shafine da aka bude wa masoyan littatafan hausa wanda aka fi sani da hausa novel wanda ni Muhammad abba gana nake rubutawa dan wayar tare da fadakarwa ga mutane a yanayin da muke ciki.

Thursday 22 October 2015

RAYUWAR***FAUZZIYA-5

rayuwar-fauziya.jpg

5RAYUWAR (FAUZIYYA) part 5 Cigaba 5. Litinin
mai zuwa na yanke hukuncin komawa makaranta
gaba 1 sbd exams, nahad'a list d'in komai da
zan bukata harda kud'in reg na shekarar da
zamu shiga don bawa mama. Cikin nutsuwa da
daidaita kalaman bakina naje wajen mama, suna
falo gaba d'ayansu natsuguna nace mama sannu
da hutawa, "yawwa tafad'a ta juya kanta tana
kallon littafin da yake hannunta, Mama dama
ranar litinin zan koma makaranta shine na kawo
miki list d'in komai sbd kisani akan lkc, list kuma
fauziyya? Nifa bazan iya jure abinda mahaifinku
yake ba, don ni mace ce 'karfinmu ba d'aya bane,
ta mi'ko hannu ta kar6a tana girgiza 'kafa, Kut...
Lallai fauziyya baki da hankali kusan 200,000 zan
baki? Nad'an razana amma nadake nace eh
mama akwai... Yimin shiru anfad'a miki ke
kad'aice 'ya? Kina ganin wahalar da take gabana
zaki afkomin da wnnn?... Wllh Mama karki biya..
Na tsinto muryar Fa'iza tana magana cikin tsiwa,
na kalleta na daka mata tsawa! Nace dalla
malama yimin shiru badake ake magana ba, "wllh
'karya kikebadake ake magana ba, "wllh 'karya
kike tunda kikai maganar kud'i kamar kinyi da
nine donba ke kad'aice me kud'inba Fa'iza ce ta
sake maganar karo na 2, to saiki hana abiyamin
na fad'a naja tsaki, harga ALLAH ko rabin
kud'innan bazan iya biyaba ballantana duka"
Mama ce tayi maganar, gabana yafad'i nace
Mama wazai biyamin? Au tambayarta kike?
Fa'iza ta sake magana, banason shishshi
malama ana Maganane da wad'anda sukasan
me suke ba irinki ba, au ALLAH? Dama kinsan
abinda kike kika za6i neman suna akan
farantawa mahaifiyarki don shashanci? Maganar
ta daki zuciyata amma nayi shiru na'kyaleta.
Mama don ALLAH kidaure kibiyamin wllh ko
sana'a ce zan nema nadingayi kafin shekara ta
zagayo, bata amsaminba hakan yasa Fa'iza ta
sake amsa, "au ashe kin iya sana'a to ki hakura
da karatun kije ki sana'ar mana" ta kaini
ma'kura hakan yasa na mi'ke cikin zafi nace "ai
bakisan darajar karatunba shiyasa kike ganin
za'a iya hkr dashi, banza da'ki'kiya sbd ke
bakyayi ko?.. Yimin shiru shashasha 'yar
uwartaki kike fad'awa haka?Ba laifin ki bane sbd
andaure miki gindin tafiya karatu ita tazauna
agida ko? Mama ba hk bane kinajin abubuwan
da take fad'aminfa... Sbd tsabar kissa
yarinyarnan tasa kuka tanacewa wai dama tasan
za'ai haka Abbane yatsayamin har yabani damar
gorantamata, bance mata 'kala ba natsuguna
ganin yadda mama take huci nace "Mama don
ALLAH kiyi hakuri ba hakane nufina ba... Zakimin
shiru kosai na dalla miki mari munafuka, tunda
hakane kema na soke karatunnaki ai badole
bane... Da sauri nad'ago kaina don tantance
abinda Mama take cewa, nace karatunnawa? Sbd
makircin Fa'iza ko sbd kud'in makarantar? Wllh
Mama idan akaimin haka ba'aimin adalci ba...
Wani wawan mari naji ya sauka afuskata, cikin
tsananin rud'ewa na nemi hayyacina narasa....
Kuka kawai nasa mai matuqar ban tausayi, inajin
dariyar Fa'iza harda shewa, na d'ago kumatuna
dana tabbatar yatsun mama sun zanu akai,
nasake magana cikin kuka nace "don ALLAH
mama kitaimakamin kece gatana akan karatunan,
wllh zanyi asara idan kika datsemin karatuna
adaidai wnnn lkcn, FAUZIYYA! Mama takira
sunana da gudu na amsa tace "fita kibani waje
tun kafin na zubar miki da jini ashe badad'i ga
ranar takardun dakika gagara bani, nasan halinta
da km zafin ranta, amma zuciyata taqi
amincemin akan nafita, haka najajirce nabar falon
'kwakwalwata cike da tsananin tashin hankali.




www.abbagana.pun.bz
Share:

2 comments:

  1. Dan Allah ga numbarta 08025342249 ta Wshap kudinga turomi litafai

    ReplyDelete

pls drop down your comment......
dan Allah ku ajiye comment.

Tallata Kayanka

Guide Tricks Blog

Be With Me Technology

Popular Posts

About Me

My photo
Hey! I’m Muhammad Abba Gana, popularly known as AbbaGana, a blog Scientist by mind and a passionate blogger by heart fountainhead of Guidetricks, Duniyan Fasaha, Duniyar Yau, Hanyantsirah, Gidan Novels, Abba Gana Novels and Be With Me Technologies, I am twenty something year old guy from Jimeta, Adamawa State, Nigeria. I’m a Freelance writer, Information marketer, professional blogger, Web designer, Internet speaker, software Developer and also an author. I make living with my laptop and can work from anywhere I find myself (as long as there is a power supply and a reliable internet connection).

Blog Archive