baya biyoki da dare, daga ke saishi a
gida ba koea. iffaat tace taaab nida ko shiri
bama bamayi, nan ta fadawa goggo ta'addancin
da tayi,goggo bataji dadiba koda dama tasan
za'ayi haka, nan goggo tadan fahimtar da iffaat
yakamata ta gane ta girma yanxu tadaina
shirme da shiririta, kina ganin idan kikaci gaba
da haka zaki sami mijin Aure,?? a qauyen nan fa
ba yarinyar da ta tabayin jini a gida, taji raaaas
ta tuna itama tayi sau daya a birni amma
bataabaiwa goggo labariba,
*****
Maganganun goggo sun dan ratsa iffaat har ta
fadawa qawayenta su daina tsokana ko su rasa
mijin Aure duk da cewa basu dainaba amma sun
rage kwarai saidak idan an musu suna ramawa,
haka kuwa akayi sunyi sauqi sosai, har takai
suna gaida mutane a hanya, amma fa idan ka
tabasu zakaga bala'ee da masifa.....
Share:

0 comments:

Post a Comment

pls drop down your comment......
dan Allah ku ajiye comment.

Tallata Kayanka

Guide Tricks Blog

Be With Me Technology

Popular Posts

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Blog Archive